Sashe 14
Hauwa Kulu Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Ya iso gida wajen karfe tara na dare. Jamaar gidan su dama ga aladar su karfe tara na dare na yi sun baje daga falo kowa ya nufi makwancin sa. Amma Abba na nan bai tashi ba, yana nan zaune a kujerar da yake zama a falon yana jiran ganin dawowar sa, yana sauraron labaran kasa da ake yi a gidan talbijin na NTA yana kuma duba tangamemen agogon dake like a bango.
Sarham yayi sallama a babban falon mahaifin sa, inda Abba Prof. ya amsa masa, ya shigo ya zauna daga kasan kafafun Abban, ya ce Abba sannu da gida Abba yace yawwa, kai kuma sannu da yawon dare, daga ina kake haka? Ka bar yan kannen ka cikin damuwa, ka birkice musu wuni guda, me ke faruwa da kai yau?
Sarham ya yi ajiyar zuciya ya ce Abba ina kofar Naisa, wata marainiyar yarinya na yi wa aikin ido, Abba cikin rashin saa zan ce ko kaddara ko tsautsayi ko gangancina ne ban sani ba, ta makance gabadaya, maimakon a samu lafiyar da ake nema.
Muryar Sarham kamar zai fashe da kuka don damuwa, zaka iya karantar tsantsar karaya da sarewar da yake ciki a cikin sautin nasa.
Prof. Abbas Shanono, ya dubi babban dan nasa Sarham cikin kulawa, yace haba Muhammad Sarhamu! Be a man mana! Sai kace ba likita ba? Da haka zaka cigaba da aikin likita kana karaya akan rashin nasarar aiki irin haka? Ai dama aikin likita ba a hannun ku yake ba, a hannun Allah yake, sai abinda ya hukunta ga marar lafiya.
Never blame yourself a kan duk wani unsuccessful surgery. Ka sa a ranka ka yi iya yin ka, sauran, wato samun lafiya ko akasin ta, yana hannun Ubangijin halitta.
Maganar mahaifin nasa ta dan kwantar masa da hankali, at least shi bai ce masa bai iya ba, bai ce don shekarunsa ba masu yawa bane, bai kuma ce laifin sa bane this is soothing, a hankali Sarham ya ce.
Abba kuma shikenan idan yaro ya makance wato ya samu nakasar ido ba zai yi karatu ba sai ‘bara?’
Abba Prof. yace in ji wa? Ai akwai cigaba yanzu sosai akan ilmin masu nakasar ido, akwai makarantu na musamman da gwamnati ta bude domin koyar da su kyauta (public special schools) can ya kamata iyayen ta su kai ta, har anan Kano akwai special school dominyara mau nakasa daban-daban.
Sai Sarham ya ji tamkar Abban sa ya bashi amsar ‘assignment’ din da ya baiwa kansa, ko yace Inna ta bashi, na yaya zai yi Hauwa tayi karatu, sannan kuma Abba ya bashi mafita akan damuwar sa kan matsalar Hauwa, at least zai iya taimaka musu da wannan wato ya tsaya a kan karatun ta, nan take ya yi wani kuduri mai girma ga zuciyar sa shi kadai; na daukan nauyi da takalihun alhakin ilmin Hauwa Blyaminu na sakandire har sai ta kammala in har yana raye, in dai da gaske makafi suna iya yin karatu da rubutu su samu ilmi kamar kowa, da yardar Allah zai tsayawa Hauwa, tunda shi ya samu yayi har gashi ya tsaya da kafafun sa yana kuma da albashin sa, to zai tsaya ya ga cewa Hauwa bata tagayyara a fannin ilmin sakandire sanadin makantarta ba.
Wannan wani alkawari ne da Dr. Sarham ya yi wa kan sa a zuciyar sa, da yake fatan Allah ya bashi iko da tsawon ran cika shi.
Sai washegari wajen karin kumallon su akan dining suka hadu da Maman sa da sauran kannen sa biyu wato Sumayyah da Surayyah. Bayan ya gaida iyayen nasu shikuma kannen sun gaishe shi yadda suka saba ya ja kujerar sa ta dindindin a dining din ya zauna. Mama ta tambaye shi me ya faru da shi ne jiya?
Nan yake gaya mata labarin aikin da yayiwa Hauwa da yadda yake blaming kansa kamar yadda ya gayawa Abban sa.
Barr Mama. itama kamar Abban nasa cewa ta yi ba laifin sa bane. Ta kuma kara da cewa kada ya kara sakawa kansa damuwa irin wannan kan aikin sa in har yana son cimma nasara a gaba, don hakan zai iya sawa ya tsani ‘profession’ din nasa da ya tashi da burin sa. Surayya ta gatsine baki ta ce,
dadi na da mutum daurawa kai damuwar wasu, damuwar da Allah bai dora masa ba, to sai me zai faru don aiki bai yi nasara ba da zaka bi ka wuni cikin damuwa har da kulle kofa da yiwa kai horon yunwa ta hanyar kin cin abinci wuni guda haka Yaya Doctor, ina dalili ina dan mafari?
Sarham ya jefe ta da harara, Mama ta ce ke bana son rashin kunya, wa ya saka ki a maganar mu?
Dagagefen sa inda take zaune Sumayya ta ce cikin jimami.
Bhaiya, kayi wa Allah ka kai ni in duba ta, haka kawai naji tausayin ta ya kama ni nima, makancewa fa totally, a hannun ka, ai da tausayi da sanya damuwa, dole ka shiga phobia dinka, dama dai a ce a hannun wani liktan ne ba kai ba bazaka damu har haka ba, Allah sarki Bhaiya na!.
Yace I know you always pity me Summy, and you are with me especially in such a bad situation (nasan koyaushe kina tausayamin Summy, kuma kina tare dani musammman a lokaci mara dadi). Madallah da wannan kanwa tawa. Karamar su-babbarsu!.
Haka suka karya kumallon suka tashi, masu zuwa aiki wato Sarham da iyayen su suka shiga motocin su daban daban suka wuce wajen aikin su, Surayya ta wuce cikin makaranta inda take karatu anan cikin jamiar Bayero, tana aji daya na digiri a tsangayar ilmin lissafi (mathematics).
Sumayya na aji biyu na babbar Sakandire a makarantar Musa Iliyasu College, dake nan daura da sabuwar jamiar Bayeron, suna fitowa ne kullum tare da Yayan ta Dr. Sarham tun bayan fara aikin sa, sai ya sauke ta sannan zai mika zuwa asibitin Murtala inda bai jima da fara aiki ba, bayan yayi aiki na dan lokaci da asibitin Abdullahi Wase da aka fi sani da asibitin Nasarawa, suka maida shi can don an fi bukatar kwararru a asibitin Murtala fiye da kowanne asibitin gwamnati a Kano.
Wannan ya faru ne jim kadan bayan dawowar sa daga kasar Saudi-Arabia da kadan, inda ya karanci fannin likitancin ido a jamiar Sarki Abdul Azeez dake Jeddah.
**** **** ****
Sarham yayi sallama a babban falon mahaifin sa, inda Abba Prof. ya amsa masa, ya shigo ya zauna daga kasan kafafun Abban, ya ce Abba sannu da gida Abba yace yawwa, kai kuma sannu da yawon dare, daga ina kake haka? Ka bar yan kannen ka cikin damuwa, ka birkice musu wuni guda, me ke faruwa da kai yau?
Sarham ya yi ajiyar zuciya ya ce Abba ina kofar Naisa, wata marainiyar yarinya na yi wa aikin ido, Abba cikin rashin saa zan ce ko kaddara ko tsautsayi ko gangancina ne ban sani ba, ta makance gabadaya, maimakon a samu lafiyar da ake nema.
Muryar Sarham kamar zai fashe da kuka don damuwa, zaka iya karantar tsantsar karaya da sarewar da yake ciki a cikin sautin nasa.
Prof. Abbas Shanono, ya dubi babban dan nasa Sarham cikin kulawa, yace haba Muhammad Sarhamu! Be a man mana! Sai kace ba likita ba? Da haka zaka cigaba da aikin likita kana karaya akan rashin nasarar aiki irin haka? Ai dama aikin likita ba a hannun ku yake ba, a hannun Allah yake, sai abinda ya hukunta ga marar lafiya.
Never blame yourself a kan duk wani unsuccessful surgery. Ka sa a ranka ka yi iya yin ka, sauran, wato samun lafiya ko akasin ta, yana hannun Ubangijin halitta.
Maganar mahaifin nasa ta dan kwantar masa da hankali, at least shi bai ce masa bai iya ba, bai ce don shekarunsa ba masu yawa bane, bai kuma ce laifin sa bane this is soothing, a hankali Sarham ya ce.
Abba kuma shikenan idan yaro ya makance wato ya samu nakasar ido ba zai yi karatu ba sai ‘bara?’
Abba Prof. yace in ji wa? Ai akwai cigaba yanzu sosai akan ilmin masu nakasar ido, akwai makarantu na musamman da gwamnati ta bude domin koyar da su kyauta (public special schools) can ya kamata iyayen ta su kai ta, har anan Kano akwai special school dominyara mau nakasa daban-daban.
Sai Sarham ya ji tamkar Abban sa ya bashi amsar ‘assignment’ din da ya baiwa kansa, ko yace Inna ta bashi, na yaya zai yi Hauwa tayi karatu, sannan kuma Abba ya bashi mafita akan damuwar sa kan matsalar Hauwa, at least zai iya taimaka musu da wannan wato ya tsaya a kan karatun ta, nan take ya yi wani kuduri mai girma ga zuciyar sa shi kadai; na daukan nauyi da takalihun alhakin ilmin Hauwa Blyaminu na sakandire har sai ta kammala in har yana raye, in dai da gaske makafi suna iya yin karatu da rubutu su samu ilmi kamar kowa, da yardar Allah zai tsayawa Hauwa, tunda shi ya samu yayi har gashi ya tsaya da kafafun sa yana kuma da albashin sa, to zai tsaya ya ga cewa Hauwa bata tagayyara a fannin ilmin sakandire sanadin makantarta ba.
Wannan wani alkawari ne da Dr. Sarham ya yi wa kan sa a zuciyar sa, da yake fatan Allah ya bashi iko da tsawon ran cika shi.
Sai washegari wajen karin kumallon su akan dining suka hadu da Maman sa da sauran kannen sa biyu wato Sumayyah da Surayyah. Bayan ya gaida iyayen nasu shikuma kannen sun gaishe shi yadda suka saba ya ja kujerar sa ta dindindin a dining din ya zauna. Mama ta tambaye shi me ya faru da shi ne jiya?
Nan yake gaya mata labarin aikin da yayiwa Hauwa da yadda yake blaming kansa kamar yadda ya gayawa Abban sa.
Barr Mama. itama kamar Abban nasa cewa ta yi ba laifin sa bane. Ta kuma kara da cewa kada ya kara sakawa kansa damuwa irin wannan kan aikin sa in har yana son cimma nasara a gaba, don hakan zai iya sawa ya tsani ‘profession’ din nasa da ya tashi da burin sa. Surayya ta gatsine baki ta ce,
dadi na da mutum daurawa kai damuwar wasu, damuwar da Allah bai dora masa ba, to sai me zai faru don aiki bai yi nasara ba da zaka bi ka wuni cikin damuwa har da kulle kofa da yiwa kai horon yunwa ta hanyar kin cin abinci wuni guda haka Yaya Doctor, ina dalili ina dan mafari?
Sarham ya jefe ta da harara, Mama ta ce ke bana son rashin kunya, wa ya saka ki a maganar mu?
Dagagefen sa inda take zaune Sumayya ta ce cikin jimami.
Bhaiya, kayi wa Allah ka kai ni in duba ta, haka kawai naji tausayin ta ya kama ni nima, makancewa fa totally, a hannun ka, ai da tausayi da sanya damuwa, dole ka shiga phobia dinka, dama dai a ce a hannun wani liktan ne ba kai ba bazaka damu har haka ba, Allah sarki Bhaiya na!.
Yace I know you always pity me Summy, and you are with me especially in such a bad situation (nasan koyaushe kina tausayamin Summy, kuma kina tare dani musammman a lokaci mara dadi). Madallah da wannan kanwa tawa. Karamar su-babbarsu!.
Haka suka karya kumallon suka tashi, masu zuwa aiki wato Sarham da iyayen su suka shiga motocin su daban daban suka wuce wajen aikin su, Surayya ta wuce cikin makaranta inda take karatu anan cikin jamiar Bayero, tana aji daya na digiri a tsangayar ilmin lissafi (mathematics).
Sumayya na aji biyu na babbar Sakandire a makarantar Musa Iliyasu College, dake nan daura da sabuwar jamiar Bayeron, suna fitowa ne kullum tare da Yayan ta Dr. Sarham tun bayan fara aikin sa, sai ya sauke ta sannan zai mika zuwa asibitin Murtala inda bai jima da fara aiki ba, bayan yayi aiki na dan lokaci da asibitin Abdullahi Wase da aka fi sani da asibitin Nasarawa, suka maida shi can don an fi bukatar kwararru a asibitin Murtala fiye da kowanne asibitin gwamnati a Kano.
Wannan ya faru ne jim kadan bayan dawowar sa daga kasar Saudi-Arabia da kadan, inda ya karanci fannin likitancin ido a jamiar Sarki Abdul Azeez dake Jeddah.
**** **** ****