Sashe 10
Hauwa Kulu Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
GULMA AJALI
A
wannan yammacin a Nurses station na sashen ido a asibitin Murtala baa komai sai gulamammaki masu lasisi, na abinda ya faru a kan aikin da sabon likitan ya yiwa maras lafiyar tasa. Su Nos Saratu da Metron Maria an samu abinda ake so, aka maida abin topic of discussion na wannan ranar.
Ko aikin su na ranar sun kasa yi yau, tsabar saboda yadda gulmar Sarham ke cin su.
Metron Maria wadda ita ta halarci aikin warware idanun Hauwa tare da likitan, ta ce hey! In baku labari dai, kunnen ku nawa?
Suka hada baki (in chorused) wajen cewa kunnen mu biyu, to ku kara biyu ku sha labari.
Dr. Sarham dai ya karasa makantar da yarinyar nan mai hakiya da yake mana balbali akan su, aikin da yayi mata was not successful at all.
Kuma ya kama bakin sa salin-alin bai ce komai akai ba ya bar asibiti, ba tareda kowa ya san taasar da yayi ba, ya ja bakinsa ya tsuke ko sum utu ko suyi rai oho musu.
Nos Gambo tace ki bari don Allah?
Saratu ta yi rantsuwa ta labarta musu abinda ya faru, ta ce yo dama idon ya gama rubewa fa, maganin su kenan suma, da sun lallaba sun tafi da muka kore su da ta ci gaba da morar dan wani abun a idon, aa su ga sarakan naci dambun kuturu, ni dama na san idon kiris yake jira a taba shi, shikuma karambanin sa kenan, an ce musu sawun su a likkafa su koma gida su cigaba da barbada farin kwallin su da suke barbadawa suka ki ji, wanda bai ji bari ba ai ya ji hoho, yanzu da ya maidata totally blind ai sa hakura.
Ni ai dama na fada muku tsautsayi ne kadai zai saka ni baiwa wannnan yaron idanuna ya saka musu wuka, har yaushe ya bar sakandire ko ince ya bar shan nono a cinyar uwar sa? Da zan bari ya fede min ido? Ai yafi kama da Romeo (Uban soyayya) fiyeda consultatant.
Ban da ilmi a Najeriya ya zama sabatta-juyatta, ya zama abinda ya zama wajen tabarbarewa, ban taba ganin inda dan kasa da shekaru talatin ya zama surgeon ba” wata bakuwa a cikin su mai hankali ta ce,
ku kuwa ku daina abinda kuke yi bai kamata ba, shi aikin fida ai haka ya gada, ko ayi nasara, ko akasin ta, kafin ayi aikin mara lafiya ya san da haka saboda haka nema ake saka hannu bisa yarjejeniyar amincewar iyaye da makusan ta, so ko mutuwa ta yi bashi da alhakin hakan. Yayi iya kokarin sa Allah ne bai yi ba.
Idan fitsari banza ne kaza ta yi mana? Kuna ta zagin sa da kushe shi alhalin bai ci muku ba bai sha muku ba, ku ku je kuyi karatun fidar idon mana? Shin wai kyawun Dr. Sarham da gayunsa ne ya koma masa abin hassada a bakunan ku ko me?.
Da wannan ta kashe bakin su murus, bayan sun musa da cewa ina abin yake da zasuyiwa hassada abu tsololo kamar karan raken takanda. Wata kuma mara kunya a cikinsu ta kada baki tace ai irinsa sun fi dadin shaani a gado, baa dakin tiyatar ido ba. suka kwashe da dariya. Har suka tashi aikin ranar basu bar wadannan zantukan ba na shegantaka har daya na cewa ya kamata a kwace licence din sa na aikin likitanci tunda daga zuwa ya fara da makantar da yayan mutane, saboda rashin iya aiki. (Ni kuma nace gulma-ajali mai yin ki kadai zaki kashe).
***** ***** *****
DESTINY TORMENTS.”
(DA KARFE SHIDDA NA YAMMA A GIDAN PROF. ABBAS SHANONO)
M
awakin ya sake cewa Destiny torments my heart… cikin baitin wata waka ne da Dr. Sarham yake saurare daga kwancen da yake a yammacin ranar, bayan komawarsa gida daga kwace idon Hauwa.
Yana kwance har kusan magriba a rigingine a tsakiyar matsakaicin gadon dakin sa. Sai ya ji shahararren mawakin zamanin wato R-Kelly kamar dashi yake. Don zuciyar sa duk ta takura. Ya shiga kunci na babu gaira babu dalili. Ya yarda abinda ya faru dashi a kan aikin da ya yiwa Hauwa Bilyaminu kaddara ne, wadda ta rigayi fata, ba don haka ba ai yaji ‘warning alarm’ a cikin kansa, mai cewa ya bari kada yayi aikin nan babu nasara a cikin sa sam, don haka tunanin sa yafi karkata ga cewa sakacin sa ne ko gangancinsa.
Amma kuma da aikin kaddara ai, altogether.
Allah ya riga ya rubuta Hauwa Bilyaminu zata makance a hannun sa. But this written destiny really touched and tormented his heart.
Ace ka zama sanadin nakasar idanun wani dan adam kwata-kwata, duk da cewa dai aikin likita irin wannan (a mutu ko a rayu) ne, sannan ba zaa tuhume shi ba, tunda ya tafiyar da komai a kan kaidar aikin sa ne, amma IDO fa ake zance, wannan kwayar tsokar guda biyu mafi amfani da muhimmanci ga halittar dan adam, sannaan in har kana da zuciyar yan adamtaka a cikin kirjin ka da humanity a tare da kai, dole zuciyar ka ta tabu, da ganin yadda fuskar Innar Hauwa ta shiga tashin hankali a lokacin da Hauwa tace,
bata ganin komai a gabanta sai duhu.
Wanda tayi ta kokarin danne tashin hankalin data shiga din saboda shi. To shi tashi zuciyar ba tabuwa kawai ta yi ba da tausayin su da disappointment akan aikinsa, ta kekkece ne, sannan ta tsatstsage ta yayyage ta yagalgale (into pieces at the same time). Ta yadda a gaban Innar Hauwa duk dauriyar da yake yi sa sai da idonsa ya kada, kwalla ta cika idonnasa, a fakaice ya yi kokari maida kwallar, ta hanyar juya musu baya ya zuba dukkan hannayen shi cikin aljihu yana maida kwallar sa, bai san Innar ta gane halin da yake ciki ba.
Hakan ya faru ne lokacin da ya ji Hauwa tana cewa.
Shike nan yanzu Inna sunana Makauniya? Ba zan sake ganin fuskar ki data Baban mu ranar da ya dawo gare mu ba? Kema na daina ganin ki kenan daga yanzu?”
Yana iya tuno kalaman Innar Hauwa gare shi, da ta ga yasa hankici yana tsane kwallar da yake ta hadidiyewa cikin idanun sa a wayance, yanzu kam tafi karfin sa, ta baiwa kanta yanci ta digo, a lokacin yana rubutu cikin fayil din Hauwa sai hawaye ya diga a kai, wannan ya faru a kan idon Innar Hauwa.
Sai Innar Hauwa ta bagarar da tasirin maganganun Hauwa suka yi mata a ranta, ta maida kulawarta a kan shi inda ta dube shi cikin lallashi tace Haba likita? Kaida zaka bata karfin guiwa? Shi Dan adam ai baya tsallake kaddarar sa. Ita Hauwa-Kulu kaddarar ta kenan.
Abin yi a yanzu gaba dayanmu shine mu yi mata fatan Allah yasa makanta ta zamo kaffara a gare ta. Idan makantar nan jarrabawarta ce ta dan wani lokaci Allah ya yaye mata ya bata ikon cinye wannan babbar jarrabawa, idan kuma ta har abada ce Allah yasa ta zamo silar shigarta aljannah. Nakasa ai ibadah ce ga wasu kebabbub bayin Allah!.
A
wannan yammacin a Nurses station na sashen ido a asibitin Murtala baa komai sai gulamammaki masu lasisi, na abinda ya faru a kan aikin da sabon likitan ya yiwa maras lafiyar tasa. Su Nos Saratu da Metron Maria an samu abinda ake so, aka maida abin topic of discussion na wannan ranar.
Ko aikin su na ranar sun kasa yi yau, tsabar saboda yadda gulmar Sarham ke cin su.
Metron Maria wadda ita ta halarci aikin warware idanun Hauwa tare da likitan, ta ce hey! In baku labari dai, kunnen ku nawa?
Suka hada baki (in chorused) wajen cewa kunnen mu biyu, to ku kara biyu ku sha labari.
Dr. Sarham dai ya karasa makantar da yarinyar nan mai hakiya da yake mana balbali akan su, aikin da yayi mata was not successful at all.
Kuma ya kama bakin sa salin-alin bai ce komai akai ba ya bar asibiti, ba tareda kowa ya san taasar da yayi ba, ya ja bakinsa ya tsuke ko sum utu ko suyi rai oho musu.
Nos Gambo tace ki bari don Allah?
Saratu ta yi rantsuwa ta labarta musu abinda ya faru, ta ce yo dama idon ya gama rubewa fa, maganin su kenan suma, da sun lallaba sun tafi da muka kore su da ta ci gaba da morar dan wani abun a idon, aa su ga sarakan naci dambun kuturu, ni dama na san idon kiris yake jira a taba shi, shikuma karambanin sa kenan, an ce musu sawun su a likkafa su koma gida su cigaba da barbada farin kwallin su da suke barbadawa suka ki ji, wanda bai ji bari ba ai ya ji hoho, yanzu da ya maidata totally blind ai sa hakura.
Ni ai dama na fada muku tsautsayi ne kadai zai saka ni baiwa wannnan yaron idanuna ya saka musu wuka, har yaushe ya bar sakandire ko ince ya bar shan nono a cinyar uwar sa? Da zan bari ya fede min ido? Ai yafi kama da Romeo (Uban soyayya) fiyeda consultatant.
Ban da ilmi a Najeriya ya zama sabatta-juyatta, ya zama abinda ya zama wajen tabarbarewa, ban taba ganin inda dan kasa da shekaru talatin ya zama surgeon ba” wata bakuwa a cikin su mai hankali ta ce,
ku kuwa ku daina abinda kuke yi bai kamata ba, shi aikin fida ai haka ya gada, ko ayi nasara, ko akasin ta, kafin ayi aikin mara lafiya ya san da haka saboda haka nema ake saka hannu bisa yarjejeniyar amincewar iyaye da makusan ta, so ko mutuwa ta yi bashi da alhakin hakan. Yayi iya kokarin sa Allah ne bai yi ba.
Idan fitsari banza ne kaza ta yi mana? Kuna ta zagin sa da kushe shi alhalin bai ci muku ba bai sha muku ba, ku ku je kuyi karatun fidar idon mana? Shin wai kyawun Dr. Sarham da gayunsa ne ya koma masa abin hassada a bakunan ku ko me?.
Da wannan ta kashe bakin su murus, bayan sun musa da cewa ina abin yake da zasuyiwa hassada abu tsololo kamar karan raken takanda. Wata kuma mara kunya a cikinsu ta kada baki tace ai irinsa sun fi dadin shaani a gado, baa dakin tiyatar ido ba. suka kwashe da dariya. Har suka tashi aikin ranar basu bar wadannan zantukan ba na shegantaka har daya na cewa ya kamata a kwace licence din sa na aikin likitanci tunda daga zuwa ya fara da makantar da yayan mutane, saboda rashin iya aiki. (Ni kuma nace gulma-ajali mai yin ki kadai zaki kashe).
***** ***** *****
DESTINY TORMENTS.”
(DA KARFE SHIDDA NA YAMMA A GIDAN PROF. ABBAS SHANONO)
M
awakin ya sake cewa Destiny torments my heart… cikin baitin wata waka ne da Dr. Sarham yake saurare daga kwancen da yake a yammacin ranar, bayan komawarsa gida daga kwace idon Hauwa.
Yana kwance har kusan magriba a rigingine a tsakiyar matsakaicin gadon dakin sa. Sai ya ji shahararren mawakin zamanin wato R-Kelly kamar dashi yake. Don zuciyar sa duk ta takura. Ya shiga kunci na babu gaira babu dalili. Ya yarda abinda ya faru dashi a kan aikin da ya yiwa Hauwa Bilyaminu kaddara ne, wadda ta rigayi fata, ba don haka ba ai yaji ‘warning alarm’ a cikin kansa, mai cewa ya bari kada yayi aikin nan babu nasara a cikin sa sam, don haka tunanin sa yafi karkata ga cewa sakacin sa ne ko gangancinsa.
Amma kuma da aikin kaddara ai, altogether.
Allah ya riga ya rubuta Hauwa Bilyaminu zata makance a hannun sa. But this written destiny really touched and tormented his heart.
Ace ka zama sanadin nakasar idanun wani dan adam kwata-kwata, duk da cewa dai aikin likita irin wannan (a mutu ko a rayu) ne, sannan ba zaa tuhume shi ba, tunda ya tafiyar da komai a kan kaidar aikin sa ne, amma IDO fa ake zance, wannan kwayar tsokar guda biyu mafi amfani da muhimmanci ga halittar dan adam, sannaan in har kana da zuciyar yan adamtaka a cikin kirjin ka da humanity a tare da kai, dole zuciyar ka ta tabu, da ganin yadda fuskar Innar Hauwa ta shiga tashin hankali a lokacin da Hauwa tace,
bata ganin komai a gabanta sai duhu.
Wanda tayi ta kokarin danne tashin hankalin data shiga din saboda shi. To shi tashi zuciyar ba tabuwa kawai ta yi ba da tausayin su da disappointment akan aikinsa, ta kekkece ne, sannan ta tsatstsage ta yayyage ta yagalgale (into pieces at the same time). Ta yadda a gaban Innar Hauwa duk dauriyar da yake yi sa sai da idonsa ya kada, kwalla ta cika idonnasa, a fakaice ya yi kokari maida kwallar, ta hanyar juya musu baya ya zuba dukkan hannayen shi cikin aljihu yana maida kwallar sa, bai san Innar ta gane halin da yake ciki ba.
Hakan ya faru ne lokacin da ya ji Hauwa tana cewa.
Shike nan yanzu Inna sunana Makauniya? Ba zan sake ganin fuskar ki data Baban mu ranar da ya dawo gare mu ba? Kema na daina ganin ki kenan daga yanzu?”
Yana iya tuno kalaman Innar Hauwa gare shi, da ta ga yasa hankici yana tsane kwallar da yake ta hadidiyewa cikin idanun sa a wayance, yanzu kam tafi karfin sa, ta baiwa kanta yanci ta digo, a lokacin yana rubutu cikin fayil din Hauwa sai hawaye ya diga a kai, wannan ya faru a kan idon Innar Hauwa.
Sai Innar Hauwa ta bagarar da tasirin maganganun Hauwa suka yi mata a ranta, ta maida kulawarta a kan shi inda ta dube shi cikin lallashi tace Haba likita? Kaida zaka bata karfin guiwa? Shi Dan adam ai baya tsallake kaddarar sa. Ita Hauwa-Kulu kaddarar ta kenan.
Abin yi a yanzu gaba dayanmu shine mu yi mata fatan Allah yasa makanta ta zamo kaffara a gare ta. Idan makantar nan jarrabawarta ce ta dan wani lokaci Allah ya yaye mata ya bata ikon cinye wannan babbar jarrabawa, idan kuma ta har abada ce Allah yasa ta zamo silar shigarta aljannah. Nakasa ai ibadah ce ga wasu kebabbub bayin Allah!.