Sashe 18
Auren Shehu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Haka na ji ana ce masa a turance, Allah ya sa dai ba zagin mu ku ke ba"
Zainab na mai murmusawa yayinda ta rufe kwaryar furar ta na kokarin aje ludayi Usman ya karbe, ya ja kwaryar gaban sa, maimakon ya dau nasa ludayin, sai ya ki da na ta ludayin ya fara sha yana mai sai ta daidai in da Zainab ta sanya na ta bakin, ita kanta Zainab ta lura da hakan dan kuwa ta ji wani irin yar har tafin kafar ta. Shiru ne ya biyu baya kafin daga bisani Usman ya ce
"Abu ina neman alfarma, me zai hana ki na dan koyar da yaran Rugar nan boko...."
"Gidan fa? Na ce da kai ka mayar da ni gida!"
Zainab ta katse shi cikin bamnami. Kai ya girgiza mata alamar "ah ah" ba tare da ya tanka ba. Tashi ta yi za ta fita har ta kai kofa sai ta sake dawowa ta ce da shi
"Dajin nan ba su iya hausa ba kuma ba sa ji, ni kuma ba na jin fulatanci, ban iya ba, ta yaya ka ke so na koyar da su?"
Jin haka Usman har da kwarewa, ta na kallan sa ya karaci tarin sa babu ko sannu, bayan da ya gama ya dago ya na duban it bakin sa kunshe da dariyar mugunta ya ce
"Kar ki damu ai da na ce mu su da ga yau kun iya hausa kawai za ki ji sun yi"
Yanda ta yi da fuska ta na kallan sa ya sa shi kasa daurewa sai gashi na ya na dariya sosai, hakan ne ya kara tunzura ta ta furta
"Na dade ban ga azzalumi irin ka ba Usman!"
Ta fice cike da fushi, Usman kuwa be dena kyakyacewa ba.
Sai da Zainab ta kwana uku ta na jinya sama sama sannan ta sami sauki. Wata ranar lahadi da safe, Usman na shirin tafiya fadar Shehu Zainab ta ce da shi ta amince za ta koyar da yaran Rugar sa. Jim yayi ya na mamakin amincewar ta dan kuwa sam be yi zato ba. Cike da mamakin yanda Zainab ta ke canza masa ya ce da ita ta bari idan ya dawo za su yi maganar.
Ko da ya dawo ya kara tambayar ta, ta jaddada masa eh da gaske ta ke Usman yayi murna kwarai. Sai dai duk yanda ya ke jin dadin zaman gidan gonar daga shi sai Zainab dole ya mayar da ita cikin alhalin sa. Cikin lallami ya sheda mata, nan ma mamaki ta ba sa dan kuwa nuna masa ta yi ta na maraba da hakan dama ta gaji da zaman kadaici duk sanda ya fita hakan nan ta ke zama daga ita sai shanu da tsintsaye.
Usman be mayar da Zainab ba sai da ya tabbatar ya gina mata bandakin kara na ta ita kadai, duk da dai shi ma din ba masai gare shi ba sai dai duk sanda tutu ya matso ta shi da kan sa ya ke raka ta daji. Ba Usman ba hatta su Iyalle sun yi mamakin sauyin da su ka gani tattare da Zainab, haka kuma Usman ya ba da umarnin a ringa yiwa Zainab hausa hakan ya ba ta damar koyawa yara har da yan mata karatu, matasa maza ne dai Usman ya hana saboda kishin kar su na kalle masa Zainab. Duk sanda wani daga cikin yan rugar ta yiwa Zainab hausa sai ran ta ya sosa, wato da gaske dai sun iya hausan, kawai mugunta ya sa da ba sa kula ta. Ta sha alwashin sakawa Usman da daidai yanda ya mata ta hanyar da be taba tsammani ba.
Inda kowa ke nan nan da Zainab, Raqeeba da Rahila kuwa bakin ciki ne ya maye zuciyar su, musammam Rahila wacce ta riga ta yiwa mijin ta Tanko alkawarin kawo karshen Usman ta hanyar Zainab, da kuma samin damar cafkar ita kan ta Zainab hankali kwance, gashi duk yanda ta so ta dan kyebe da Zainab ko ta dan zuge ta abin ya gagara.
Babban tashin hankalin ta shi ne yanda Usman ke nan nan da Zainab, babu wanda be lura da yanda ya canza ba, walwalar shi ta karu, haka ma yawan zaman shi cikin gidan. So tari sai ya faki lokacin da Zainab za ta koyawa yara karatu sai ya kirkiri wani aikin da zai iya zama tsakar gidan yanda shi ma zai samu ya dan tsinci darasin, ya na so ya ce ta na koyar da shi amma ya na tsoran harshen Zainab.
Haka rayuwa ta cigaba har tsayin sati biyu, Rugar Shehu kaf maganar Zainab ne a bakin su domin kuwa jan su jikin ta ta ke sosai, haka ya sa Usman fara sakin jiki da ita, duk dai har lokacin ta ki yarda ya fara biyan bashin sadakin ta, duk sanda ya zo da batun ta tashi su yi karatu ya fara sauke nauyi sai ta ce bacci ta ke ji.
Misalin shadaya da rabi na dare Usman na zaune bakin kofar bukkar sa, tunanin duniya da yanda zai yi da Zainab ne ya addabi zuciyar sa, haka kawai ya ji zuciyar sa na kwadaita masa san ganin ta. Tun yana iya jurewa ya kasawa yayi, cikin himma ya tashi ya shige bukkar.
Bisa gadon kara ya tadda ta kwance ta yi daidai ta na bacci, da ke garin akwai hasken wata be damu da ya kunna fitilar acibalbal ba. Sanye ta ke cikin kayan saki, ta dunkule jikin ta kamar mai jin sanyi hakan ya Usman dauko daya daga cikin haramin sa mai kauri ya rufe ta da shi, tare da mata addua ya tofa hannun sa sannan ya bi jikin ta ya shafe, ga mamakin sa sai ji yayi ta furta
"Usman"
"Abu"
Ya amsa ya na mai kokarin kallan fuskar ta dan a tunanin sa tashi ta yi. Ganin idanun ta rufe ya san bacci ta ke yi, cikin mafarki ta ke kiran sunan sa. Ya na mai shafa fuskar ta ya yunkura zai tashi Zainab ta ruko hannun sa, cikin magagin bacci ta ce
"Kar ka tafi, ka kwanta mu yi bacci"
Toh dama abin nema ne ya samu, ba musu Usman ya shimfide kusa da Zainab, yayinda ta yi saurin dora kan ta jikin sa ta na mai sakin ajiyar zuciya. Dama mafarki ta ke da Usman tun kafin ya shigo dan haka ba ta yi yunkurun hana shi aika mata sakonnin da ya fara da hannun sa ba, sai ma taya shi da ta yi ta hanyar masa sabon abun da sai da ya je birni ya taba gani turawa na yi a talabijin, wato "kiss" a baki, a hankali shi ma ya shiga mayar mata da martani. Can dai abu ya wuce gona da iri Zainab ta bude idanu, ta ga a zahiri Usman din ne ba wai mafarki ta ke ba, ta fara kokarin ture shi Usman na mai girgiza mata kai ya ce
"Kar ki hana mu abin da Allah ya halatta mana Abu, ni halak din ki ne ba a mafarki ba kadai, har a zahiri, ki bari na ba ki hakkin ki.."
Ta bude baki ta niyar magana yayi saurin katse ta ta hanyar rufe bakin ta da nashi. Ganin Zainab ta saki jiki har da ba da na ta gudunmawar na ja mu su assabari na yi gaba abu na, dan da alama yau soyayya za a sha.
Da sanyin asuba Usman ya sa Iyalle dora ruwan zafi. Cikin al'ajabin rashin kunyar da su ke gani kala kala Kado ta sanya Usman ya zama mara kunyar kamar ba bafulatanin usul ba ta dafa masa ruwan zafi, ita ta kaiwa Zainab har saban bandakin kara da Usman ya sa aka yi mata.
Tunda ta bude ido abubuwan da su ka faru tsakanin ta da Usman ya fara dawo mata cikin ran ta, ta tsani kan ta, duk yanda zuciyar ta ta kauracewa gangan jikin ta, sai da gangan jikin ta ya fi karfin zuciyar ta har ta kai ga sakarwa Usman jikin ta dan abin kunya. Allah ya so ta dama ba ya dawowa daga masallaci har sai gari ya waye sosai, kuma ko ya dawo din ma ba ya shiga bukkar ta, dan haka ta na idar da sallah ta yi kokarin komawa bacci, amma fargabar halin da tsinci kan ta ciki ya sa ta kasa komawa bacci.
Gari ya waye tangararan Zainab ba ta ko rintsa ba, ta na shirin tashi ta fara shiri kafin yan karatu su fara zuwa kamar daga sama ta juyo muryar Usman a tsakar gida ya na amsa gaisuwa, kafin ta ankara sai gashi ya shigo bukkar. Gaban ta yayi mummunar faduwa yayinda bugun zuciyar ta ya karu sa'ad da su ka hada idanu, ta yi saurin kawar da kanta, yin hakan ne ya sanya Usman tunanin kunyar sa ta ke ji, kenan Zainab ta na san sa tunda har ta kai ba iya hada idanu da shi. Ciki da jin dadi ya janyo ta jikin sa, hannun sa hagu sa zagaye da kugun ta ya furta
"Ina kwana Gimbiya Abu? Kunya ta ake ji haka?"
Cikin kokarin boye tasirin da ya ke da shi akan ta, ta furta
"Dallah Malam ka sake ni! Me zai sa na ji kunyar ka!"
Dariya Usman ya sa dan kuwa yau Abu ta na masa tsiwa amma ta kasa daga idanu ta kalle shi, hannu ya sa ya dago habar ta yanda zai iya sanya idanun sa cikin na ta, kamar mai rada ya ce
"Ki kalle ni toh, ki kalli idanu na ki min magana Abu...."
Maimakon ta kalle shi, ta tsinci kan ta tana mai lumshe idanun ta, hakan ya bawa Usman bin kyakkywar fuskar ta da kallo, yayinda ya tsaya daidai lips din ta. Murya kasa kasa ya furta
"A daren jiya kin koyar da ni wani abu da ban taba tunanin zan yiwa wata ba Abu, ina alfahari kan ki na koya, ina alfahari ke na fara yiwa...."
Zainab na mai murmusawa yayinda ta rufe kwaryar furar ta na kokarin aje ludayi Usman ya karbe, ya ja kwaryar gaban sa, maimakon ya dau nasa ludayin, sai ya ki da na ta ludayin ya fara sha yana mai sai ta daidai in da Zainab ta sanya na ta bakin, ita kanta Zainab ta lura da hakan dan kuwa ta ji wani irin yar har tafin kafar ta. Shiru ne ya biyu baya kafin daga bisani Usman ya ce
"Abu ina neman alfarma, me zai hana ki na dan koyar da yaran Rugar nan boko...."
"Gidan fa? Na ce da kai ka mayar da ni gida!"
Zainab ta katse shi cikin bamnami. Kai ya girgiza mata alamar "ah ah" ba tare da ya tanka ba. Tashi ta yi za ta fita har ta kai kofa sai ta sake dawowa ta ce da shi
"Dajin nan ba su iya hausa ba kuma ba sa ji, ni kuma ba na jin fulatanci, ban iya ba, ta yaya ka ke so na koyar da su?"
Jin haka Usman har da kwarewa, ta na kallan sa ya karaci tarin sa babu ko sannu, bayan da ya gama ya dago ya na duban it bakin sa kunshe da dariyar mugunta ya ce
"Kar ki damu ai da na ce mu su da ga yau kun iya hausa kawai za ki ji sun yi"
Yanda ta yi da fuska ta na kallan sa ya sa shi kasa daurewa sai gashi na ya na dariya sosai, hakan ne ya kara tunzura ta ta furta
"Na dade ban ga azzalumi irin ka ba Usman!"
Ta fice cike da fushi, Usman kuwa be dena kyakyacewa ba.
Sai da Zainab ta kwana uku ta na jinya sama sama sannan ta sami sauki. Wata ranar lahadi da safe, Usman na shirin tafiya fadar Shehu Zainab ta ce da shi ta amince za ta koyar da yaran Rugar sa. Jim yayi ya na mamakin amincewar ta dan kuwa sam be yi zato ba. Cike da mamakin yanda Zainab ta ke canza masa ya ce da ita ta bari idan ya dawo za su yi maganar.
Ko da ya dawo ya kara tambayar ta, ta jaddada masa eh da gaske ta ke Usman yayi murna kwarai. Sai dai duk yanda ya ke jin dadin zaman gidan gonar daga shi sai Zainab dole ya mayar da ita cikin alhalin sa. Cikin lallami ya sheda mata, nan ma mamaki ta ba sa dan kuwa nuna masa ta yi ta na maraba da hakan dama ta gaji da zaman kadaici duk sanda ya fita hakan nan ta ke zama daga ita sai shanu da tsintsaye.
Usman be mayar da Zainab ba sai da ya tabbatar ya gina mata bandakin kara na ta ita kadai, duk da dai shi ma din ba masai gare shi ba sai dai duk sanda tutu ya matso ta shi da kan sa ya ke raka ta daji. Ba Usman ba hatta su Iyalle sun yi mamakin sauyin da su ka gani tattare da Zainab, haka kuma Usman ya ba da umarnin a ringa yiwa Zainab hausa hakan ya ba ta damar koyawa yara har da yan mata karatu, matasa maza ne dai Usman ya hana saboda kishin kar su na kalle masa Zainab. Duk sanda wani daga cikin yan rugar ta yiwa Zainab hausa sai ran ta ya sosa, wato da gaske dai sun iya hausan, kawai mugunta ya sa da ba sa kula ta. Ta sha alwashin sakawa Usman da daidai yanda ya mata ta hanyar da be taba tsammani ba.
Inda kowa ke nan nan da Zainab, Raqeeba da Rahila kuwa bakin ciki ne ya maye zuciyar su, musammam Rahila wacce ta riga ta yiwa mijin ta Tanko alkawarin kawo karshen Usman ta hanyar Zainab, da kuma samin damar cafkar ita kan ta Zainab hankali kwance, gashi duk yanda ta so ta dan kyebe da Zainab ko ta dan zuge ta abin ya gagara.
Babban tashin hankalin ta shi ne yanda Usman ke nan nan da Zainab, babu wanda be lura da yanda ya canza ba, walwalar shi ta karu, haka ma yawan zaman shi cikin gidan. So tari sai ya faki lokacin da Zainab za ta koyawa yara karatu sai ya kirkiri wani aikin da zai iya zama tsakar gidan yanda shi ma zai samu ya dan tsinci darasin, ya na so ya ce ta na koyar da shi amma ya na tsoran harshen Zainab.
Haka rayuwa ta cigaba har tsayin sati biyu, Rugar Shehu kaf maganar Zainab ne a bakin su domin kuwa jan su jikin ta ta ke sosai, haka ya sa Usman fara sakin jiki da ita, duk dai har lokacin ta ki yarda ya fara biyan bashin sadakin ta, duk sanda ya zo da batun ta tashi su yi karatu ya fara sauke nauyi sai ta ce bacci ta ke ji.
Misalin shadaya da rabi na dare Usman na zaune bakin kofar bukkar sa, tunanin duniya da yanda zai yi da Zainab ne ya addabi zuciyar sa, haka kawai ya ji zuciyar sa na kwadaita masa san ganin ta. Tun yana iya jurewa ya kasawa yayi, cikin himma ya tashi ya shige bukkar.
Bisa gadon kara ya tadda ta kwance ta yi daidai ta na bacci, da ke garin akwai hasken wata be damu da ya kunna fitilar acibalbal ba. Sanye ta ke cikin kayan saki, ta dunkule jikin ta kamar mai jin sanyi hakan ya Usman dauko daya daga cikin haramin sa mai kauri ya rufe ta da shi, tare da mata addua ya tofa hannun sa sannan ya bi jikin ta ya shafe, ga mamakin sa sai ji yayi ta furta
"Usman"
"Abu"
Ya amsa ya na mai kokarin kallan fuskar ta dan a tunanin sa tashi ta yi. Ganin idanun ta rufe ya san bacci ta ke yi, cikin mafarki ta ke kiran sunan sa. Ya na mai shafa fuskar ta ya yunkura zai tashi Zainab ta ruko hannun sa, cikin magagin bacci ta ce
"Kar ka tafi, ka kwanta mu yi bacci"
Toh dama abin nema ne ya samu, ba musu Usman ya shimfide kusa da Zainab, yayinda ta yi saurin dora kan ta jikin sa ta na mai sakin ajiyar zuciya. Dama mafarki ta ke da Usman tun kafin ya shigo dan haka ba ta yi yunkurun hana shi aika mata sakonnin da ya fara da hannun sa ba, sai ma taya shi da ta yi ta hanyar masa sabon abun da sai da ya je birni ya taba gani turawa na yi a talabijin, wato "kiss" a baki, a hankali shi ma ya shiga mayar mata da martani. Can dai abu ya wuce gona da iri Zainab ta bude idanu, ta ga a zahiri Usman din ne ba wai mafarki ta ke ba, ta fara kokarin ture shi Usman na mai girgiza mata kai ya ce
"Kar ki hana mu abin da Allah ya halatta mana Abu, ni halak din ki ne ba a mafarki ba kadai, har a zahiri, ki bari na ba ki hakkin ki.."
Ta bude baki ta niyar magana yayi saurin katse ta ta hanyar rufe bakin ta da nashi. Ganin Zainab ta saki jiki har da ba da na ta gudunmawar na ja mu su assabari na yi gaba abu na, dan da alama yau soyayya za a sha.
Da sanyin asuba Usman ya sa Iyalle dora ruwan zafi. Cikin al'ajabin rashin kunyar da su ke gani kala kala Kado ta sanya Usman ya zama mara kunyar kamar ba bafulatanin usul ba ta dafa masa ruwan zafi, ita ta kaiwa Zainab har saban bandakin kara da Usman ya sa aka yi mata.
Tunda ta bude ido abubuwan da su ka faru tsakanin ta da Usman ya fara dawo mata cikin ran ta, ta tsani kan ta, duk yanda zuciyar ta ta kauracewa gangan jikin ta, sai da gangan jikin ta ya fi karfin zuciyar ta har ta kai ga sakarwa Usman jikin ta dan abin kunya. Allah ya so ta dama ba ya dawowa daga masallaci har sai gari ya waye sosai, kuma ko ya dawo din ma ba ya shiga bukkar ta, dan haka ta na idar da sallah ta yi kokarin komawa bacci, amma fargabar halin da tsinci kan ta ciki ya sa ta kasa komawa bacci.
Gari ya waye tangararan Zainab ba ta ko rintsa ba, ta na shirin tashi ta fara shiri kafin yan karatu su fara zuwa kamar daga sama ta juyo muryar Usman a tsakar gida ya na amsa gaisuwa, kafin ta ankara sai gashi ya shigo bukkar. Gaban ta yayi mummunar faduwa yayinda bugun zuciyar ta ya karu sa'ad da su ka hada idanu, ta yi saurin kawar da kanta, yin hakan ne ya sanya Usman tunanin kunyar sa ta ke ji, kenan Zainab ta na san sa tunda har ta kai ba iya hada idanu da shi. Ciki da jin dadi ya janyo ta jikin sa, hannun sa hagu sa zagaye da kugun ta ya furta
"Ina kwana Gimbiya Abu? Kunya ta ake ji haka?"
Cikin kokarin boye tasirin da ya ke da shi akan ta, ta furta
"Dallah Malam ka sake ni! Me zai sa na ji kunyar ka!"
Dariya Usman ya sa dan kuwa yau Abu ta na masa tsiwa amma ta kasa daga idanu ta kalle shi, hannu ya sa ya dago habar ta yanda zai iya sanya idanun sa cikin na ta, kamar mai rada ya ce
"Ki kalle ni toh, ki kalli idanu na ki min magana Abu...."
Maimakon ta kalle shi, ta tsinci kan ta tana mai lumshe idanun ta, hakan ya bawa Usman bin kyakkywar fuskar ta da kallo, yayinda ya tsaya daidai lips din ta. Murya kasa kasa ya furta
"A daren jiya kin koyar da ni wani abu da ban taba tunanin zan yiwa wata ba Abu, ina alfahari kan ki na koya, ina alfahari ke na fara yiwa...."