Sashe 75
Furar Danƙo Part 1 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Napep ya samu ta kaisa har ƙofar pharmacy ɗin data kwatanta masa ana iya samun maganin, koda ya basu takardar yaron saida ya kallesa, amma sai baice komai ba ya dai wuce wajen ɗakko masa maganin. Koda ya dawo da maganin ya faɗa masa kuɗin ya cire daga aljihu ya bashi. Napep ya sake samu ta maidashi gida. Yanzu kam sai da ya rufe ko'ina da ɗaukar abubuwan da Ahmad ya siya musu sannan ya nufi ɗakin. Inda ya barta anan ya sameta, sai dai yanzu ta koma ta kwanta. Duk da taji sallamarsa bata motsa ba har sai da ya kai hannu ya yaye bargon data rufa har kanta. Jikinta har tsuma yake lokacin da ya fiddo maganin da ga leda mai tambarin pharmacy ɗin, amma sai tai ƙoƙarin kannewa.
“Yanzu mi zaki ci?”.
Ya faɗa yana ɗagowa ya kalleta. “Ni bana jin yunwa, naci abu tare da Mamy”. Ta bashi amsa idonta akan ledar nan dai. Bai san wa take cema Mamy ɗin ba, sai dai yanda tai maganar cikin serious ya sashi gamsuwa, sai kawai ya cire maganin biyu ya miƙa mata tare da goran ruwa. Bata musa ba ta amsa tasha. Sannu ya sake mata da tattare sauran maganin ya ajiye a bedside drawer da ruwan. Zamewa tai ta sake kwanciya da faɗin, “Sai da safe”.
Murmushi ya ɗan saki ƙasa-ƙasa. Dan ya fahimci korarsa akeyi. Baice mata komai ba ya tattare sauran ledojin ya fice yana rage mata hasken ɗakin. Ajiyar zuciya ta saki mai ƙarfi, sai kuma ta miƙe zumbur da raka bayansa da harara ta dannama ƙofar key sannan ta dawo. Cikin rawar jiki ta fisgi ledar nan ta zazzage kusan ƙwayoyin maganin biyar a tafin hanunta ta afa a baki batare da ruwa ba. Sai da ta haɗiye sannan ta ɗauka ruwan ta kora kaɗan. Wani irin farin ciki take ji na samun kayan nan cikin sauƙi, sai kawai ta faɗa saman gadon cike da jishaɗi tai juyi ta sake juyawa........✍️
_(ALLAH ka rabamu da mummunar ƙaddara. Wlhy irin masu ɗabi'ar nan tausayi suke ban. Dan rayuwar kawai suke batare da sun san ina ta dosa ba, idan sukai nisa sai an dage kafin su bari, ku ga dai, kwana biyu batasha ba amma ta koma kamar mara lafiya. Iyaye dan ALLAH mu ƙara dagewa wa ƴaƴanmu, mu bar aibata ƴaƴan wasu idan muka gamsu a irin wannan halin. ALLAH ka shiryar damu😭🙏)._
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣0️⃣
........Koda Smart ya kai kayan nan kitchen ya adana wanda zai iya lalacewa a fridge sai ya nufi ɗayan ɗakin kasancewar duk yasan sirrikansu, hasalima key ɗin ɗakin na hannunsa dan a rufe yake tun da aka gama shirya masa kaya aunty Saliha ta damƙa masa ko ƴan ganin gidan amarya babu wanda ya leƙa cikinsa. Shima nan ɗin kayane lafiyayyu aka shirya, dan shine ma matsayin master bedroom. Ɗakin yayi ƙyau sosai, komai ya zauna a inda ya dace. Duk da gajiyar da yake ji bai kwanta ba sai ya zare rigarsa da ga shi sai dogon wandon da singlet ya nufi bathroom. Bai jima ba ya fito da alamar alwala yayi, lafiyayyen carpet ɗin gaban gadon ɗakin ya hau dan yin salla. Sallar isha'i yay da shafa'i da wutri. Bayan ya idar yay zaman yin addu'a mai tsayi kafin ya miƙe. Har ya zauna a bakin gadon sai kuma ya miƙe, zuciyarsa ke ayyana masa ya kamata ya binciketa ko tayi sallar isha'i, ya kuma duba ko zazzaɓin ya sauka. Sai dai me, yana taɓa ƙofar ya jita a kulle. Shiru yay yana kallon hannunsa da ke saman handle ɗin, sai kuma ya ɗage kafaɗunsa alamar ko oho ya juya ɗakin da ya fito yay kwanciyarsa dan barci yake ji matuƙa. Dan shi a tunaninsa ko Lulun tayi hakanne dan kar ya nema wani abu a gareta.....
_WASHE GARI_ koda ya tashi sallar asuba sai da ya ƙwanƙwasa mata ƙofa, ganin zai makara saboda ya tashi shima a ƙurarren lokaci ya sashi ƙyaleta ya wuce. Ana idar da sallar ya dawo gidan, ɗakin nata dai ya sake nufa ya ƙara knocking. Lulu da ke kwance a ƙasa ta buɗe idanunta da sukai matuƙar nauyi da ƙyar ta iya miƙewa cikin takaicin damunta da ake tun ɗazun ta nufi ƙofar ta buɗe, dan ta manta ma a ina take, dai da ta ɗan jingina da ƙofar na wani ƴan sakanni sannan ta murɗa key ɗin ta buɗe kaɗan. Da farko bai niyyar shigowa ba, dan haka yace da ita, “Kin tashi kinyi salla ne?”.
“Zanyi”.
Ta amsa masa cikin yanayin muryar maye da tura ƙofar zata rufe dan abun bai gama sakinta ba. Da sauri ya riƙe ƙofar gabansa na faɗuwa, bata da wani isashen ƙarfin dan haka ya samu nasarar shigowa. Yanda ya kafeta da idanunsa da suka kaɗa sukai ja a ƙanƙanin lokaci ya sata zabga masa harara itama da nata dake a juye ta bar masa wajen cikin ɗan tangaɗi na rashin ƙarfi ta je ta faɗa saman gadon a rufda ciki gashinta dake a hargitse ya lulluɓe fuskar tata gaba ɗaya. (Ina ta samu abinda tasha?) Zuciyar sa keta kaikawo wajen son hasasowa amma iya hasashen ya auna a ɗan tsukun lokacin baro gidansu zuwa nan hakan bamai yiwuwa bane, sai dai idan dama tana tare da abunta. Inda take ya ƙarasa ya ɗauki handbag ɗin ta gaba ɗayanta ya zazzage a saman gadon. Babu komai a ciki daya danganci ƙwaya, jakkar ya ajiye cikin furzar da iska sai idanunsa suka sauka kan ledar maganin jiya daya sayo mata, jawo ledar yay ya fiddo maganin, an ƙara ɗiba kusan shida a ciki, ya tsirama maganin ido kallon da yaron pharmacy ɗin ya dinga masa lokacin da ya bashi takardar na dawo masa a rai da zuciya. Tabbas wannan maganin tasha. Kallonsa ya maida gareta ya zuba mata idanu kawai maƙogwaronsa na kai kawo a cikin wuyarsa da ɗan sauri-sauri. Da ga ƙarshe ma sai ya tashi ya fice da ga ɗakin kawai.....
____________________★
Cikin ɓacin rai yake dubansa ganin yanda yake neman haukata kansa. Gaba ɗaya kwanakin nan baida wani aiki sai shaye-shaye tunda ya baro Kano. Ƴar ƙaramar robar giya da ke a hannunsa ya fisge cikin masifa. “Wai mi kake son maida kanka ne kai kuwa MM? Akan mace! Ka zauna ka susuta rayuwarka. Tunda ka dawo da ga kano an kasa gane kanka, ka bar zuwa aiki ka barma fita a gidan nan gaba ɗaya sai shaye-shaye, kana ganin hakan da kake shine zai baka damar samunta? Yarinya sai kace wata autar mata ko hurul-ayni Mtsowww!!!”.
Murmushin takaici MM Atik ya saki sai kuma ga hawaye sharrrr. Ya miƙa hannu zai amshi ƴar robar giyarsa da abokin nasa ya karɓe amma sai ya hanashi. Lips ɗin sa ya ciza da ƙarfi da faɗin, “Bazaka gane ba Asim, duk yanda zan faɗa maka bazaka gane ba. Aure fa sukai mata, aure da wani bani ba. Idan ban mallaketa ba zan iya rasa raina, ina matuƙar sonta da buƙatarta Asim, wlhy da gaske nake ina sonta da gaba ɗaya zuciyata..”
“A haba gyara dai zancenka my man, kana dai sha'awarta. Kai har kasan wata soyayya ne. Ni yanzu Indai dan batun yarinyar nan ne ka nutsu dan ALLAH ka dawo hayyacinka. Ba igiyar aure ba ko ɗaurin kabari sukai mata namaka alƙawarin sai ta dawo taka...”
Wani irin zuba masa ido MM Atik yayi, sai kuma yay murmushi da lumshe idanunsa ya buɗe a lokaci guda, “Asim karka yaudari kanka nima ka yaudarani. Kasan minene aure a ƙasar hausa kuwa?....”
“Mtsoww kafin wannan zamanin yake wani abu a ƙasar hausar, amma a yanzu bana jin wasu matan na tuna matsayin auren, dan ajiyesa suke su shigo barikin ko ƴammatan basu kaisu iskanci ba. Balle ma ita munada hanyoyi kala-kala na kamata a tafin hannunmu. Ko an faɗa maka wani son auren take, to nayi bincike mai zurfi na gane komai har ma yanda aka ƙulla auran. Kai dai kawai ka dawo a hayyacinka kasha labari”. Ya ƙare maganar yana tattare sauran kwalaben giya da su cigarette da shisha da MM Atik ɗin ya baza, sannan ya zo ya kamashi ya kai toilet yasa a ƙarƙashin shower ya sakar masa ruwa. “Malam yi wanka ka cire wannan dattin sai warin hayaƙi kakeyi”. Daga haka ya fice ya barsa.
_____________★
“Yanzu mi zaki ci?”.
Ya faɗa yana ɗagowa ya kalleta. “Ni bana jin yunwa, naci abu tare da Mamy”. Ta bashi amsa idonta akan ledar nan dai. Bai san wa take cema Mamy ɗin ba, sai dai yanda tai maganar cikin serious ya sashi gamsuwa, sai kawai ya cire maganin biyu ya miƙa mata tare da goran ruwa. Bata musa ba ta amsa tasha. Sannu ya sake mata da tattare sauran maganin ya ajiye a bedside drawer da ruwan. Zamewa tai ta sake kwanciya da faɗin, “Sai da safe”.
Murmushi ya ɗan saki ƙasa-ƙasa. Dan ya fahimci korarsa akeyi. Baice mata komai ba ya tattare sauran ledojin ya fice yana rage mata hasken ɗakin. Ajiyar zuciya ta saki mai ƙarfi, sai kuma ta miƙe zumbur da raka bayansa da harara ta dannama ƙofar key sannan ta dawo. Cikin rawar jiki ta fisgi ledar nan ta zazzage kusan ƙwayoyin maganin biyar a tafin hanunta ta afa a baki batare da ruwa ba. Sai da ta haɗiye sannan ta ɗauka ruwan ta kora kaɗan. Wani irin farin ciki take ji na samun kayan nan cikin sauƙi, sai kawai ta faɗa saman gadon cike da jishaɗi tai juyi ta sake juyawa........✍️
_(ALLAH ka rabamu da mummunar ƙaddara. Wlhy irin masu ɗabi'ar nan tausayi suke ban. Dan rayuwar kawai suke batare da sun san ina ta dosa ba, idan sukai nisa sai an dage kafin su bari, ku ga dai, kwana biyu batasha ba amma ta koma kamar mara lafiya. Iyaye dan ALLAH mu ƙara dagewa wa ƴaƴanmu, mu bar aibata ƴaƴan wasu idan muka gamsu a irin wannan halin. ALLAH ka shiryar damu😭🙏)._
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣0️⃣
........Koda Smart ya kai kayan nan kitchen ya adana wanda zai iya lalacewa a fridge sai ya nufi ɗayan ɗakin kasancewar duk yasan sirrikansu, hasalima key ɗin ɗakin na hannunsa dan a rufe yake tun da aka gama shirya masa kaya aunty Saliha ta damƙa masa ko ƴan ganin gidan amarya babu wanda ya leƙa cikinsa. Shima nan ɗin kayane lafiyayyu aka shirya, dan shine ma matsayin master bedroom. Ɗakin yayi ƙyau sosai, komai ya zauna a inda ya dace. Duk da gajiyar da yake ji bai kwanta ba sai ya zare rigarsa da ga shi sai dogon wandon da singlet ya nufi bathroom. Bai jima ba ya fito da alamar alwala yayi, lafiyayyen carpet ɗin gaban gadon ɗakin ya hau dan yin salla. Sallar isha'i yay da shafa'i da wutri. Bayan ya idar yay zaman yin addu'a mai tsayi kafin ya miƙe. Har ya zauna a bakin gadon sai kuma ya miƙe, zuciyarsa ke ayyana masa ya kamata ya binciketa ko tayi sallar isha'i, ya kuma duba ko zazzaɓin ya sauka. Sai dai me, yana taɓa ƙofar ya jita a kulle. Shiru yay yana kallon hannunsa da ke saman handle ɗin, sai kuma ya ɗage kafaɗunsa alamar ko oho ya juya ɗakin da ya fito yay kwanciyarsa dan barci yake ji matuƙa. Dan shi a tunaninsa ko Lulun tayi hakanne dan kar ya nema wani abu a gareta.....
_WASHE GARI_ koda ya tashi sallar asuba sai da ya ƙwanƙwasa mata ƙofa, ganin zai makara saboda ya tashi shima a ƙurarren lokaci ya sashi ƙyaleta ya wuce. Ana idar da sallar ya dawo gidan, ɗakin nata dai ya sake nufa ya ƙara knocking. Lulu da ke kwance a ƙasa ta buɗe idanunta da sukai matuƙar nauyi da ƙyar ta iya miƙewa cikin takaicin damunta da ake tun ɗazun ta nufi ƙofar ta buɗe, dan ta manta ma a ina take, dai da ta ɗan jingina da ƙofar na wani ƴan sakanni sannan ta murɗa key ɗin ta buɗe kaɗan. Da farko bai niyyar shigowa ba, dan haka yace da ita, “Kin tashi kinyi salla ne?”.
“Zanyi”.
Ta amsa masa cikin yanayin muryar maye da tura ƙofar zata rufe dan abun bai gama sakinta ba. Da sauri ya riƙe ƙofar gabansa na faɗuwa, bata da wani isashen ƙarfin dan haka ya samu nasarar shigowa. Yanda ya kafeta da idanunsa da suka kaɗa sukai ja a ƙanƙanin lokaci ya sata zabga masa harara itama da nata dake a juye ta bar masa wajen cikin ɗan tangaɗi na rashin ƙarfi ta je ta faɗa saman gadon a rufda ciki gashinta dake a hargitse ya lulluɓe fuskar tata gaba ɗaya. (Ina ta samu abinda tasha?) Zuciyar sa keta kaikawo wajen son hasasowa amma iya hasashen ya auna a ɗan tsukun lokacin baro gidansu zuwa nan hakan bamai yiwuwa bane, sai dai idan dama tana tare da abunta. Inda take ya ƙarasa ya ɗauki handbag ɗin ta gaba ɗayanta ya zazzage a saman gadon. Babu komai a ciki daya danganci ƙwaya, jakkar ya ajiye cikin furzar da iska sai idanunsa suka sauka kan ledar maganin jiya daya sayo mata, jawo ledar yay ya fiddo maganin, an ƙara ɗiba kusan shida a ciki, ya tsirama maganin ido kallon da yaron pharmacy ɗin ya dinga masa lokacin da ya bashi takardar na dawo masa a rai da zuciya. Tabbas wannan maganin tasha. Kallonsa ya maida gareta ya zuba mata idanu kawai maƙogwaronsa na kai kawo a cikin wuyarsa da ɗan sauri-sauri. Da ga ƙarshe ma sai ya tashi ya fice da ga ɗakin kawai.....
____________________★
Cikin ɓacin rai yake dubansa ganin yanda yake neman haukata kansa. Gaba ɗaya kwanakin nan baida wani aiki sai shaye-shaye tunda ya baro Kano. Ƴar ƙaramar robar giya da ke a hannunsa ya fisge cikin masifa. “Wai mi kake son maida kanka ne kai kuwa MM? Akan mace! Ka zauna ka susuta rayuwarka. Tunda ka dawo da ga kano an kasa gane kanka, ka bar zuwa aiki ka barma fita a gidan nan gaba ɗaya sai shaye-shaye, kana ganin hakan da kake shine zai baka damar samunta? Yarinya sai kace wata autar mata ko hurul-ayni Mtsowww!!!”.
Murmushin takaici MM Atik ya saki sai kuma ga hawaye sharrrr. Ya miƙa hannu zai amshi ƴar robar giyarsa da abokin nasa ya karɓe amma sai ya hanashi. Lips ɗin sa ya ciza da ƙarfi da faɗin, “Bazaka gane ba Asim, duk yanda zan faɗa maka bazaka gane ba. Aure fa sukai mata, aure da wani bani ba. Idan ban mallaketa ba zan iya rasa raina, ina matuƙar sonta da buƙatarta Asim, wlhy da gaske nake ina sonta da gaba ɗaya zuciyata..”
“A haba gyara dai zancenka my man, kana dai sha'awarta. Kai har kasan wata soyayya ne. Ni yanzu Indai dan batun yarinyar nan ne ka nutsu dan ALLAH ka dawo hayyacinka. Ba igiyar aure ba ko ɗaurin kabari sukai mata namaka alƙawarin sai ta dawo taka...”
Wani irin zuba masa ido MM Atik yayi, sai kuma yay murmushi da lumshe idanunsa ya buɗe a lokaci guda, “Asim karka yaudari kanka nima ka yaudarani. Kasan minene aure a ƙasar hausa kuwa?....”
“Mtsoww kafin wannan zamanin yake wani abu a ƙasar hausar, amma a yanzu bana jin wasu matan na tuna matsayin auren, dan ajiyesa suke su shigo barikin ko ƴammatan basu kaisu iskanci ba. Balle ma ita munada hanyoyi kala-kala na kamata a tafin hannunmu. Ko an faɗa maka wani son auren take, to nayi bincike mai zurfi na gane komai har ma yanda aka ƙulla auran. Kai dai kawai ka dawo a hayyacinka kasha labari”. Ya ƙare maganar yana tattare sauran kwalaben giya da su cigarette da shisha da MM Atik ɗin ya baza, sannan ya zo ya kamashi ya kai toilet yasa a ƙarƙashin shower ya sakar masa ruwa. “Malam yi wanka ka cire wannan dattin sai warin hayaƙi kakeyi”. Daga haka ya fice ya barsa.
_____________★