← Book details Furar Danƙo Part 1 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 114

Sashe 34

Furar Danƙo Part 1 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

★★★ ∆ ★★★

   Smart kam tattara al'amarin Lulu yay ya wancalakar gefe domin fuskantar tasa mai muhimmanci. Gida ya nufa kai tsaye saboda kiran da Abba yay masa. Ya samu gidan da ƴar hayaniyar kasancewar zuwan Sa'id da wasu kawunansa uku. Cikin girmamawa ya gaishesu batare da ya kalla inda Sa'id ya ke gurfane ba kamar mai kuka. Ya maida hankalinsa ga Abba da Hawwah ke a kusa da ƙafafunsa kamar tana kuka itama.
      “Abba gani”.
Ya faɗa cikin dakewarsa. Nisawa Abba yay da nuna Hawwah ya ce, “Kaine ka ɗakko Hauwa'u a gidanta?”.
          “Eh tabbas nine Abba”.
      “Me yasa?”.
  Shiru ya ɗan yi kafin ya nisa. “Abba saboda ta kirani akan ga mahaifiyar mijinta na neman ƙonata da mangyaɗa. Banje gidan da nufin ɗakkota ba sai jin ba'asi na kuma sasanta kamar na baya da akai batare da kun sani ba. Sai dai na samu abin ya wuce yanda nake zatonsa shiyyasa na ɗakkota kafin a cutar da ita tunda mu bawai mun daina sonta bane ba. Ba kuma mun bashi bane dan mun gaji da ita a gidan nan kota gundiremu. Abba abubuwa da yawa sun faru akan auren Hawwah amma ina sasantawa a iya can batare da kai ko Ammah kun taɓa sani ba. Bama ku ba hatta da Aunty Bilkisu ban taɓa sanarmawa ba, kuma na gargaɗi Hawwah sanar ma kowa. Shiyyasa wannan karon na ɗakkota kuma bazata sake koma musu gida ba. Yaje ya auri wadda mahaifiyarsa ke son zama da ita haka nan dan ALLAH kowa ya huta.”........✍️

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗

           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣7️⃣

........Cikin ɓacin rai ƙanin mahaifin Sa'id ya ce, “Ai ba ita kaɗai ce keda iko da shi ba. Sannan kuma ni banga laifinka anan ba yaro. Hasalima abinda kai sai ka birgeni dan kayi abinda ya kamata ace ƴan uwa na ƙwarai suyi akan ƙannensu. Wannan shine girman kuma shine darajtawar.”
      “Tabbas abinda yay yayi dai-dai. Kuma tunda hakane muma kan zamu fidda kammu a wannan zancen ku ɗauki duk matakin da kuke gani shine dai-dai dan halin Rafi'a sam bashi da burgewa. Narasa mitake son maida kanta a rayuwa ita ba ƙaramar yarinya ba amma kullum aita abu guda kamar cin ƙwan makauniya, yanzu da tsautsayi yasa ta samu yarinyar nan da mangyaɗan yaya kenan? Wace amsa take da shi na kare kanta. Dama tausayin yaron nan ya samu tasowa mu biyosa da wuri kafin abin yay zurfi. Amma tunda hakane zamuje muma har sai kun yanke hukunci kafin sannan shima Yaya Ibrahim ɗin ya dawo da ga tafiyar da yayi”.
       Kuka mai tsuma rai Sa'id ya saki, dan harga ALLAH yana matuƙar ƙaunar matarsa Hauwa'u da ƴar ɗiyarsu Nasreen da taci sunan mahaifiyar tasa. Amma hukuncin da iyayen nasa suka yanke yasa bazai iya jayayya da su ba. Babu yanda zai yi ya bisu yana kallon Hawwah da kanta ke ƙasa tun shigiwarta batako kalla sashen da yake ba ma......

      Ajiyar zuciya Abba ya saki a hankali, kamar zai yi magana sai kuma ya fasa. A taƙaice ya ce, “Kuje ciki zamuyi maganar a nutse”. Daga Hawwah har Smart miƙewa sukai suka fice. Babu kowa a tsakar gidan sai Umma da ke kai kawon girkin rana. Yanda bata tanka musu ba suma basu tanka mata ba. Sai dai murmushin data saki akan idon Smart. Shi ba ma'abocin maida hankali bane akan irin waɗan nan abubuwan dan haka yay shigewarsa, sai dai murmushin ya sosa masa zuciya da tsaya masa a rai. Ammah dake zaune a falo Nasreen a cinyarta tana shan kunu kallo ɗaya tai musu ta maida hankalinta ga Nasreen ɗin. Zama yay kamar yanda Hawwah da ke sharar hawaye itama ta zauna. Idanu ya ɗan zuba mata tare da furzar da huci kaɗan. “Shi wannan kukan babu amfanin da zai miki, bakuma zai gyara abinda yake faruwar ba. Kisama ranki haƙuri da nutsuwa, dan bazaki koma wannan gidan ba har sai tasan darajarki. Idan kuma kina ganin ba'ai miki gata ba a hakan dan naga k da mijin naki duk shashashu ne ga hanya nan zaki iya binsu” Daga haka ya miƙe.
           “Kayi haƙuri Yaya ni banga laifinka ba, kuma nagode da ƙoƙarinka a kaina”.
     Komai baice mata ba, sai duban Ammah da tai kamar bata ɗakin da yay. “Ammah ni zan koma”.
        “ALLAH ya tsare ya bada sa'a”. Tace masa batare data ɗago ba. Da Amin ya amsa yana ɗan lakatar kumatun Nasreen da itama tai masa a dawo lafiyar. Da ga haka ya fice abinsa badan yasan ina ya kamata ya dosa ba tunda boss ɗin tasa ta korosa yau.

       Sai da ya fito gaba ɗaya da ga layin nasu zuciyarsa ta kwaɗaita masa zuwa ma ya duba trainers ɗinsu. Dan kwana biyu basuga juna ba. Waya ya ciro tare da ɗan ƙura mata ido kamar mai tunani, sai kuma ya ɗan ɗage kafaɗa tare da kai wayar kunnensa bayan yay dailing number daya lalubo. Bugu uku aka ɗaga, yay ƙaramin murmushi da faɗin, “Barka da hantsi sir”. Amsar da aka bashi da ga can ta sakashi sakin murmushi. Sai kuma ya ɗan shafo kansa alamar jin kunya tamkar yana gabansa. “Am sorry Sir na ɗauka laifina. Yanzu ma ina son zuwa gaishekanne shiyyasa nace bara naji inda kake”. Ya ɗan yi shiru alamar saurare. Sai kuma ya amsa da “Okay gani nan zuwa in sha ALLAHU”.
Chapter 34 · 0% Book details