Sashe 6
Auren Shehu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ya aka yi ta zama matar ka? Dama ka yi aure ban sani ba?"
"Zan maka bayani daga baya, yanzu na gaji matuka"
"Shin ya aka yi ta yarda ta biyo ka? Nonon da ka bata yanzu kar dai......?
Bello ya kasa karasa maganar cikin shakkar tambayar da zai yi. Usman na mai girgiza kai ya ce
"Kiranye?"
Bello ya girgiza kai. Usman na mai murmushin mugunta ya cigaba da fadin
"Tabbas shi na mata, shi ne hanya mafi sauki da zan iya taho da ita, ka ga wannan yarinyar da ke kwance bisa gado na? Hatsabibiya ce, fitinanniya ce dan haka kada ka taba tausaya mata! Idan har ka ga na mata wani abu na alkhairi toh ka tabbata darajar mahaifin ta za ta ci, na kuma ba ta makarin kiranyen da na mata ba don komai ba da dai ina bukatar ta cikin hayyacin ta, ina so na gan ta cikin kunci kamar yanda zuciya ta take cikin kunci!"
Jikin Bello ne yayi sanyi kwarai, tun da ya zo duniya be taba ganin Usman cikin halin bacin rai da neman daukar fansa kamar yanda ya ke a yau ba, shi da ya sha duka ma be kullece ta kamar yanda Usman ya kulla ce ta ba, lalle Zainab abar a tausaya mata ce tunda ta iya tado fushin mai hakuri, tabbas ta kai bango.
"Ka na nufin babu soyayyar ta cikin ran ka?"
Cewar Bello cikin adduar Allah ya saukaka. Usman na mai girgiza kai ya furta
"Daukar fansa shi ya kawo Abu Rugar Shehu, Abu ce mace ta karshe da zan iya so a duniya!"
Ya na gama fadin haka ya wuce ya bar Bello cikin tunani da sakar zuci.
*Khadija Sidi*
Auren Shehu 2
3
Allah yayi dare gari ya waye, carar zakara tare da kukan shanu, gami da guje guje da ihu da yara ke yi ne ya sanya Zainab sanya hannayen ta bisa kunnuwan ta, tare da runtse idanu, ga wani zugin azama da take ji a kafafun ta, haka kuma kan ta ya mata nauyi. Tun tana jin komai tamkar cikin mafarki, har ya fi karfin kunnuwan ta ya kai ga sanya ta bude idanu a hankali. Maimakon ta ga silin da fanka sai ganin karare ta yi jere reras, idanun ta ta rufe a karo na biyu ta na mai fatan farkawa daga mafarkin da ta ke. Ko da ta sake budewa ta ga dai har lokacin rufin kara idanun ta ke gane mata ta shi zaune a firgice ta na mai bin bukkar da idanu, bukka ce maidaidaciya wacce aka gina da jar kasa mai dauke da yayin ciyawa da rufin kara. A kideme ta kai kallan ta ga in da ta ke kwance, sai a sannan ta lura da gadon kara mai dauke da matacciyar katifar da ta ke zaune kai. A hankali ta ke karewa bukkar kallo tundaga ledar da ke shimfide kasan bukkar, har zuwa koren akwaitin karfe da ke aje gefe kusa da katan kwaryar da aka rufe da wani fefe, sai butoci guda biyu, na roba da na karfe.
"Mafarki na ke!"
Cewar Zainab ta na mai duban kayan da ke jikin ta, sam ta kasa tuna sanda ta sanya shi, abun da za ta tuna kadai shi ne sanda ta ke karatu cikin dare ba kayan ba ne jikin ta. Ta na jinjina kai ta kara fadin
"Da na gama karatu bacci ya sace ni, shi ne na ke mafarki! Da kabari kato ake yin shi da sai na ce mutuwa na yi, bari dai na koma bacci ko Allah zai sa na farka!"
Ta na maganar ne yayinda ta koma ta kwanta tare da rufe idanun ta. Jim kadan taurin gadon karen ya dame ta, haka ma hayaniyar yara da ta ke jiyowa daga waje ya sa duk yanda taso ta koma bacci ko Allah ya sa ta tashi ya gagara. Tsaki ta ja ta na mai tashi da sauri da niyar ta fita ta tsawatarwa ma su hayaniyar, ko da ta taka kafarta wani raradi ne ya ziyarci kwakwalwar ta har sai da ta koma ta zauna da sauri tana fadin
"Wayyoo Dady!"
Sai a sannan ta lura da yanayin kumburi da kafafun ta su ka yi. Hakan ne ya karasa ta tsorata da halin da ta tsinci kan ta ciki. A haka ta yi karfin hali ta tashi ta na mai takawa da kyar wanda duk sanda ta taka sai ta cije lebe har ta kai ga assabarin da aka saka bakin kofar daki, hannun ta biyu ta saka ta daga shi nan ta yi tozali da abin da tun da ta zo duniya ba ta taba gani ba, kanta ya zuye ya na mai sarawa ganin bukkai ba adadi, gabas da yamma kudu da arewa, Rugace ta gargajiya tsantsa in da jama'ar wajan mata da yara ke kai kawo cikin kwanciyar hankali.
Matan sanye da rigar saki irin na fulani mai hade da zani, in da wasu su ka sanya fari, wasun su shudi ne jikin su, duk da akwai dankwali kan su, sun saki jiki rabashe rabashe su na hidimar su, daga mai share na su bangaran bukkar, sai mai kwasar manshanu daga cikin kwaryar nonon da ta tatso tare da taimakon yara mata guda hudu wanda ba su fi shekara goma sha uku ba, can gefe kuwa mata ne guda shida wanda dudu ba za su haura shekara ishirin ba amma gaba daya cikin su ya sake saboda wahala, musammam kirgin su wanda ya ya kwanta sharkaf kamar tsumma, sun zage dantse wajan dakan geron fura. Kusa da su mata biyu ne zaune daga gani ka san kishiyoyi ne, suna cin abinci hannu baka hannu kwarya, daya daga cikin su dauke da yaro akan cinya ta tana ba shi nonan da tsabagen yanda ya kwanta kai ka ce tsumma ne. Daga can gefe kuwa tsoffine guda biyu zaune suna koyawa yara mata guda biyu da ke zaune gaban su sakar riga, wanda za su kimanin shekara goma. Sai kuma yara maza da ke wasan langa sun yi kacaca tsabagen wasan bazan da su ke yi cikin kasa. Sai kuma
Yaran ne su ka fara ganin Zainab wacce ta saki baki da hanci ta na kallan sarautar Allah. Shirun da yaran su ka yi ya ja hankalin iyayen su ka ankare da Zainab. Kamar yanda ta bude baki ta na kallan su haka su ma su ka bude baki su na kallan ta cike da mamaki. Sun ji labarin Shehu ya dawo da Kado Rugar Shehu, wanda har aka mu su kashedin kada wanda ya yarda yayi wani yare cikin Rugar face fulatanci, musammam ga Kado, Amma sam ba su taba tunanin irin wannan kadon Shehun su ya kawo Ruga ba.
Kallon Zainab su ke tun daga dankwalin da ke kan ta, zuwa doguwar riga mara hannu da ke sanye jikin ta, surar Zainab, da kuma yanayin fatar ta da ya fita daban, duk da yawancin su farare ne, ita baka ce amma yanda fatar Zainab ya ke subul subul ya na sheki kadai abin kallo ne.
Tuni su ka fara kuskus a junan su, in da yara su sa tafi suna fadin
"Kado! Kado! Kado"
Hakan ne ya sanya Zainab sakin assabarin da sauri cikin faduwar gaba, ta na dingishi jikin ta har rawa ya ke ta komo cikin bukkar. Cikin yanayin tashin hankali ta ke kara duban bukkar, gani ta ke kamar za ta ga wata alama da zai bayyana mata halin dimuwar da ta tsinci kan ta ciki.
Ganin jikin wani abu kamar akwaitin ta leko ta karkashin gado ya sanya Zainab ta karasa gaban gadon da dingishi, dan gaba daya ji tayi zafin kafar ya dena damun ta. Cikin zafin nama ta janyo akwatin, ganin nata ne da gaske ta ji wani dan sanyi cikin ranta yayinda ta bude da sauri ta na mai mamakin yanda aka yi akwaitin ya je in da ta ganshi ta zuge zip din akwatin, haka kuma kayan ta da ke ciki ya bata mamaki dan kuwa ba za ta iya tuna sanda ta jera kayan cikin akwatin ba.
Ciki ta yi kacibus da wayar ta, da murnar ta ta dauko wayar, hannu na rawa ta kunna ganin a kashe ta ke. Allah Allah ta ke ya gama kunnuwa ta samu ta kira waya ko Allah ya sa ta sami mafita, amma ko da wayar ta kunnu ta shiga cikin wajan kira sai taga anbuga mata waya a adadi, kuma duka miskul ne, kiran Ammy ya fi sau goma, haka ma na Falmat da sauran yan ajin su. Sakon waya kuwa su ma ga su nan birjik.
Jin wayar na kugin neman chaji ne ya sa Zainab dena duba kira da sakonnin da aka tura mata, ta shiga kokarin kiran Ammy kafin wayar ta mutu, Nan ma wani tashin hankali ne ya ziyarci idanun ta, domin kuwa wayar nunawa ta yi ba za ta iya kiran kowa ba sanadiyar rashin sabis, haka kuma wajan da ke nuna alamar sabis a wayar ma ya dauke gaba daya, a sannan Zainab ta dada jaddada kalmar 'babu sarki sai Allah'
Zufa na ketowa daga goshin ta rufe akwatin, hannun ta ruke da wayar ta tashi tsaye ta na dingisawa ta sanya silfas din da ke aje kusa da akwatin na ta, ta ja akwatin yayinda ta bude assabari ta fito waje, cak ta tsaya ganin yanda yaran nan da iyayan su duka su ka baro abin da su ke, su ka yi da'ira bakin kofar bukkar Shehu kamar masu jiran tsammani.
Babban abin da ya kara tsorata Zainab shi ne yanda su ka karu dan kuwa har na gona sai da yaran nan su ka je su ka kira su zo su ka ga Kado a dakin Shehu. Zainab na mai ja da baya cikin dakiya da rashin nuna tsoro ta ce
"Ban san ko su waye ba! Ban san wata duniya na ke ba! Ban kuma damu da na sani ba! Roko na daya dan Allah....ku nuna min hanyar da zan koma tawa duniyar! Kada ku cutar da ni....."
"Zan maka bayani daga baya, yanzu na gaji matuka"
"Shin ya aka yi ta yarda ta biyo ka? Nonon da ka bata yanzu kar dai......?
Bello ya kasa karasa maganar cikin shakkar tambayar da zai yi. Usman na mai girgiza kai ya ce
"Kiranye?"
Bello ya girgiza kai. Usman na mai murmushin mugunta ya cigaba da fadin
"Tabbas shi na mata, shi ne hanya mafi sauki da zan iya taho da ita, ka ga wannan yarinyar da ke kwance bisa gado na? Hatsabibiya ce, fitinanniya ce dan haka kada ka taba tausaya mata! Idan har ka ga na mata wani abu na alkhairi toh ka tabbata darajar mahaifin ta za ta ci, na kuma ba ta makarin kiranyen da na mata ba don komai ba da dai ina bukatar ta cikin hayyacin ta, ina so na gan ta cikin kunci kamar yanda zuciya ta take cikin kunci!"
Jikin Bello ne yayi sanyi kwarai, tun da ya zo duniya be taba ganin Usman cikin halin bacin rai da neman daukar fansa kamar yanda ya ke a yau ba, shi da ya sha duka ma be kullece ta kamar yanda Usman ya kulla ce ta ba, lalle Zainab abar a tausaya mata ce tunda ta iya tado fushin mai hakuri, tabbas ta kai bango.
"Ka na nufin babu soyayyar ta cikin ran ka?"
Cewar Bello cikin adduar Allah ya saukaka. Usman na mai girgiza kai ya furta
"Daukar fansa shi ya kawo Abu Rugar Shehu, Abu ce mace ta karshe da zan iya so a duniya!"
Ya na gama fadin haka ya wuce ya bar Bello cikin tunani da sakar zuci.
*Khadija Sidi*
Auren Shehu 2
3
Allah yayi dare gari ya waye, carar zakara tare da kukan shanu, gami da guje guje da ihu da yara ke yi ne ya sanya Zainab sanya hannayen ta bisa kunnuwan ta, tare da runtse idanu, ga wani zugin azama da take ji a kafafun ta, haka kuma kan ta ya mata nauyi. Tun tana jin komai tamkar cikin mafarki, har ya fi karfin kunnuwan ta ya kai ga sanya ta bude idanu a hankali. Maimakon ta ga silin da fanka sai ganin karare ta yi jere reras, idanun ta ta rufe a karo na biyu ta na mai fatan farkawa daga mafarkin da ta ke. Ko da ta sake budewa ta ga dai har lokacin rufin kara idanun ta ke gane mata ta shi zaune a firgice ta na mai bin bukkar da idanu, bukka ce maidaidaciya wacce aka gina da jar kasa mai dauke da yayin ciyawa da rufin kara. A kideme ta kai kallan ta ga in da ta ke kwance, sai a sannan ta lura da gadon kara mai dauke da matacciyar katifar da ta ke zaune kai. A hankali ta ke karewa bukkar kallo tundaga ledar da ke shimfide kasan bukkar, har zuwa koren akwaitin karfe da ke aje gefe kusa da katan kwaryar da aka rufe da wani fefe, sai butoci guda biyu, na roba da na karfe.
"Mafarki na ke!"
Cewar Zainab ta na mai duban kayan da ke jikin ta, sam ta kasa tuna sanda ta sanya shi, abun da za ta tuna kadai shi ne sanda ta ke karatu cikin dare ba kayan ba ne jikin ta. Ta na jinjina kai ta kara fadin
"Da na gama karatu bacci ya sace ni, shi ne na ke mafarki! Da kabari kato ake yin shi da sai na ce mutuwa na yi, bari dai na koma bacci ko Allah zai sa na farka!"
Ta na maganar ne yayinda ta koma ta kwanta tare da rufe idanun ta. Jim kadan taurin gadon karen ya dame ta, haka ma hayaniyar yara da ta ke jiyowa daga waje ya sa duk yanda taso ta koma bacci ko Allah ya sa ta tashi ya gagara. Tsaki ta ja ta na mai tashi da sauri da niyar ta fita ta tsawatarwa ma su hayaniyar, ko da ta taka kafarta wani raradi ne ya ziyarci kwakwalwar ta har sai da ta koma ta zauna da sauri tana fadin
"Wayyoo Dady!"
Sai a sannan ta lura da yanayin kumburi da kafafun ta su ka yi. Hakan ne ya karasa ta tsorata da halin da ta tsinci kan ta ciki. A haka ta yi karfin hali ta tashi ta na mai takawa da kyar wanda duk sanda ta taka sai ta cije lebe har ta kai ga assabarin da aka saka bakin kofar daki, hannun ta biyu ta saka ta daga shi nan ta yi tozali da abin da tun da ta zo duniya ba ta taba gani ba, kanta ya zuye ya na mai sarawa ganin bukkai ba adadi, gabas da yamma kudu da arewa, Rugace ta gargajiya tsantsa in da jama'ar wajan mata da yara ke kai kawo cikin kwanciyar hankali.
Matan sanye da rigar saki irin na fulani mai hade da zani, in da wasu su ka sanya fari, wasun su shudi ne jikin su, duk da akwai dankwali kan su, sun saki jiki rabashe rabashe su na hidimar su, daga mai share na su bangaran bukkar, sai mai kwasar manshanu daga cikin kwaryar nonon da ta tatso tare da taimakon yara mata guda hudu wanda ba su fi shekara goma sha uku ba, can gefe kuwa mata ne guda shida wanda dudu ba za su haura shekara ishirin ba amma gaba daya cikin su ya sake saboda wahala, musammam kirgin su wanda ya ya kwanta sharkaf kamar tsumma, sun zage dantse wajan dakan geron fura. Kusa da su mata biyu ne zaune daga gani ka san kishiyoyi ne, suna cin abinci hannu baka hannu kwarya, daya daga cikin su dauke da yaro akan cinya ta tana ba shi nonan da tsabagen yanda ya kwanta kai ka ce tsumma ne. Daga can gefe kuwa tsoffine guda biyu zaune suna koyawa yara mata guda biyu da ke zaune gaban su sakar riga, wanda za su kimanin shekara goma. Sai kuma yara maza da ke wasan langa sun yi kacaca tsabagen wasan bazan da su ke yi cikin kasa. Sai kuma
Yaran ne su ka fara ganin Zainab wacce ta saki baki da hanci ta na kallan sarautar Allah. Shirun da yaran su ka yi ya ja hankalin iyayen su ka ankare da Zainab. Kamar yanda ta bude baki ta na kallan su haka su ma su ka bude baki su na kallan ta cike da mamaki. Sun ji labarin Shehu ya dawo da Kado Rugar Shehu, wanda har aka mu su kashedin kada wanda ya yarda yayi wani yare cikin Rugar face fulatanci, musammam ga Kado, Amma sam ba su taba tunanin irin wannan kadon Shehun su ya kawo Ruga ba.
Kallon Zainab su ke tun daga dankwalin da ke kan ta, zuwa doguwar riga mara hannu da ke sanye jikin ta, surar Zainab, da kuma yanayin fatar ta da ya fita daban, duk da yawancin su farare ne, ita baka ce amma yanda fatar Zainab ya ke subul subul ya na sheki kadai abin kallo ne.
Tuni su ka fara kuskus a junan su, in da yara su sa tafi suna fadin
"Kado! Kado! Kado"
Hakan ne ya sanya Zainab sakin assabarin da sauri cikin faduwar gaba, ta na dingishi jikin ta har rawa ya ke ta komo cikin bukkar. Cikin yanayin tashin hankali ta ke kara duban bukkar, gani ta ke kamar za ta ga wata alama da zai bayyana mata halin dimuwar da ta tsinci kan ta ciki.
Ganin jikin wani abu kamar akwaitin ta leko ta karkashin gado ya sanya Zainab ta karasa gaban gadon da dingishi, dan gaba daya ji tayi zafin kafar ya dena damun ta. Cikin zafin nama ta janyo akwatin, ganin nata ne da gaske ta ji wani dan sanyi cikin ranta yayinda ta bude da sauri ta na mai mamakin yanda aka yi akwaitin ya je in da ta ganshi ta zuge zip din akwatin, haka kuma kayan ta da ke ciki ya bata mamaki dan kuwa ba za ta iya tuna sanda ta jera kayan cikin akwatin ba.
Ciki ta yi kacibus da wayar ta, da murnar ta ta dauko wayar, hannu na rawa ta kunna ganin a kashe ta ke. Allah Allah ta ke ya gama kunnuwa ta samu ta kira waya ko Allah ya sa ta sami mafita, amma ko da wayar ta kunnu ta shiga cikin wajan kira sai taga anbuga mata waya a adadi, kuma duka miskul ne, kiran Ammy ya fi sau goma, haka ma na Falmat da sauran yan ajin su. Sakon waya kuwa su ma ga su nan birjik.
Jin wayar na kugin neman chaji ne ya sa Zainab dena duba kira da sakonnin da aka tura mata, ta shiga kokarin kiran Ammy kafin wayar ta mutu, Nan ma wani tashin hankali ne ya ziyarci idanun ta, domin kuwa wayar nunawa ta yi ba za ta iya kiran kowa ba sanadiyar rashin sabis, haka kuma wajan da ke nuna alamar sabis a wayar ma ya dauke gaba daya, a sannan Zainab ta dada jaddada kalmar 'babu sarki sai Allah'
Zufa na ketowa daga goshin ta rufe akwatin, hannun ta ruke da wayar ta tashi tsaye ta na dingisawa ta sanya silfas din da ke aje kusa da akwatin na ta, ta ja akwatin yayinda ta bude assabari ta fito waje, cak ta tsaya ganin yanda yaran nan da iyayan su duka su ka baro abin da su ke, su ka yi da'ira bakin kofar bukkar Shehu kamar masu jiran tsammani.
Babban abin da ya kara tsorata Zainab shi ne yanda su ka karu dan kuwa har na gona sai da yaran nan su ka je su ka kira su zo su ka ga Kado a dakin Shehu. Zainab na mai ja da baya cikin dakiya da rashin nuna tsoro ta ce
"Ban san ko su waye ba! Ban san wata duniya na ke ba! Ban kuma damu da na sani ba! Roko na daya dan Allah....ku nuna min hanyar da zan koma tawa duniyar! Kada ku cutar da ni....."