← Book details Furar Danƙo Part 1 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 114

Sashe 32

Furar Danƙo Part 1 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

   Kallon mamaki yake ma matar tasa akan furucinta. Fahimtar hakan ya saka Aunty Saliha sake faɗin, “Wlhy da gaske nake Sweetheart bata nan fa. Alamu ma ya nuna ta jima da barin gidan nan kamar”. Sosai ran Uncle Yousuf ya sake dugunzuma. Dan haka ya cije lips ɗinsa da ƙarfi batare da yace komai ba. Ture shayin gabansa yay tare da miƙewa ya fice a falon. Cike da tausayin mijin nata ta bisa da kallo. Baba maigadi ya gaishesa da girmamawa duk da ganin yau fuskar ubangidan nasa babu walwala. Hannu kawai ya iya ɗaga masa. Sai kuma ya furta “Baba ko akwai wanda ya fita a gidan nan ne bayan yara da suka wuce school?”.
      Baba maigadi da ya ɗan daburce ya shiga in-ina da inda-inda. “Baba tambayarkafa nake? Bana son kwane-kwane ka faɗa min”. Uncle Yousuf ya faɗa da ɗan jin haushi a muryarsa. “Kayi haƙuri Alhaji, abunne dai kamar da ruɗewar kai. Hajiya Muwaddat dai ta fita kam tunda duku-duku kafimma yara su wuce, sai dai abinda ya ɗauremun kai da hargitsani ni banga shigowarta bane shiyyasa na fara tunanin ko junnu ne ke son buɗe min idanu n....”
      Takaici ya saka Uncle Yousuf yin gaba batare da tsayawa jin ƙarashen labarin da yayma kallon na soki burutsu ba. Sai dai harga ALLAH shi baba maigadi iya gaskiyarsa da yake faɗa. Sosai hankalin Uncle Yousuf ɗin ke'a tashe, dan zuciyarsa ta fara masa wasi-wasin karfa taƙi zuwa gida. Yana shiga key ɗin motarsa da ke a dining kawai ya bama aunty Saliha umarnin bashi, bai ma ko saurareta akan magiyar yazo ya ƙarasa break fast ɗinsa baiyi ba ya sake ficewa abinsa. Sai ƙarar buɗe gate da fitar motarsa kawai tajiyo. Addu'ar isa lafiya kawai tai masa dan bata da yanda ta iya tunda tasan ƙaunar da yakema ahalinsa dabance a rayuwa. Bai haɗa son su da komai ba. Ita hakan bai taɓa zame mata matsala ba dan itama suna nuna mata ƙauna a cikinsu. Basu taɓa wareta ba ko nuna mata bambancin kasancewarta bare garesu. Hasalima suna ɗaukar mahaifinta matsayin uba garesu a yanzu fiye da kowa har danginsu na Jiƙamshi. Dan haka bazataima ALLAH butulci ba sai dai ma ta tayashi son danginsa itama tare da musu fatan alkairi musamman akan Mawaddat data zame musu tamkar zakka.........✍️

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗

           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣6️⃣
Chapter 32 · 0% Book details