Sashe 8
Auren Shehu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ni na kawo ki nan? Ko kin ga sanda na dauko ki? Ki tuna yanda aka yi ki ka zo sai ki koma da kan ki, matukar ba haka ba ki shirya zama karkashi na a matsayayin miji ke kuma baiwa ta......."
"Ba za ka taba zama miji gare ni ba! Uban kuturu yayi kadan! Ni ce baiwar ta ka? Ka san dawa ka ke kuwa? Da na zauna karkashin ka gwara na kwanta kabari!"
Ta katse shi a fusace, ta na mai daukar akwaitin ta ta furta
"Fine zan nemi hanya ta da kai na, Amma dukkan ku ku kuka da kan ku! Sai kun dandana gudar ku!"
Ta fara jan akwaitin ta, wayar ta dake ta kukan neman chaji ta duba ko alamar sabis ya dawo, fadi ta ke
"Wawaye jahilai kawai! no wonder aka ce a guji iskancin bakauye! Kun ci sa'a network di na ya dauke da ban ma tsaya musayar magana da almajirai irin ku ba, ka yi da diyar halak"
Ko da ta karasa wajan yara da iyayen su mata, sai su ka ki dara mata hanya, a fusace ta ce
"Dallah ku matsa min na wuce! Duk karnin manshanu ku ke da warin rana! Ga warin talauci! Kai wannan masifa har ina! Kazamai kawai!"
Ganin da gaske ba su da niyar matsawa ya sanya ta juya ta kalli Usman
"ka fada mu su su bani hanya ko na ci kaniyar su wallahi!"
Usman ya kawar da kai gefe ba tare da ya tanka ba, Bello ne ya taso ya ce da mata da yaran su bata hanya ta wuce cikin harshen fulatanci sannan su ka buda mata hanya, sai a sannan Zainab ta gan shi da kyau, ta gane shi ne kanin Usman da aka kamo. Ta na duban Bello ta ce
"Halan ba ka bashi labarin kashin da ka sha ba ne shi ya sa be daddara ba! Toh tun wuri ka masa bayani idan ma giyar wake ya sha gwara ya wattsake! Sakakkaru kawai!"
Tana gama maganar ta ja akwaitin ta. Bata kula da kugin yunwa da cikin ta ya ke mata ba, bare ta tuna da sallar asubahi da ke kan ya, ta na takawa da kyar ta doshi wata yar siririyar hanya da take tunanin shi zai fitar da ita hanyar da zai sada ta ga titin barin Rugar Shehu, nan kuwa bata san dokar daji ta kara nufa ba. da sauri Bello ya dawo wajan Usman ya ce
"Ta tafi fa Shehu, hanyar da ta dosa hanya ce da zai kara batar da ita cikin dokar daji, ka ga yanda ta ke tafiya da kyar, gashi akwai hatsari sosai cikin dajin kasan bata daya daga cikin mu, halittun dajin ba su san da zaman ta ba kada ta je ta hakala, ba za ka dakatar da ita ba?"
Usman na duban mata da yara ya ce kowa ya koma harkokin sa, haka kuma ya gyara zama in da ya ba da umarnin su cigaba da tattauna abin da su ke tattaunawa kafin zuwan Zainab. Ganin haka Bello ya san Usman be da niyar amsa masa, dan haka shi ma ya koma wajan zaman sa, zuciyar na da tunanin dangantakar da ke tsakanin Zainab da Shehun su, da kuma halin da Zainab za ta iya shiga cikin dokar daji.
*Khadija Sidi*
Auren Shehu 2
4
In da Ammy da Anty Sauda ke cikin fargaban halin da Zainab ta ke ciki, Zainab kuwa kasa daurewa ta yi, cikin akwatin ta ta sami dankwalin wata atamfar ta dinkin doguwar riga, hannun ta dauke da buta ta sa kai ta fito daga bukka.
Hankalin ta yayi gaba bare ta lura da jama'ar da ke kallan ta, ta na dingisawa kai tsaye bandakin da aka nuna mata ta sake komawa. Ta na shiga ta sami busasshen waje nan ta baje dankwalin ta saboda gudun cutar bandaki, sannan ta tsugunna ta gandara kashin ta sai da ta kasayar da komai sannan ta dawo hayyacin ta. Cike da kyamkayamin kan ta ta matsa daga gefe ta yi tsarki, Nan ta bar mu su kashin ta fito ta na yarfe hannu ta shige daki cikin akwatin ta ta dauko sabulun wankan ta da Allah ya sa ta hado da shi, ta sake fitowa tsakar gidan tana waige waige ko Allah ya sa ta ga boki.
Allah ya taimake ta ta hangi bokitin karfe, cikin dauriya ta karasa wajan bokiti, ganin babu komai ciki ta zara ta na waigawa lungu da sakon nema ma'ajiyar ruwa. Ta karaci waige waigen ta ko rijiya ba ta hanga ba bare famfo, haka kuma tambayar jama'ar gidan da suka mayar da ita tamkar talabijin bata lokaci ne. Idanun ta ne su ka sauka kan randuna manya guda uku, duka rufe da murfin langa, kawannan su da moda bisa kai. Kai tsaye ta nufi randar, ta fara duba na farko ta ga ba ruwa, na biyun kuma ruwan ya kai rabi, sai na ukun ne cike da ruwa. Wani dan yaro ta kalla ta ce
"Kai zo ka zuba min ruwa...."
Yaro ya tsaya ya na kallan ta ba tare da ya motsa ba, Zainab ta ja tsaki yayinda ta aje bokitin, hannun ta na dama ta sa ta bude randar, da modar da ta gani bisa randar ta debo ruwa ta na mai murzar sabulu ta wanke hannun ta, sannan ta goga sabulun cikin bokitin ta na cudawa da hannun ta. Kan ka ce me tuni yara sun matso suna mamakin kumfar da sabalun Zainab ke bayarwa, dan kuwa ba kowa ba ne ke samun damar wanka da omo bare kuma uwa uba sabulu.
Sai da ta wanke bokitin tas, ta dauraye da ruwan randar nan da dama rabi ne ciki, har ta karar da ruwan, sannan kuma ta bude randar da ke cike da ruwa, Amma babu damar dauka, hannun ta ruke da sabulun ta, ta jefa modar cikin bokiti ta fara ja, ta yi ta na hutawa haka kuma ruwa be fasa zubewa ba, haka ta shige bukka ta na jiyo maganganun mata gidan da ta tabbatar da ita su ke akan ruwan da ta kwasa.
Cikin bukka ta aje bokitin gefe guda, tana mai tura kwararen abincin da aka aje mata karkashin gadon kara, ta sa hannu ta tattare yar ledar da ke shimfide, da ke dama ba wata ledar arziki ba ce, bukkar ya zama sai kasa ne kamar yanda tsakar gida da bandaki. Assabarin daki ta saka ta na fadin
"Duk wanda ya shigo kan sa yayiwa in ba dai wannan tsinannan ba ne"
Ta na mai juyawa kofa baya ta cire kayan ta, ya rage daga ita sai dan fantari. Nan tsakar bukkar ta dau moda ta shiga kwararawa jikin ta ruwa, duk sanda ruwan ya sauka jikin ta sai ta kusan shidewa tsabagen sanyi, Amma haka ta zake dantse ta cigaba watsa ruwa ta na kwashewa Usman albarka.
Can tsakar gida kuwa kanwar mahaifyar Usman wato Iyalle ce ta shiga bandaki, Nan ta tarar da kashin Zainab malale bisa dankwali. Ta juyo ta na salati da sallallami ta ke shedawa jama'ar gidan ta'asar da Kado ta mu su na bahaya a bandaki. Hansai matar Kawu Iliya wacce dama ta fi kowa zafi cikin gidan ce ta fusata cikin harshen fulatanci ta ce
"Kan uban can! Kashi ta mana a bayi? Ita sarauniya ba za ta iya yankar daji ba? Nan fa kuna kallo ta kwashe ruwan shan gidan nan kaf ta shige daka da shi! Zan yi magana aka hana ni! Wallahi ba za sabu ba!"
Fuuuu ta wuce bukkar Usman, su Iyalle na tsayar da ita amma ta mu su banza, ta na isa bakin bukkar ta sa hannu ta daga assabari ta cusa kai, Nan ta yi arba da Zainab daga ita sai fantari ta juya baya ta na saba jikin ta sabulu. Hansai ta saki assabari ta na salati har da kuka fadi ta ke
"Innalillahi ni Hansai an cuce ni! Wayyo na shiga uku na lalace wannan Kadon be da mutunci! Wayyo na yi gamo Allah ya isa ban yafe ba! Wayyoo...."
Da gudun ta ta bar bakin kofar bukkar in da ta tsugunna musu a tsakar gida ta na rafka ihu kamar wacce aka aikowa sakon mutuwa, jama'a na tambayar ta lafiya amma ta kasa magana sai nuni ta ke ga bukkar Shehu, Iyalle ta yi kokarin zuwa ta duba abin da ya birkita Hansai haka amma Hansai ta ruke kafar ta, fadi ta ke
"kada wanda ya je kusa da bukkan can! Ku kira Shehu! Fitina ta sauka Rugar Shehu! Masifa ta saukar mana!"
Zainab kuwa tun da ta ji alamar an daga assabari gaban ta ya fadi, jin salatin mace ya tabbatar mata ba Usman ba ne ya leko, cikin azama ta dauraye jikin ta tas ruwa na malalewa tsakar dakin. Bisa gadon kara ta haye, tana daga durkushe ta fitar da dan towel din ta ta tsane jikin ta sannan ta daura, ko da ta duba ta ga tana da fantari har hudu cikin akwatin ta, wulgi ta yi da wanda ta cire. Kaya set biyar ne kacal cikin jakar, atamfa dinkin doguwar riga guda uku, duk da akan kallabin daya daga ciki ta yi kashi, sai kuma dogwayen ruguna, wanda ta bar makaranta sanye jikin ta da shi, da kuma wata koriya mara hannu, sai panties guda hudu, da bra guda hudu, sai kuma bumshort din ta guda biyu da yan rugunan su suma guda biyu. Koriyar doguwar rigar ta fitar, cikin azama ta ke shiryawa saboda hayaniyar da take jiyowa daga waje duk da dai ba ta san takamammen abun da ake cewa ba.
*****
Usman na zaune fadar Shehu, tattaunawa su ke akan maganar cigaba da Shehu ya kawo mu su, wato na azancin Shugaban kasa Muhammdu Buhari akan 'Ruga settlement policy'. Cewar shi zai so ace Rugar Shehu na daya daga cikin Rugar da za ta amfana da wannan tsari da shugaban kasa ke kokarin kafawa cikin kasar Nigeria. Kawu Iliya ne ya nisa, kana ya ce
"Ba za ka taba zama miji gare ni ba! Uban kuturu yayi kadan! Ni ce baiwar ta ka? Ka san dawa ka ke kuwa? Da na zauna karkashin ka gwara na kwanta kabari!"
Ta katse shi a fusace, ta na mai daukar akwaitin ta ta furta
"Fine zan nemi hanya ta da kai na, Amma dukkan ku ku kuka da kan ku! Sai kun dandana gudar ku!"
Ta fara jan akwaitin ta, wayar ta dake ta kukan neman chaji ta duba ko alamar sabis ya dawo, fadi ta ke
"Wawaye jahilai kawai! no wonder aka ce a guji iskancin bakauye! Kun ci sa'a network di na ya dauke da ban ma tsaya musayar magana da almajirai irin ku ba, ka yi da diyar halak"
Ko da ta karasa wajan yara da iyayen su mata, sai su ka ki dara mata hanya, a fusace ta ce
"Dallah ku matsa min na wuce! Duk karnin manshanu ku ke da warin rana! Ga warin talauci! Kai wannan masifa har ina! Kazamai kawai!"
Ganin da gaske ba su da niyar matsawa ya sanya ta juya ta kalli Usman
"ka fada mu su su bani hanya ko na ci kaniyar su wallahi!"
Usman ya kawar da kai gefe ba tare da ya tanka ba, Bello ne ya taso ya ce da mata da yaran su bata hanya ta wuce cikin harshen fulatanci sannan su ka buda mata hanya, sai a sannan Zainab ta gan shi da kyau, ta gane shi ne kanin Usman da aka kamo. Ta na duban Bello ta ce
"Halan ba ka bashi labarin kashin da ka sha ba ne shi ya sa be daddara ba! Toh tun wuri ka masa bayani idan ma giyar wake ya sha gwara ya wattsake! Sakakkaru kawai!"
Tana gama maganar ta ja akwaitin ta. Bata kula da kugin yunwa da cikin ta ya ke mata ba, bare ta tuna da sallar asubahi da ke kan ya, ta na takawa da kyar ta doshi wata yar siririyar hanya da take tunanin shi zai fitar da ita hanyar da zai sada ta ga titin barin Rugar Shehu, nan kuwa bata san dokar daji ta kara nufa ba. da sauri Bello ya dawo wajan Usman ya ce
"Ta tafi fa Shehu, hanyar da ta dosa hanya ce da zai kara batar da ita cikin dokar daji, ka ga yanda ta ke tafiya da kyar, gashi akwai hatsari sosai cikin dajin kasan bata daya daga cikin mu, halittun dajin ba su san da zaman ta ba kada ta je ta hakala, ba za ka dakatar da ita ba?"
Usman na duban mata da yara ya ce kowa ya koma harkokin sa, haka kuma ya gyara zama in da ya ba da umarnin su cigaba da tattauna abin da su ke tattaunawa kafin zuwan Zainab. Ganin haka Bello ya san Usman be da niyar amsa masa, dan haka shi ma ya koma wajan zaman sa, zuciyar na da tunanin dangantakar da ke tsakanin Zainab da Shehun su, da kuma halin da Zainab za ta iya shiga cikin dokar daji.
*Khadija Sidi*
Auren Shehu 2
4
In da Ammy da Anty Sauda ke cikin fargaban halin da Zainab ta ke ciki, Zainab kuwa kasa daurewa ta yi, cikin akwatin ta ta sami dankwalin wata atamfar ta dinkin doguwar riga, hannun ta dauke da buta ta sa kai ta fito daga bukka.
Hankalin ta yayi gaba bare ta lura da jama'ar da ke kallan ta, ta na dingisawa kai tsaye bandakin da aka nuna mata ta sake komawa. Ta na shiga ta sami busasshen waje nan ta baje dankwalin ta saboda gudun cutar bandaki, sannan ta tsugunna ta gandara kashin ta sai da ta kasayar da komai sannan ta dawo hayyacin ta. Cike da kyamkayamin kan ta ta matsa daga gefe ta yi tsarki, Nan ta bar mu su kashin ta fito ta na yarfe hannu ta shige daki cikin akwatin ta ta dauko sabulun wankan ta da Allah ya sa ta hado da shi, ta sake fitowa tsakar gidan tana waige waige ko Allah ya sa ta ga boki.
Allah ya taimake ta ta hangi bokitin karfe, cikin dauriya ta karasa wajan bokiti, ganin babu komai ciki ta zara ta na waigawa lungu da sakon nema ma'ajiyar ruwa. Ta karaci waige waigen ta ko rijiya ba ta hanga ba bare famfo, haka kuma tambayar jama'ar gidan da suka mayar da ita tamkar talabijin bata lokaci ne. Idanun ta ne su ka sauka kan randuna manya guda uku, duka rufe da murfin langa, kawannan su da moda bisa kai. Kai tsaye ta nufi randar, ta fara duba na farko ta ga ba ruwa, na biyun kuma ruwan ya kai rabi, sai na ukun ne cike da ruwa. Wani dan yaro ta kalla ta ce
"Kai zo ka zuba min ruwa...."
Yaro ya tsaya ya na kallan ta ba tare da ya motsa ba, Zainab ta ja tsaki yayinda ta aje bokitin, hannun ta na dama ta sa ta bude randar, da modar da ta gani bisa randar ta debo ruwa ta na mai murzar sabulu ta wanke hannun ta, sannan ta goga sabulun cikin bokitin ta na cudawa da hannun ta. Kan ka ce me tuni yara sun matso suna mamakin kumfar da sabalun Zainab ke bayarwa, dan kuwa ba kowa ba ne ke samun damar wanka da omo bare kuma uwa uba sabulu.
Sai da ta wanke bokitin tas, ta dauraye da ruwan randar nan da dama rabi ne ciki, har ta karar da ruwan, sannan kuma ta bude randar da ke cike da ruwa, Amma babu damar dauka, hannun ta ruke da sabulun ta, ta jefa modar cikin bokiti ta fara ja, ta yi ta na hutawa haka kuma ruwa be fasa zubewa ba, haka ta shige bukka ta na jiyo maganganun mata gidan da ta tabbatar da ita su ke akan ruwan da ta kwasa.
Cikin bukka ta aje bokitin gefe guda, tana mai tura kwararen abincin da aka aje mata karkashin gadon kara, ta sa hannu ta tattare yar ledar da ke shimfide, da ke dama ba wata ledar arziki ba ce, bukkar ya zama sai kasa ne kamar yanda tsakar gida da bandaki. Assabarin daki ta saka ta na fadin
"Duk wanda ya shigo kan sa yayiwa in ba dai wannan tsinannan ba ne"
Ta na mai juyawa kofa baya ta cire kayan ta, ya rage daga ita sai dan fantari. Nan tsakar bukkar ta dau moda ta shiga kwararawa jikin ta ruwa, duk sanda ruwan ya sauka jikin ta sai ta kusan shidewa tsabagen sanyi, Amma haka ta zake dantse ta cigaba watsa ruwa ta na kwashewa Usman albarka.
Can tsakar gida kuwa kanwar mahaifyar Usman wato Iyalle ce ta shiga bandaki, Nan ta tarar da kashin Zainab malale bisa dankwali. Ta juyo ta na salati da sallallami ta ke shedawa jama'ar gidan ta'asar da Kado ta mu su na bahaya a bandaki. Hansai matar Kawu Iliya wacce dama ta fi kowa zafi cikin gidan ce ta fusata cikin harshen fulatanci ta ce
"Kan uban can! Kashi ta mana a bayi? Ita sarauniya ba za ta iya yankar daji ba? Nan fa kuna kallo ta kwashe ruwan shan gidan nan kaf ta shige daka da shi! Zan yi magana aka hana ni! Wallahi ba za sabu ba!"
Fuuuu ta wuce bukkar Usman, su Iyalle na tsayar da ita amma ta mu su banza, ta na isa bakin bukkar ta sa hannu ta daga assabari ta cusa kai, Nan ta yi arba da Zainab daga ita sai fantari ta juya baya ta na saba jikin ta sabulu. Hansai ta saki assabari ta na salati har da kuka fadi ta ke
"Innalillahi ni Hansai an cuce ni! Wayyo na shiga uku na lalace wannan Kadon be da mutunci! Wayyo na yi gamo Allah ya isa ban yafe ba! Wayyoo...."
Da gudun ta ta bar bakin kofar bukkar in da ta tsugunna musu a tsakar gida ta na rafka ihu kamar wacce aka aikowa sakon mutuwa, jama'a na tambayar ta lafiya amma ta kasa magana sai nuni ta ke ga bukkar Shehu, Iyalle ta yi kokarin zuwa ta duba abin da ya birkita Hansai haka amma Hansai ta ruke kafar ta, fadi ta ke
"kada wanda ya je kusa da bukkan can! Ku kira Shehu! Fitina ta sauka Rugar Shehu! Masifa ta saukar mana!"
Zainab kuwa tun da ta ji alamar an daga assabari gaban ta ya fadi, jin salatin mace ya tabbatar mata ba Usman ba ne ya leko, cikin azama ta dauraye jikin ta tas ruwa na malalewa tsakar dakin. Bisa gadon kara ta haye, tana daga durkushe ta fitar da dan towel din ta ta tsane jikin ta sannan ta daura, ko da ta duba ta ga tana da fantari har hudu cikin akwatin ta, wulgi ta yi da wanda ta cire. Kaya set biyar ne kacal cikin jakar, atamfa dinkin doguwar riga guda uku, duk da akan kallabin daya daga ciki ta yi kashi, sai kuma dogwayen ruguna, wanda ta bar makaranta sanye jikin ta da shi, da kuma wata koriya mara hannu, sai panties guda hudu, da bra guda hudu, sai kuma bumshort din ta guda biyu da yan rugunan su suma guda biyu. Koriyar doguwar rigar ta fitar, cikin azama ta ke shiryawa saboda hayaniyar da take jiyowa daga waje duk da dai ba ta san takamammen abun da ake cewa ba.
*****
Usman na zaune fadar Shehu, tattaunawa su ke akan maganar cigaba da Shehu ya kawo mu su, wato na azancin Shugaban kasa Muhammdu Buhari akan 'Ruga settlement policy'. Cewar shi zai so ace Rugar Shehu na daya daga cikin Rugar da za ta amfana da wannan tsari da shugaban kasa ke kokarin kafawa cikin kasar Nigeria. Kawu Iliya ne ya nisa, kana ya ce