← Book details Duk Daya Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 15

Sashe 15

Duk Daya Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sau nawa mahmud yazo gidan nan da
bana nan ? ban tanka mishi ba na juya zan
koma dakina sai kawai naji ya figoni ya wurgar
dani Ian kujera nayi mummnunan faduwa, ai in
riga kinyi kuskure da kika zabe ni kika barshi
tun farko da dai kinyi hikima kin dauke shi kika
bar ni a wancan lokacin to da na nuna nuna
miki halacci na don bazan taba daga ido in kalle
ki da wani kallo ba face na matar aboki na to
amma tunda shi yaga zai keta haddin aure na ke
kuma kin yardan mishi yayi hakan to zan nuna
muku iyakar ku ke da shi, ina da hakuri da
tawakkali akan al amura na amma akan wannan
cin zarafin da kuka mun zan tsaya inga iyakar
abin da kuke nufi ya juya zai bar wurin sai ga
wata takarda a yashe a kasa ya sunkuya ya
dauke ta ya zuba mata ido zuwa can ya juyo
yace ga wasikar ki na karba ina duba wa, ga
abin da aka rubuta:
"Na gode kwarai da alkwarin da kika
samu cika mun jiya, nima kuwa nayi kokarin
cika nawa da nayi miki in har zaki samu sarari
tsakanin gode da jibi zan so mu sake haduwa
sai dai zan shawar ce ki, da ki kula kwarai don
kin san mutumnin in har yana gari to zaisa ido
kwarai a kanki, don haka in har kinhango fitan
naki zai zamo da mas ala to kar ki damu sai mu
jira sai ya sake yin wata tafiyar
Sai mun sake saduwa
Na Gode Da Kaunar Da Kike Nuna Mun.

Na saki takardar ta fadi a kasa na daga
ido na kalli sa id nace mishi yayan sahura na
gaji da wadannan al amuran da suke faruwa,
kafi kowa sanin inda kaje ka dauko ni, in akwai
tarbiya a gidan mu ma ka sani, in ma babu
kasani, baka da hujjar zargina da abubuwan da
kake zargina inyi mu'amala da wani na miji
bayan kai, akan wane dalili?

Ban taba yin
sha'awar data zarce taka ba, kaima yaya na kare
da kai balle inje ina neman wani?

Ya zubo ido
yana saurarona cikin natsuwa lokacin da wani
sako ya shigo cikin wayar shi ya duba sakon
sannan ya miko mun wayar na karba ina
dubawa daga bankin da yake mun ajiya ne aka
turo mishi ana baiyana mishi an sake sabunta
account din da wasu zunzurutun kudi da ban
tsaya kallon sub a itama wayar na sake ta a kasa
yace wannan ba alkawarin da akace an cika
miki bane?

Nace shine bazan sake musu da kai
b akan wannan al amarin abu daya dai kawai da
zan sheda maka a yanzu shine ban bukatar
zama da kai tunda har zuciyar ka ta yarda ta
amince da cewar zan 1y aikata wadannan
abubuwan da kake zargina akan su in ka manta
bari in tuna maka kaje ka daukoni ne a gidan da
ake ganin dan halal baya zina kaje ka daukoni
ne a gidan da ake gudun abin kunya saboda
kawai an baka ni ka kawo ni inda bani da kowa
kazo kana wulakan ta ni to ka maidani cikin
dangina sub a zasu taba zargina da abinda kake
yiba, hankali yakai matuka wajen tashi in banda
kuka babu abin da nake yi, sa'id ya juya zai
koma dakin shi sai kawai na mika hannu na rike
rigar dake jikinshi, a sanyaye yace mun sake ni
maryam tun ranki bai baci ba, sannan daga yau
zan miki kashedin inma shi ya bak
shawarar in
muna maganar dake ki rike ni to kar ki sake
sakemun rigata nace bazan saki ba sai ka
salla.....ban karasa ba ya juyo cikin sauri ya
dauke ni da wani gigitaccen mari sai da ya kifar
da ni a kasa ya wuce yayi tafiyar shi ya shige
dakin shi ya turo kofa ya rufe, na gama
kwanciyata anan har na gaji na tashi na koma
daki na kama shirye-shiryen tafiya manbila zan
koma gaban 1yaye na zan koma rayuwata ta
farko ta fimun wannan rayuwar da nake yi a
yanzu, na kara gane gaskiyar ardo da yace mun
babu komai cikin rayvwar birni in banda
kwarauniya da kwamacala na kammala shiri na
tsaf sai dai kuma abin takaicin shine ban
mallaki komai ba in banda naira dubu daya da
dari bakwai a dakina na tsaya ina tunanin ina
zan samu kudin mota'?

Nayi ta tunani na rasa
sai nace to bari tunda tafiya zanyi bari inje in
tunawa sa'id rabon da ya bani kudin aiwatar da
hidimar gida kusan kwana arba' in ne in yaso in
ya bani sai inyi amfani da su kawai, ina i
dakin nashi sai kawai naji shi yana cewa aikin
sun da itan kika bugomun wayar a yanZu tunda
kuwa tsoron da kike magana akai bai hanaki
bugomun wayar dare ba nima kuwa ai bazai
hanani amsawa ba da sauri na bar wurin saboda
wani abin da naji zuciyata tana yi ban taba jin
maganar sa'id da wata mata ba tsawon zaman
da nayi da shi sai ko yau har gari ya waye ina
tsaye a dakina ban samu zama ba balle inyi
tunanin kwanciya malle ta shigo ta sameni a
tsaye gaishe ni kawai tayi ta juya zata tafi nayi
maza nace mata zo mana malle ta dawo ta
tsuguna tace gan
nace mata zani manbila yanzu
kizo mu tafi amma karki gaya wa kowa tace
a'a, bazan biki ba, nayi maza nace mata akan
nme malle?

Na zauna ina rarrashin ta ta yarda ta
bini mu tafi, tace mun a ajiya da daddare tayi
wa yaya sa' id alkawarin zata zauna da shi na
sake kallon ta nace alkawari malle kina
haukane?

Tace mun kiyi hakurI amma na gaji
da irin sabinda kike mishi ace shi da gidan shi
amma wai jiya ya kwana a waje sabaoda gudun
fitinar da zakiyi mishi bayan daga tafiya ya
dawo kuma ai baffa yace mana abinda duk
muka san bama so ayi mana to muma kar
muyiwa wasu da matar yaya jauro take koro shi
waye yake kwana ai tashin hankali kuka rinkayi
da ita to yaya ke kuma zaki so kina Koran yaya
sa'id?

Da sauri nace mata ke malle wane irin
maganar banzane wannan nice zan iya Koran
yayan sahura daga cikin gidahnan?

In baki sani
ba jiya har duka na yayi na kuma ji shi yana
waya a dakin shi suna hira da wata mata nan
take ta kama kuka dadi ya kamani don ina
ganin kukan tausayi na take yi sai kawai naji
tace mun Allah sarki da-da in zaki mance da
komai ai bai kamata ki mance da nasihar baffa
ba ko don soyaiyar da yake miki shi kuwa
nasha jin sh
yana cewa mafi munin abinda dan
adam zai yi shine fadar maganar da ba gaskiya
bace kinre mun ya
uge ki kuma kin ji
hi yana
hira da wata a waya bayan kum
ni yaya sa id a
dakin mu ya kwana yana gaya nmun ya bar nan
dinne sabodd gudun fitinar ki, a kidime nace
mata a wurin ku yayan sahura ya kwana malle?

Tace kwarai kuwa nace to waye ya bugenswaye
naji yana hira da mata a dakin shi?

Tace uhun
ta juya tayi tafiyar ta ta barni nan a zaune tsoro
ya sake kamani ha tabbatar al'amarin dake
faruwa dani don haka babu abinda ya kamace
ni illa in koma gaban iyaye na, a yau dinnan ko
bani da kudin mata da sauri na tashi na dauki
akwatina na saci idon mutanen gidan na nufi
tasha na dauki shatar mota zuwa manbila har
cikin iugarmu na cewa direba to ai zaka shiga
ne ka dan huta sai gobe ka tafi ko?

Yace a'a ni
yanzu zan juya nace to bari in shiga in miko ma
kudin ka yace a'a aini an riga an biyani nace wa
ya biya ka?

Yace a'a w2ce irin tambaya ce
wannan nace to bari ina zuwa nayi maza na tafi
na kira yaya jauro don yazo ya tanbaye direban
motar mutumin dayake cewa va biya shi muna
dawowa muka ga babu shi habu dalilin shi, na
kalli yaya jauro cikin matsanancin tsoro da
fargaba nace mishi yaya jauro anan fa direban
motar ya tsaya yace ashe har ya ar nan wurin
ya bace daga tsaunukan nan da suke kewaye da
mu?

Yaya jauro vace ke suengel nifa dama ban
wani ji motsin wata mota ba ganin ki kawai
nayi kin shigo da jakar ki.

Ina jin yaya jauro ya fadi haka na yanke
jiki na fadi a kasa na suma.

Masu karatu sai ayi mun hakuri abiyo ni
littafi na hudu don jin karslhen labarin ayi
hakuri kwarai don kuwa ban so jan labarin
haka ba, bai zai kammalau bane cikin littafi
na uku ba.
124
Na Gode.

Taku
Hafsat Chindo Sodangi.

SADAKA GA MATA DAKE DA MAS ALA DA
MAZAJEN SU
Su yawaita karanta wannan ayar
dake cikin Suratul Yusuf (Alaihis -
Salam):
"Rabbi Kad Ataita Ni Minal Mulki
Wa Allamtani Min Ta'awilil Ahadis
Fadirus Samawati Wal Ardi Anta
Waliyyi Fidduniya Wal Akhira
Tawaffani Musliman Wa Alhikni
Bissalihin"
Ubangijin Mu Allahu Yasa Mu
doge Amin Sunma Amin.

In Kika
Dimance karanta ta Allah Zai Baki
Zaman Iafiya Da Mijin Ki.

SAKO
Ga wadan da suka samu mas'alar
rashin fahintar wani abu cikin littafin
matn da kicin dinsu suna iya aiko da
tanbaya ta cikin wannan layin dana bayar
cikin wancan littafin. 07035586299,
Allah Ya taimake mu amin.
126
SummaryInformation
DocumentSummaryInformation
WpsCustomData
TECNO LD7
WPS Office
Normal
Times New Roman
Times New Roman
Calibri
Calibri
!%),.:;>?]}
$([{
ed9f3e0a2ede4458a7cd31dfba2aeff9
Chapter 15 · 0% Book details