Sashe 14
Duk Daya Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya
zubamun ido yana kallona yace wadannan duk
kudin kine seungel da kika yi ta wahala kina
neman su, kusan shekaru hudu baki taba
daukan ko kwandala ba, gashi kin bani su a
matsayin rance babu wanda ya sani, watakila
kuma kin taba jin labarin cin manar maza da
kuke cewa ko ince rashin alkwarin su na matan
su su tallaba musu lokacin da suke wani abu na
neman ci gaba in kuma bukatar su ta biya sai
suyiwa matan nasu tukuici da kishiya, bakya
tunanin nima zan iya yi miki haka? nace ban
sani ba, ni dai abinda na sani shine kawai alheri
nake nufi yace haka ne, to misali innayi miki
irin wannan din fa tunda nima miji ne ban kuma
banbanta da sauran maza masu yin hakan ba
yaya zakiyi?
Nace Allah ba zai hanani yanda
zanyi ba, ya sake cewa hakane, 'n kara tunani in
gani ko zan karbi kudi na kawai a sayamun
wata kadara ko shiga na a matsayin rance, nace
mishi yayi amfani da su kawai.
Nan da nan aka sayi fili aka Katangeshi
aka gayara komai aka gama ni da umma da
tasi'u muka je ganin wurin umma, ta tara ce
mishi ai kuwa dah har kace zaka hakura da
wannan din, saboda kudin ka baza su kai ba
yace eh umma maryam ce ta bani kudin ta tace
in hada umma tace to Allah ya kara rufa asiri
yace amin.
Wata guda bayan nan tasi'u suka dawo
daga manbila, shanun da ardo ya baiwa sa'id
sukaje daukowa suka hado da nasu, ni ma ardo
ya aikomun da yanmatan shanu wadan da basu
taba haihuwa ba guda ashirin da bijimaye uku
da akuyoyi irin na manbila masu manyan
kunnuwa, suma guda goma da bunsurayen su
uku, yace a kawo mun inyi iri, shikenan sai aka
soma kiwo an riga an sanya kaji a wurin su, an
zuba leyas an zuba buroilas.
Tasi'u sa'id ya sanya a matsayin mai
kula da gonar ya kuma dibi ma'aikata su hudu
tare da masu gadin gonar suma su hudu, a haka
aka soma.
Ranran ya dawo daga gonar da.
yanma hankalinshi a tashe yake yana gaya mun
wani yanayi da ya gani a jikin shanun ya kuma
kira likitan dabbobin da yake duba su ammaa
bayanin da yayi mishi shi bai gamsu da shi ba,
nace to ko zanje ne in duba in gani gobe in
Allah Ya kaimu?
Yace yau wa maryam in kinyi
hakan ai kin taimaka.
Washegari da safe nayi shiri kwalliya
mai kyau nayi cikin wata doguwar riga har kasa
dinkin senegal na daura dankwali a kaina na
kuma yafa gyale na madaidaici na sanya
takalmi na lowshoe mai kyan gaske ga
waraiwarai da zobuna sun kama hannu na sai
daukan ido sukeyi nayiwa umma sallama muka
fita ni sa' id zuwa gonar nayi matukar jin dadin
ganin dabbobin gidan mu cikin murmushi da jin
dadi na shiga cikin su sa'id yana mun kashedin
harbi fa suke yin ace mishi ai sun sanni ba zasu
manta niba, na matsa jikin su ina duba su nace
mishi bafa wata mas'ala ban, canjin wuri ne
kawai da kuma ciwon da wasu sukayi a kofato
da za'a bani sabuwar reza da almakashi zan
gyara musu kofato da sauri, ya sa aka kawo
mun ina karba sai yace mun to bari inje nan
wurin da ake Fada mana abincin su ba bazan fi
minti taiatin ba, zan dawo sai in kaiki gida nace
ko awa daya ba laifi yace to sai na dawo nace to
Allah Ya bada sa'a.
Said yana barin wurin na shiga yin aiki
na har n agama ina kara dudduba su sai naji ina
shakkar kamshin wani turare da baimun kama
da na miji na ba, na juya maza na waiwaya don
inga waye mai wannan kamshin?
Mahmud na
gani tsaye a bayana gabana yayi matukar
fadiwa don kuwa nayi ma rabon da in ganshi
tun zuwan da suka yi da sa'id nayi musu bari
sai ko yau, ya sakn mun wani lallausan
murmushi yace sengel kenan kin kara kyau kin
kara gwarjini kin waye kin zama matar birni
banyi kokari ba dana hango ki daga nesa na
gane ki?
Rabon da in ganki fa tun kina amarya
saboda na gane mai gidan bai son zuwa na
gidan shi, a zuciyata nace babu damuwa tunda
dai nasan kina so na, nayi maza nace mishi
waya gaya maka haka?
Ya sake wani
murmushin yace aiyukan ki suke nuna mun
rashin jaruntakar ki a kusa da ni shike kara
baiyanar mun da asirin zuciyar ki in daga ido
don in baiwa Mahmud amsa sai kawai ga sa id
a bayan shi yana tsaye fargaba da tscro suka a
kamani jikina ya sake daukan wani rawan ganin
yanda yanayi naya sauya gaba daya yasa
Mahmud yayi saurin juyawa don ganin abin da
ke faruwa yana murmushi kuwa bai motsa ba
daga yanda yake, hannayen shi duka biyu suna
cikin aljihun shi yace mishi barka dai.
Bansan yanda aka yi ba sai na tsinci
kaina dace mishi har ka dawo?
Ya zubamun ido
Cikin natsuwa yace nayi sauri ko? nayi maza
nace mishi a'a don na gane kuskuren tanbayar
da nayi mishin, yaya in kin gama mu tafi ko?
nace to na wuce na barsu shi da Mahmud ban
san me suka tattauna ba.
Tun daga hanya na lura shan iska yake yi
nima sai na tsira muna isa gida kuwa naje na
gaya wa uinma dawowan mu na wuce dakina
na turo kofa ta na rufe har na hau gado na na
kwanta sai gashi yazo ya tsaya mun a bakin
kofar dakina dama kun shirya zaku hadu acan
ne? bakin ciki da takaicin tanbayar yasa na
amsa cewar eh, ya zubo mun ido cikin natsuwa
yace yayi kyau, haka din ba kuma laifin ki
bane, sakarci nane ya jawomun hakan in bah
aka ba ai na dade da zargin akwai wani abinda
ke gudana tsakanin ku amma na krsa daukan
mataki mai tsanani, saboda ina tsoron abinda
zai kawo batanci a tsakanina da ke nayi maza
nace me kake nufi yayan sahura da irin wadan
nan kalaman naka?
Yace abinda kika gayamun
kin san kowanne dan adam yana da jarrabawar
shi a rayuwa, ai an jarrabe ni da son wacce bata
sona duk abubuwan da kike yi tayi mun na
nuna mun kiyaiya a zahiri na kasa hakura da
ken a kasa daukan mataki mai tsanani akan ki,
saboda zuciyata ta kasa jaruntakar yin hakan to
gashi yanzu gashiii... .. yana cikin maganar ya
soma haki da sauri da sauri saboda tsananin
bacin rai nayi maza na isa gare shi don in kai
mishi dauki tare da fadin bah aka bane yayan
sahura ina dora hannuna a jikin shi yayi maza
ya hankade ni kar ki sake kar ki sake yin
nnan gangancin ki barni kawai ki kyale ni ki
fita hanya ta kar ki sake taba ni.
Tsoro ya kara kamani ganin yanda sa'id
ya fita cikin haiyacin shi cikin dan takaitaccen
lokaci na taso nazo kusa da shin a durkusa
yayan sahura bafa komai tsakani na da
Mahmud da sauri yace mun karki karamun
wani bakin cikin kar ki nemi ki mai da ni wani
mahaukaci sabo da rawai kinga duk abinda
kike yina kasayin komai bayan na fara zargin
wannan al'amarin bana kama wasikan Mahmud
da yawa a gidan nan sunanan kuma ina ajiye
dasu nama dauki sabon complimentry card din
shi a cikin falon nan na kuma san bani nazo da
shi ba, na zaro ido cikin matsananncin tsoro ban
taba sanin akwai irin wannan zargin a tsakani
na da shi ba, zargi a tsakanina da mijina,
wannan al'amari ya muna na Inna Lillahi Wa
Inna llaihir Raju'un' abinda kawai nake ta fadi
kenan cikin zuciyata.
Zama na da sa'id ya shiga wani hali na
wani irin matsanancin tsananin da ban taba
tsanmanin zama tsakanin mace da mijin ta
yakan kai wannan matsayin ba, na rasa inda
zansa raina inji dadi nayi kamar inje in kai
maganar wurin umma sai kuma nayi wani
tunani nace to ai watakila su dukan su sun dade
suna mun irin wannan zargin dana zauna nayi
tunani mai zurfi sai naga ni karshen wulakanci
da tozartawan da sa'id zai mun kenan, shi ne
nay a zauna dani yana zargi na akan ina auren
shi ina mu'amala da wani can daban to akan
me?
Akan bukata ta ta zarce tashi ko kuma
akan zai bani wani abin duniya?
Ina zaune da
sa'id a haka rannan sai aka wayi gari da safe
ban ji motsin shi ba har yamman tayi bangan
shi ba babu shi babu dalilin shi, hankali na yayi
matukar tashi saboda ko bama kula juna ni da
shi amma kuma muna jin motsin shiga da fitar
juna, na tashi na fito cikin dare na bude kofar
dake tsakanin na da umma don inje in tanbaye
ta ko ta san wani abu game da shi ina shiga
cikin gidan sai na fasa yin hakan, saboda yanda
na same su dukkan su suna barci, na tabbatar
idan yana cikin wani hali babu yanda za'ayi
gidan yayi shiru haka, na juya na dawo wuri na
nayi alwala nayi sallah sannan na hau gadona
na kwanta.
Washegari da safe wurin malle na
samu labarin sa'id ya na Senegal sai da ya cika
sati biyu ya dawo ina jin kwarainiyar oyoyon
da akc mishi ban je ba, har ya gama zaman shi
wurin umma ban shiga ba, ya shigo wurin mu
ya nufi wurin shi ban kula shi ba, ina kwance a
dakina sai naji yana kwala nin kira na taso
nazo batare da na amsa ba.
zubamun ido yana kallona yace wadannan duk
kudin kine seungel da kika yi ta wahala kina
neman su, kusan shekaru hudu baki taba
daukan ko kwandala ba, gashi kin bani su a
matsayin rance babu wanda ya sani, watakila
kuma kin taba jin labarin cin manar maza da
kuke cewa ko ince rashin alkwarin su na matan
su su tallaba musu lokacin da suke wani abu na
neman ci gaba in kuma bukatar su ta biya sai
suyiwa matan nasu tukuici da kishiya, bakya
tunanin nima zan iya yi miki haka? nace ban
sani ba, ni dai abinda na sani shine kawai alheri
nake nufi yace haka ne, to misali innayi miki
irin wannan din fa tunda nima miji ne ban kuma
banbanta da sauran maza masu yin hakan ba
yaya zakiyi?
Nace Allah ba zai hanani yanda
zanyi ba, ya sake cewa hakane, 'n kara tunani in
gani ko zan karbi kudi na kawai a sayamun
wata kadara ko shiga na a matsayin rance, nace
mishi yayi amfani da su kawai.
Nan da nan aka sayi fili aka Katangeshi
aka gayara komai aka gama ni da umma da
tasi'u muka je ganin wurin umma, ta tara ce
mishi ai kuwa dah har kace zaka hakura da
wannan din, saboda kudin ka baza su kai ba
yace eh umma maryam ce ta bani kudin ta tace
in hada umma tace to Allah ya kara rufa asiri
yace amin.
Wata guda bayan nan tasi'u suka dawo
daga manbila, shanun da ardo ya baiwa sa'id
sukaje daukowa suka hado da nasu, ni ma ardo
ya aikomun da yanmatan shanu wadan da basu
taba haihuwa ba guda ashirin da bijimaye uku
da akuyoyi irin na manbila masu manyan
kunnuwa, suma guda goma da bunsurayen su
uku, yace a kawo mun inyi iri, shikenan sai aka
soma kiwo an riga an sanya kaji a wurin su, an
zuba leyas an zuba buroilas.
Tasi'u sa'id ya sanya a matsayin mai
kula da gonar ya kuma dibi ma'aikata su hudu
tare da masu gadin gonar suma su hudu, a haka
aka soma.
Ranran ya dawo daga gonar da.
yanma hankalinshi a tashe yake yana gaya mun
wani yanayi da ya gani a jikin shanun ya kuma
kira likitan dabbobin da yake duba su ammaa
bayanin da yayi mishi shi bai gamsu da shi ba,
nace to ko zanje ne in duba in gani gobe in
Allah Ya kaimu?
Yace yau wa maryam in kinyi
hakan ai kin taimaka.
Washegari da safe nayi shiri kwalliya
mai kyau nayi cikin wata doguwar riga har kasa
dinkin senegal na daura dankwali a kaina na
kuma yafa gyale na madaidaici na sanya
takalmi na lowshoe mai kyan gaske ga
waraiwarai da zobuna sun kama hannu na sai
daukan ido sukeyi nayiwa umma sallama muka
fita ni sa' id zuwa gonar nayi matukar jin dadin
ganin dabbobin gidan mu cikin murmushi da jin
dadi na shiga cikin su sa'id yana mun kashedin
harbi fa suke yin ace mishi ai sun sanni ba zasu
manta niba, na matsa jikin su ina duba su nace
mishi bafa wata mas'ala ban, canjin wuri ne
kawai da kuma ciwon da wasu sukayi a kofato
da za'a bani sabuwar reza da almakashi zan
gyara musu kofato da sauri, ya sa aka kawo
mun ina karba sai yace mun to bari inje nan
wurin da ake Fada mana abincin su ba bazan fi
minti taiatin ba, zan dawo sai in kaiki gida nace
ko awa daya ba laifi yace to sai na dawo nace to
Allah Ya bada sa'a.
Said yana barin wurin na shiga yin aiki
na har n agama ina kara dudduba su sai naji ina
shakkar kamshin wani turare da baimun kama
da na miji na ba, na juya maza na waiwaya don
inga waye mai wannan kamshin?
Mahmud na
gani tsaye a bayana gabana yayi matukar
fadiwa don kuwa nayi ma rabon da in ganshi
tun zuwan da suka yi da sa'id nayi musu bari
sai ko yau, ya sakn mun wani lallausan
murmushi yace sengel kenan kin kara kyau kin
kara gwarjini kin waye kin zama matar birni
banyi kokari ba dana hango ki daga nesa na
gane ki?
Rabon da in ganki fa tun kina amarya
saboda na gane mai gidan bai son zuwa na
gidan shi, a zuciyata nace babu damuwa tunda
dai nasan kina so na, nayi maza nace mishi
waya gaya maka haka?
Ya sake wani
murmushin yace aiyukan ki suke nuna mun
rashin jaruntakar ki a kusa da ni shike kara
baiyanar mun da asirin zuciyar ki in daga ido
don in baiwa Mahmud amsa sai kawai ga sa id
a bayan shi yana tsaye fargaba da tscro suka a
kamani jikina ya sake daukan wani rawan ganin
yanda yanayi naya sauya gaba daya yasa
Mahmud yayi saurin juyawa don ganin abin da
ke faruwa yana murmushi kuwa bai motsa ba
daga yanda yake, hannayen shi duka biyu suna
cikin aljihun shi yace mishi barka dai.
Bansan yanda aka yi ba sai na tsinci
kaina dace mishi har ka dawo?
Ya zubamun ido
Cikin natsuwa yace nayi sauri ko? nayi maza
nace mishi a'a don na gane kuskuren tanbayar
da nayi mishin, yaya in kin gama mu tafi ko?
nace to na wuce na barsu shi da Mahmud ban
san me suka tattauna ba.
Tun daga hanya na lura shan iska yake yi
nima sai na tsira muna isa gida kuwa naje na
gaya wa uinma dawowan mu na wuce dakina
na turo kofa ta na rufe har na hau gado na na
kwanta sai gashi yazo ya tsaya mun a bakin
kofar dakina dama kun shirya zaku hadu acan
ne? bakin ciki da takaicin tanbayar yasa na
amsa cewar eh, ya zubo mun ido cikin natsuwa
yace yayi kyau, haka din ba kuma laifin ki
bane, sakarci nane ya jawomun hakan in bah
aka ba ai na dade da zargin akwai wani abinda
ke gudana tsakanin ku amma na krsa daukan
mataki mai tsanani, saboda ina tsoron abinda
zai kawo batanci a tsakanina da ke nayi maza
nace me kake nufi yayan sahura da irin wadan
nan kalaman naka?
Yace abinda kika gayamun
kin san kowanne dan adam yana da jarrabawar
shi a rayuwa, ai an jarrabe ni da son wacce bata
sona duk abubuwan da kike yi tayi mun na
nuna mun kiyaiya a zahiri na kasa hakura da
ken a kasa daukan mataki mai tsanani akan ki,
saboda zuciyata ta kasa jaruntakar yin hakan to
gashi yanzu gashiii... .. yana cikin maganar ya
soma haki da sauri da sauri saboda tsananin
bacin rai nayi maza na isa gare shi don in kai
mishi dauki tare da fadin bah aka bane yayan
sahura ina dora hannuna a jikin shi yayi maza
ya hankade ni kar ki sake kar ki sake yin
nnan gangancin ki barni kawai ki kyale ni ki
fita hanya ta kar ki sake taba ni.
Tsoro ya kara kamani ganin yanda sa'id
ya fita cikin haiyacin shi cikin dan takaitaccen
lokaci na taso nazo kusa da shin a durkusa
yayan sahura bafa komai tsakani na da
Mahmud da sauri yace mun karki karamun
wani bakin cikin kar ki nemi ki mai da ni wani
mahaukaci sabo da rawai kinga duk abinda
kike yina kasayin komai bayan na fara zargin
wannan al'amarin bana kama wasikan Mahmud
da yawa a gidan nan sunanan kuma ina ajiye
dasu nama dauki sabon complimentry card din
shi a cikin falon nan na kuma san bani nazo da
shi ba, na zaro ido cikin matsananncin tsoro ban
taba sanin akwai irin wannan zargin a tsakani
na da shi ba, zargi a tsakanina da mijina,
wannan al'amari ya muna na Inna Lillahi Wa
Inna llaihir Raju'un' abinda kawai nake ta fadi
kenan cikin zuciyata.
Zama na da sa'id ya shiga wani hali na
wani irin matsanancin tsananin da ban taba
tsanmanin zama tsakanin mace da mijin ta
yakan kai wannan matsayin ba, na rasa inda
zansa raina inji dadi nayi kamar inje in kai
maganar wurin umma sai kuma nayi wani
tunani nace to ai watakila su dukan su sun dade
suna mun irin wannan zargin dana zauna nayi
tunani mai zurfi sai naga ni karshen wulakanci
da tozartawan da sa'id zai mun kenan, shi ne
nay a zauna dani yana zargi na akan ina auren
shi ina mu'amala da wani can daban to akan
me?
Akan bukata ta ta zarce tashi ko kuma
akan zai bani wani abin duniya?
Ina zaune da
sa'id a haka rannan sai aka wayi gari da safe
ban ji motsin shi ba har yamman tayi bangan
shi ba babu shi babu dalilin shi, hankali na yayi
matukar tashi saboda ko bama kula juna ni da
shi amma kuma muna jin motsin shiga da fitar
juna, na tashi na fito cikin dare na bude kofar
dake tsakanin na da umma don inje in tanbaye
ta ko ta san wani abu game da shi ina shiga
cikin gidan sai na fasa yin hakan, saboda yanda
na same su dukkan su suna barci, na tabbatar
idan yana cikin wani hali babu yanda za'ayi
gidan yayi shiru haka, na juya na dawo wuri na
nayi alwala nayi sallah sannan na hau gadona
na kwanta.
Washegari da safe wurin malle na
samu labarin sa'id ya na Senegal sai da ya cika
sati biyu ya dawo ina jin kwarainiyar oyoyon
da akc mishi ban je ba, har ya gama zaman shi
wurin umma ban shiga ba, ya shigo wurin mu
ya nufi wurin shi ban kula shi ba, ina kwance a
dakina sai naji yana kwala nin kira na taso
nazo batare da na amsa ba.