← Book details Hauwa Kulu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 27

Sashe 17

Hauwa Kulu Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

A karshen shekarar har kyauta aka bata wato ranar hutun karshen shekara prize giving day kasancewar a shekarar gabadaya ita ke daukar na daya, kuma tafi kowa zuwa makaranta akan lokaci da kasancewa cikin tsaftar jiki data kayan makaranta.
Hakan yasa Sarham da kan sa kawowa Hauwa tasa kyautar ta musamman don kara mata karfin gwiwa inda ya dauki Sumayya a motar sa suka je Levintis suka yo mata sayayyar kayan kamun azumi rankatakaf. Kayan dadi na kwali dana gongoni iri-iri.
Wannan ne karon Sumayyah na farko da zuwa gidan su Hauwa, tunda jimawa Bhaiyan ta Sarham ke bata labarin su, amma bai taba yarda ta biyo shi ba sai yau, yau din ma don ta taya shi sayayya ne don ta iya provision na kayan kwalama, ta kuma taya shi da daukar kayan zuwa cikin lungun.

Suka yi sallama Hauwa na gindin famfo tana alwalah Inna na daga kitchen, Inna ta amsa musu don ta dau muryar Sarham tun daga madafi, amma Hauwa a cikin cikinta ta amsa, zaka ga dai yadda bakin ta ya motsa alamar ta amsa, Sumayya ta tsaya daga nesa ta saka ma Hauwa ido don jikin ta ya gama bata itace Maijiddan, Hauwa Kulun Badalar kofar Naisa da Yayanta yake yawan bata labari kullum, wadda yake cewa ya makantar daga kuskuren aikin ido. A kunnen sa yaji Sumayyah ta rada masa cewa.
Tabarakallah-masha Allah, Subhanallah Ahsanal Khaliqeen da wadannan idanuwa na Hauwau. Bhaiya, ashe dai Hauwa-Jidda beauty ce, irin kalar dana ke so na koma (kasancewar Sumayyah fara ce tas).
Sarham ya juya ya galla mata harara don ya ji ta sarai. Yace wallahi zaki koma yanzunnan in baki yi min shiru ba”. Inna ta leko jin maganganun su tana maraba da bakuwa, nan da nan ta saki fara tace Sumayyatu ce ko?
Sumayyah ta washe baki jin farad daya Inna ta kama sunan ta, ko da wannan ta san tana da matsayi mai girma a gun Bhaiya, tunda har wadanda yake muamala da su sun san da zaman ta.
Ta ce ni ce Inna ina wuni?
Inna ta bata shimfidar karaunin ta ta zauna, inda Hauwa ta tashi, a lokacin ta gama alwalarta ta juyo tana tafe zuwa inda suke kanta tsaye babu ko lalube, tsabar ta dade da sanin kowanne lungu da kowanne sako na gidan su. Sumayyah ta kamo hannunta ta zaunar da ita a kusa da ita, cikin girmamawa Hauwa tace da Sarham Ina wuni likita, yaya aiki? Ya dan dubeta kadan kafin yace an gode Allah Maijidda, ga Yayarki Sumayyah na kawo miki Sumayyah ta saka hannunta cikin na Hauwa, sai Hauwata rike hannayen nata sosai a cikin nata tana murmushi tace sannu da zuwa.
Basu jima suna hira ba Inna ta kammala girkin ta na dambun shinkafa da yaji zogale da soyayyen mangyada ta zubo musu a kwano guda, sannan ta zubawa Sarham yadda ta saba zuba masa a kwanon sa da ta ware masa na samira wanda sabida shi ta dauko shi daga cikin samirunta, shikadai take zubawa abinci a ciki. Ga yaji da yaji tafarnuwa a gefen abincin. Kamar ta san shi da son tafarnuwa, Sumayya ta hadiyi miyau tun kan ta kai loma abincin ya gama yi mata, sannan tsaftar masu gidan ta gamshe ta.
Hauwa kasa cin abincin tayi da Inna ta hada musu itada Sumayyah don bata sakewa da baki amma Sumayyah sosai take kai loma, nan da nan ta tashi da dambunnan. Shima Sarham tuni ya tada nasa sai kwanuka aka direwa Inna.
A ranta Sumayya ta ce eh, wato dole Bhaiya yayiwa abincin gidan su kaura, yana nan an gargajiyantar da shi da wannan girki mai motsa kunnuwa. Basu jima ba sosai don zasu gidan Hajiya Kulu, Sumayya ta baiwa Hauwa sayayyar a hannun ta inda ta saka mata ledojin a cikin hannun ta ta ce,
ga nan gift dinki ne inji Bhaiya, ki cigaba da dauko na daya kin ji Hauwan Inna, shi kuma yayi ta kawo additional gift, duk karshen shekara.
Murmushi Hauwa tayi, tana shafa kayan da ledojin, murmushin na karuwa a fuskar ta, kanta a kasa ta ce kice masa nagode, Allah ya saka da alkhairi, kema na gode da ziyara Anti Sumayyah.
Bayan fitar su da kadan itada Inna shiru suka yi. Hauwa tace Inna ni bazan taba komai ba, don bana son abinda zaa zo ace muna kwadayi. Inna tace to ban ki ta taki ba Kulu, amma shima ya san bamu kwadayin komai nasa tunda baki roke shi ba kuma ba yau ya fara ba, saidai na yau nima ya tsorata ni, don kayan sun ci kudi da yawa da alama. “To Inna ki ajiye ni dai bazan taba ba Inna tace “tsahon shekara guda kenan muna tare da yaron nan, in da wata manufa a tare da shi ko da wani hali nasa mara kyau zuwa yanzu ya kamata in sani, to ban taba gani ba sai tarin alkhairi da nagarta a tare da shi.
Alheri da kyauta wannan na lura halin sa ne na halitta kawai. Don haka ni mahaifiyar ki Safiya na ce ko bayan raina duk abinda Sarhamu ya dauka ya baki da hannun sa ki karba da godiya, ki kuma yi amfani da shi da zuciya daya, wannan yaron bashi da wata manufa akan mu sai zumuncin Allah da ya saka kansa tsakanin sa da mu, don bazan ce wani ne ya saka shi ba ko don neman wani abu daga gare mu”.
**** **** ****
Chapter 17 · 0% Book details