Sashe 15
Hauwa Kulu Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Bayan ya sauke Sumayyah ta daga masa hannu, ya ja motar sa zuwa asibiti. Koda ya zo ward round na wannan ranar sai idanun sa suka hango masa gadon da “Hauwa-Kulu” ta kwanta jinya. Nan da nan ya tuno su, wadanda dama da su ya kwana ya kuma tashi a ran sa.
Sai ya ji yana son sake zuwa ya duba su, ya ga lafiyar su itada Innar ta.
Haka kawai yake jin Innar Hauwa a ran sa, jinta yake kamar uwa a gare shi, sabida halin kirkin ta da dattaku, da kuma tawakkalin data nuna akan abinda ya samu yar ta a hannun su.
Don haka da ya fito daga asibiti sai ya samu kansa da juya sitiyarin motar sa zuwa unguwar su Inna, da ya isa bayan Badalar kofar Naisa kasa gane gidan yayi, da tambaya ya isa har kofar gidan su Hauwa don ya kasa ganewa da farko, kansa ma juyewa yayi ya rasa direction abode gidan yayi cikin lungu sosai, amma da yake ya rike sunan maigidan da Inna ta gaya masa kamar ta san zai bata din sai baa sha wahalar kai shi har kofar gidan ba.
Dr. Sarham yayi sallama a kofar gidan Mal. Bilyaminu, Inna dake duke tana share tsakar gidan ta amsa sannan ta leko, koda dau taso daukar muryar dama mai kaifi kamar an fike ta anyi sharpening fitar ta gently daga makogaron sa, bakin ta ya koma har kunne da ganin Dr. Sarham, ta dau wankan ta tsaf ta sha wankakkiyar atampa, kodayake dama ta dauki muryar sa, Inna ta bashi iznin shigowa ya sa kai ya rage dogon wuyan sa ya shigo da sallama.
Inna ta amsa cike da faraa ta shiga lale marhabin da shi, sannan ta dauki tabarmar karauninta ta shimfida masa.
Sarham ya tsuguna har kasa ya sake gaishe da Inna, ya kuma tambayi jikin Hauwa. Inna ta ce cikin damuwa,
ai tun bayan tafiyar ka jiya zazzabi ya rufe Kuluwa, ko tashi bata iya yi, sallah ma sai na taimaka mata take iya yi daga zaune, ta dauki damuwar duniya ta dorawa kanta a banza akan abinda Allah ya kaddara mata. Dr. Sarham ya ce,
ashsha! Kakata jiki bai yi dadi ba ashe, ki barta Inna, dole ne ta damu, amma a hankali damuwar zata bi jikin ta in sha Allah, bari to in koma in samo mata magani.
Har ya mike zai saka takalmin sa sai ya dubi Hauwa dake zaune a kan tabarma daga gefe, ta jingina da filo, ga idanuwan tarr a bude kal dasu, amma shi a iya dan ilmin likitancin ido da Allah ya bashi, da abinda ya karanta, ya san wadannan idanun na Hauwa’u in ba wani babban kudurar Allah ba sun tafi kenan, wato sun tashi aiki sai ko wani ikon Allah, wanda ya fi gaban ilminsu su likitocin fidar idon.
Ya matsa gaban tabarmar ya russuna yace sannu Kakus, ina yake miki ciwo? Don in san irin maganin da zan karbo? Ko allura kike so?” Hauwa ta bata rai sosai saboda sunan da ya kira ta da shi kamar wata tsohuwa, haka mafa a asibiti yace mata Kululu bata ce masa don me ba, yanzu kuma yace mata kuskus, ta dan fiddo manyan idanun kamar tana ganin sa irin warning look dinnan, ta yi fuska sosai ta ce masa, sunana Hauwau Bilyaminu ba kuskus sunana ba, kuma ni ai bana tsoron allura inda a hannu za’a yimin, ba sai na kwaye zani ba”, Inna ta ce an ce miki Kuskus din, ke da baki san wasa ba. Yayi murmushi ya sake cewa.
Kakus, idan na ce miki sunan Kakata gare ki, wadda ta haifi mahaifina zaki yarda? I mean you have my Grandmas name, Hajiya Kulu Shanono”.
Anan kuma sai tayi shiru, don ta san ba karya yake ba, ba kuma zolaya a maganar sa ta yanzu, ta zuba masa gululun idanunta kawai kamar tana ganin sa, yace to sunan ki daya da Kakata Hajiya Kulu (Hajiyar Gadon kaya), ni kuma Kakus nake kiran ta, idan ban kira ki Kakata ba bazan iya cewa Hauwa ba, don in ta ji na fadi sunan ta haka gatsau, ba sakayawa, sai tayi kuli-kulin kubra da ni.
Hauwa bata san sanda ta yi dan murmushi ba, sabida yadda Sarham ya fadi kuli-kulin kuburar ya bata dariya matuka.
Ya ce daga yau ni da kaina zan saka miki sunan da ya dace da kyakkyawar diyar Inna kamar ki, kin ga daga Hauwa, har Hauwau, har Kulu, zuwa Kuluwa duk na tsofaffi ne Inna ta lika miki, don haka ki lamunce min daga yau in kira ki da MAIJIDDAH!.
Ai kuwa nan da nan Hauwa ta washe baki, fararen hakoranta suka bayyana, batun yau take so a kirata da Maijidda ba amma ba mai kiranta da hakan. Dr. Sarham ya ce, amma bisa yarjejeniyar banni arawa kowa sunan nan, nawa ne nikadai, ni na saka miki, don haka nikadai zan kira ki da shi, ke ko wani kika ji ya kira ki da shi ki gaya masa ba nasa bane nawa ne, ban yarda ko Inna ta kwaikwayar mun ba.
Inna tayi dariya tana cin goro ta ji Sarham ya kara burgeta, ko ba komai yau ya saka Hauwa murmushi don ta manta rabon Hauwa’u da murmushi (ear to ear) irin haka, watakila tun kafin ta fara ciwon idon yayi na apolo.
Yadda Sarham yayi ta yi musu hira sai da zazzabin Hauwa ya sauka a take, ba tare da sun san lokacin da ya sauka ba, ko dama damuwa ce ta sanya a ranta ta hanata sukuni har ta saukar mata da zafin jiki, amma duk da haka Sarham bai kyale ta ba saida ya fita chemist din Lamco ya samo mata magunguna da first aid kala-kala ya dawo, har da gorar locozade da daurin gasassar kaza da biredi. Ga kayan shayi ya sayo musu makil, tun daga kan sukari, milo da madara har da lipton.
Lokacin da ya dawo ya tsugunna gaban Inna yana nuna mata komai kasa magana ta yi ta ce dan nan ya da wahala haka? Ya murmusa yace kada ki damu Inna, na neman albarka ne.
Inna ko ta shiga shi masa albarka kwando kwando sannan shi da kan sa ya dau kunshin naman ya isa gaban Hauwa, ya bude ya tura mata gabanta, kamshin kazar nan wadda taji kayan kamshi na gargajiya har cikin kwakwalwar Hauwa wadda rabon ta da abinci dama tun kokon safe da ta dan kurba, don ta rasa ‘appetite’ dinta gabadaya, yace kanwata ci nama ko zazzabi ya idasa tafiya sosai yana ganin yadda ta hadiye miyau, mukut, a makoshin ta, amma don karfin hali da ki-fadi irin na Hauwa sai tayi fuska, ta ce ita ta koshi, sai ya ce “to in ni ne baki so in ga lomar ki, bari in tafi, Inna zan wuce gida sai an kwana biyu, kin san na zama dan ki yanzu, zuwa gidan mu sai kin gaji kin kore ni.
Inna tace wane mutum ya kori mai kaunar sa, likita Allah ya jikan mahaifan ka, idan suna raye kuma Allah ya kara musu lafiya da nisan kwana mai albarka.
Wannan addua tafi komai dadi da ga Sarham, da sauri Dr. Sarham yake amsawa da Amin-amin ya rabbi Inna, Abba da Mama duk suna lafiya, cikin koshin lafiya. Allah ya karawa kanwata Maijidda lafiya, da Yakanar karbar kaddarar ta.
Sai ya ji yana son sake zuwa ya duba su, ya ga lafiyar su itada Innar ta.
Haka kawai yake jin Innar Hauwa a ran sa, jinta yake kamar uwa a gare shi, sabida halin kirkin ta da dattaku, da kuma tawakkalin data nuna akan abinda ya samu yar ta a hannun su.
Don haka da ya fito daga asibiti sai ya samu kansa da juya sitiyarin motar sa zuwa unguwar su Inna, da ya isa bayan Badalar kofar Naisa kasa gane gidan yayi, da tambaya ya isa har kofar gidan su Hauwa don ya kasa ganewa da farko, kansa ma juyewa yayi ya rasa direction abode gidan yayi cikin lungu sosai, amma da yake ya rike sunan maigidan da Inna ta gaya masa kamar ta san zai bata din sai baa sha wahalar kai shi har kofar gidan ba.
Dr. Sarham yayi sallama a kofar gidan Mal. Bilyaminu, Inna dake duke tana share tsakar gidan ta amsa sannan ta leko, koda dau taso daukar muryar dama mai kaifi kamar an fike ta anyi sharpening fitar ta gently daga makogaron sa, bakin ta ya koma har kunne da ganin Dr. Sarham, ta dau wankan ta tsaf ta sha wankakkiyar atampa, kodayake dama ta dauki muryar sa, Inna ta bashi iznin shigowa ya sa kai ya rage dogon wuyan sa ya shigo da sallama.
Inna ta amsa cike da faraa ta shiga lale marhabin da shi, sannan ta dauki tabarmar karauninta ta shimfida masa.
Sarham ya tsuguna har kasa ya sake gaishe da Inna, ya kuma tambayi jikin Hauwa. Inna ta ce cikin damuwa,
ai tun bayan tafiyar ka jiya zazzabi ya rufe Kuluwa, ko tashi bata iya yi, sallah ma sai na taimaka mata take iya yi daga zaune, ta dauki damuwar duniya ta dorawa kanta a banza akan abinda Allah ya kaddara mata. Dr. Sarham ya ce,
ashsha! Kakata jiki bai yi dadi ba ashe, ki barta Inna, dole ne ta damu, amma a hankali damuwar zata bi jikin ta in sha Allah, bari to in koma in samo mata magani.
Har ya mike zai saka takalmin sa sai ya dubi Hauwa dake zaune a kan tabarma daga gefe, ta jingina da filo, ga idanuwan tarr a bude kal dasu, amma shi a iya dan ilmin likitancin ido da Allah ya bashi, da abinda ya karanta, ya san wadannan idanun na Hauwa’u in ba wani babban kudurar Allah ba sun tafi kenan, wato sun tashi aiki sai ko wani ikon Allah, wanda ya fi gaban ilminsu su likitocin fidar idon.
Ya matsa gaban tabarmar ya russuna yace sannu Kakus, ina yake miki ciwo? Don in san irin maganin da zan karbo? Ko allura kike so?” Hauwa ta bata rai sosai saboda sunan da ya kira ta da shi kamar wata tsohuwa, haka mafa a asibiti yace mata Kululu bata ce masa don me ba, yanzu kuma yace mata kuskus, ta dan fiddo manyan idanun kamar tana ganin sa irin warning look dinnan, ta yi fuska sosai ta ce masa, sunana Hauwau Bilyaminu ba kuskus sunana ba, kuma ni ai bana tsoron allura inda a hannu za’a yimin, ba sai na kwaye zani ba”, Inna ta ce an ce miki Kuskus din, ke da baki san wasa ba. Yayi murmushi ya sake cewa.
Kakus, idan na ce miki sunan Kakata gare ki, wadda ta haifi mahaifina zaki yarda? I mean you have my Grandmas name, Hajiya Kulu Shanono”.
Anan kuma sai tayi shiru, don ta san ba karya yake ba, ba kuma zolaya a maganar sa ta yanzu, ta zuba masa gululun idanunta kawai kamar tana ganin sa, yace to sunan ki daya da Kakata Hajiya Kulu (Hajiyar Gadon kaya), ni kuma Kakus nake kiran ta, idan ban kira ki Kakata ba bazan iya cewa Hauwa ba, don in ta ji na fadi sunan ta haka gatsau, ba sakayawa, sai tayi kuli-kulin kubra da ni.
Hauwa bata san sanda ta yi dan murmushi ba, sabida yadda Sarham ya fadi kuli-kulin kuburar ya bata dariya matuka.
Ya ce daga yau ni da kaina zan saka miki sunan da ya dace da kyakkyawar diyar Inna kamar ki, kin ga daga Hauwa, har Hauwau, har Kulu, zuwa Kuluwa duk na tsofaffi ne Inna ta lika miki, don haka ki lamunce min daga yau in kira ki da MAIJIDDAH!.
Ai kuwa nan da nan Hauwa ta washe baki, fararen hakoranta suka bayyana, batun yau take so a kirata da Maijidda ba amma ba mai kiranta da hakan. Dr. Sarham ya ce, amma bisa yarjejeniyar banni arawa kowa sunan nan, nawa ne nikadai, ni na saka miki, don haka nikadai zan kira ki da shi, ke ko wani kika ji ya kira ki da shi ki gaya masa ba nasa bane nawa ne, ban yarda ko Inna ta kwaikwayar mun ba.
Inna tayi dariya tana cin goro ta ji Sarham ya kara burgeta, ko ba komai yau ya saka Hauwa murmushi don ta manta rabon Hauwa’u da murmushi (ear to ear) irin haka, watakila tun kafin ta fara ciwon idon yayi na apolo.
Yadda Sarham yayi ta yi musu hira sai da zazzabin Hauwa ya sauka a take, ba tare da sun san lokacin da ya sauka ba, ko dama damuwa ce ta sanya a ranta ta hanata sukuni har ta saukar mata da zafin jiki, amma duk da haka Sarham bai kyale ta ba saida ya fita chemist din Lamco ya samo mata magunguna da first aid kala-kala ya dawo, har da gorar locozade da daurin gasassar kaza da biredi. Ga kayan shayi ya sayo musu makil, tun daga kan sukari, milo da madara har da lipton.
Lokacin da ya dawo ya tsugunna gaban Inna yana nuna mata komai kasa magana ta yi ta ce dan nan ya da wahala haka? Ya murmusa yace kada ki damu Inna, na neman albarka ne.
Inna ko ta shiga shi masa albarka kwando kwando sannan shi da kan sa ya dau kunshin naman ya isa gaban Hauwa, ya bude ya tura mata gabanta, kamshin kazar nan wadda taji kayan kamshi na gargajiya har cikin kwakwalwar Hauwa wadda rabon ta da abinci dama tun kokon safe da ta dan kurba, don ta rasa ‘appetite’ dinta gabadaya, yace kanwata ci nama ko zazzabi ya idasa tafiya sosai yana ganin yadda ta hadiye miyau, mukut, a makoshin ta, amma don karfin hali da ki-fadi irin na Hauwa sai tayi fuska, ta ce ita ta koshi, sai ya ce “to in ni ne baki so in ga lomar ki, bari in tafi, Inna zan wuce gida sai an kwana biyu, kin san na zama dan ki yanzu, zuwa gidan mu sai kin gaji kin kore ni.
Inna tace wane mutum ya kori mai kaunar sa, likita Allah ya jikan mahaifan ka, idan suna raye kuma Allah ya kara musu lafiya da nisan kwana mai albarka.
Wannan addua tafi komai dadi da ga Sarham, da sauri Dr. Sarham yake amsawa da Amin-amin ya rabbi Inna, Abba da Mama duk suna lafiya, cikin koshin lafiya. Allah ya karawa kanwata Maijidda lafiya, da Yakanar karbar kaddarar ta.