Sashe 30
Auren Shehu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Hakkun ka yi gaskiya, Amma kuma wannan karan za ka kara da zamani, idan mu ka gama da asibitin nan za mu biya shopping mall mu siyo su brush da abin goge bakin ka ga sai ka kara wasai ko?"
Darawa Usman yayi, kafin ya kara magana Umar ya kara da
"Ka bari fa Usmanu, yanda ka zama gaye din nan sai fa mun yi da gaske, dan wallahi ba ka bina bashin rantsuwa matan da za su fara binka sai Allah, musammam ga ka da dukiya, fata na dai kada ka yi zaben tumun dare, na kuma san kai mai sani ne, ka ji tsoran Allah ka kuma roki Allah ya kare ka daga kaidin shedanun mata, ya kuma ba ka mace ta gari....."
"Amen summa amen"
Cewar Usman, cikin ran sa kuwa Zainab ya ke hangowa. Tunanin ko ta cigaba da rayuwar ta yanda ta ke a da ya ratsa zuciyar sa, be san sanda ya furta
"Innalillahi wainnailaihi rajiun! Allahumma ajirni fi masibati haza wakallifni khairan minha!"
A tsorace Umar ke kallan sa ya na tambayar lafiya? Me ya faru. Shi kuwa Usman bakin kishi ne da ya taso ma sa ya turnuke kirjin sa ya sanya shi salati. Amsawa Umar yayi da babu komai, kawai ya tuna wani abu ne. Yayi saurin barin wajen gudun kar Umar ya gane halin da ya ke ciki, dan kuwa sirri irin na Usman ya sa har yanzu be taba bawa Umar labarin Zainab ba.
*****
Sanda cikin Zainab ya cika wata tara chif, ya rage saura sati biyu EDD din ta ya cika Halitta ta dawo Nigeria. Ganin yanda Zainab ta bude ta zama katuwa zama da kyar ta shi da kyar Halitta ta sako ta a gaba da tsokana, duk dai ita ma din dauke ta ke da na ta yaron cikin wata uku cif.
Wata ranar lahadi da yamma likis, Zainab da Halitta sun dawo daga strolling, Halitta ke raka ta kusan kullum safe da yamma. Su ka tadda Anty Sauda zaune gaban Ammy ta hada kai da gwiwa ta na ta sharbar kuka. Hankalin su ba karamin tashi yayi ba dan kuwa a tunanin su ko General ne ya mutu. Muryar Halitta na rawa ta furta
"Anty Sauda lafiya? Ammy lafiya? Wani abu ya sami Genaral ne?"
"Ba gwara wani abu ya same shi ba da cin fuskar da ya min! Ni General zai ci Amana?"
Jin haka Zainab ta samu waje ta zauna cike da mamaki, shin dama akwai ranar da Anty Sauda za ta kuka da General? Mutumin da ta ke ikirarin ta gama da shi ko tsinke ta aje be isa ya tsallake ba sai da izinin ta. Zainab ba ta yi mutuwar zaune ba sai da ta ji Anty Sauda ta furta
"Wai Genaral ya rasa wacce zai auro min sai yar aiki! Da ilimi na! Da wayewa ta! Da arziki na amma ya auri yar aiki na? Wata jaka yar kauyen kayayau! Har ya na ikirarin matukar ba zan iya zama ba toh kofa bude ta ke!"
Jikin Halitta yayi sanyi kwarai, haka ma Falmat wacce shigowar ta kenan ita ma ta tsinci maganar. Ammy kuwa ta dade da kasa magana tsabagen al'ajabi. Zainab ce kadai ta furta
"Tooooh yar kauye fa Anty Sauda? Ki na nufin yar kauye dai kamar miji na Shehu?"
Ta yi maganar da manufa biyu wanda in aka dauki Anty Sauda babu wanda be fahimci in da Zainab ta dosa ba, Anty Sauda ta furta
"Irin su fa tsinannun tsintattun mage! Kuma ita ma din bafulatana ce waya sani ma ko Rugar su daya shi ne ya min shune tsinannun! Sai na yi maganin su! Wallahi bokan ta ya mata karya yanda na sha wahalar mallakar Malam sai ba ta isa ta zo da ruguje min ba! Yarinya ce fa kankanuwa! Ga ta bagidajiya! Kin san mazan nan daga na barta ta na masa girki saboda business ya dan fara hawa kai na, shi ne ta yi amfani da damar ta ta masa barbade...."
"Assha kin ga inda kuskuren na ki ya ke Anty Sauda, wayewa da ganin ke kin isa ya sanya ki ka bari wacce ki ke tunanin bagidajiya ce kuma yar kauye ta aure mutum mai daraja kamar General! Kenan akwai lokacin da wayewar ba ta amfani...!"
"Yakura!!!"
Ammy ta dakawa Zainab tsawa, in da Anty Sauda ta saki baki ta na duban ta. Zainab ta dubi Ammy ta furta
"Ammy kar ki hana ni magana! Ranar wanka ba a boye cibi! Ina ga nan Anty Sauda ta zauna ta gama kare min tatas! Har fadi ta ke ilimi na da jami'a ta be amfana min komai ba na rasa wanda zan so sai dan kauye! Da ke da na shiga jami'ar ko wayewar ita ce mizanin auna darajar dan adam ko azanci na dan adam! Ita ya aka yi ga shekarun, ga wayewar, ga arzikin ga ilimin amma ta yi sakaci irin wannan? Da wayewa, ilimin boko ko shiga jami'a shi ne mizani azancin dan Adam da wayyayu dayawa ba su halaka ba! Da yan kauye dayawa ba su cigaba ba! Wannan abun da ya faru da ke kukan kurciya ne Anty Sauda!"
Kuka Anty Sauda ta saka, fadi ta ke
"Ni Yakura? Ni ki ke gasawa maganganu haka? Na dade da sanin ba ki da kunya amma ban taba tunanin za ki iya shafawa idanun ki toka ki gasa min cin kashi haka ba!"
"Yakura ki bata hakuri! Ba ki kyauta ba!"
Cewar Ammy cikin tsawatarwa. Sai da ta yunkurin tashi da kyar, ta dubi Anty Sauda ta ce
"Allah ya ba ki hakuri tunda Ammy ta ce na baki hakuri, Amma sam ban yi dana sanin maganar da fada mi ki ba, rayuwa dai is a circle, na dade da gane haka ina kuma fatan ke ma za ki gane"
Ta wuce ciki ba tare da ta damu da kukan da Anty Sauda ta ke yi ba, bare fadan da Ammy ta bita da shi. Nan ta ke Anty Sauda ta ja jakar ta tace ta fasa zama gidan Ammy. Sai da su ka yi da gaske sannan ta hakura, ta ce amma Ammy ta mata tsakani da mara kunyar diyar ta. Ita kan ta Ammy mamakin yanda rayuwa ta juya ta ke, Halitta da Zainab wanda da ba sa ga maciji ne yau su ka zama tamkar aminan juna, Anty Sauda da Zainab wanda su ka saba kullawa su kunce babu wanda ya sani ne yau kuma ba sa ga maciji. Lalle kam rayuwa na da ban mamaki.
Tun kafin EDD din Zainab ya cika, ana sauran sati guda Zainab ta tashi da nakuda, wuni daya ta yi cur ta na yi sannan Allah ya sauke ta lafiya ta haifo dan ta namiji mai kama da Shehu sak tamkar yayi kaki ya tofar. Ita kan ta Zainab da aka daga mata shi sai da gaban ta ya fadi kasancewar shi jinjiri be sa ta kasa ganin Usman a fuskar sa da komai na sa ba.
Ko da aka miko sa hannun ta, ta na hawaye ta masa huduba ta saka masa suna Usman. Yanda ta ke yi ya sanya nurse din tambayar ta ko dai uban dan ya rasu ne? Zainab na duban Usman junior ta furta
"Eh ya rasu tun kafin na san ina dauke da cikin dan sa, Amma gashi Allah ya kara dawo min dashi, sai dai wannan karan jini na ne, tsatso na"
Cike da tausayawa nurse ta furta
"Allah sarki, Allah ya ji kan sa ya kuma raya dan sa"
Zainab ta amsa da "amen"
Babu wanda be yi murna da haihuwar Zainab ba, hatta Anty Sauda sai da ta aje fushin ta gefe da ta ga dan da Zainab ta haifa. yaro sak uban sa, kai ka ce balarabiya ta haifo sa. Jin Zainab ta saka sunan Usman ba Malam da kowa yayi zato ba sai da aka yi dan kananan maganganu. Zainab kuwa ta ce da dai ita ta haifo kayan ta, kuma Usman ta ga daman saka masa, za kuma ta kira shi Shehu, ta ga wanda ya ke da ikon canzawa dan ta suna.
Ranar suna aka sha shagali, Hajja Kilishi da na ta ayarin sun yiwa Ammy kara kwarai dan kuwa sai bayan suna da kwana biyu su ka tafi.
****
Bangaran Usman kuwa ya na can ya na hidamar kafa Rugar Shehu cikin saban gidan gonar da ya ke ginawa sam be san an masa takwara ba. Umar ya mayar da shi dan zamani, dake dama mutum ne mai ilimin addini gashi ya hada da zamananci nan da nan ya zama goge. Kullum cikin masa tayin aure ake, abokan sana'ar su ne, mata masu kawo kan su kai har ma daga bangaran Alhaji Ibrahim Balla, Amma kullum Usman cikin zillewa ya ke. Har Umar ya gaji ya fito ya tambayi Usman shin lafiyar sa kalau kuwa? Usman ya bashi amsa da kada ya damu, dake su na shirin zuwa Rugar Shehu domin taho da wasu daga cikin shanun Usman, ya ce ya bari idan su ka dawo zai masa bayanin komai. Da haka su ka dauki hanyar su na Rugar Shehu.
Amma ko da su ka isa Mambila, aka yiwa Umar bayanin tafiyar kasa da za su yi kafin su karasa Rugar Shehu nan yayi kememe ya ce ba shi iyawa. Usman dai ya je ya dawo shi zai yi tsimayin shi nan Mambila. Hakan ko aka yi, Usman shi kadai ya niki hanya har Rugar Shehu.
Ganin yanda Usman ya canza kasa gasgata zatan su na Shehun na su ne da gaske. Nan fa Usman ya zama abin kallo kamar yanda Zainab ta zama farkon zuwan ta Rugar Shehu, bambamcin dai shi wannan mamakin yanda Usman ya canza gaba daya ne ya rufe su. Kowa burin sa ya taba Usman. Shaddar da ke sanye jikin sa, hular kan sa kai hatta takalmin kafarsa abin kallo ne gare su. Cikin su har da masu fadin babu shakka cikin wannan injin kyera mutane da aka ce akwai a birni aka sanya Usman, ya zama dan birni tamkar kado.
Darawa Usman yayi, kafin ya kara magana Umar ya kara da
"Ka bari fa Usmanu, yanda ka zama gaye din nan sai fa mun yi da gaske, dan wallahi ba ka bina bashin rantsuwa matan da za su fara binka sai Allah, musammam ga ka da dukiya, fata na dai kada ka yi zaben tumun dare, na kuma san kai mai sani ne, ka ji tsoran Allah ka kuma roki Allah ya kare ka daga kaidin shedanun mata, ya kuma ba ka mace ta gari....."
"Amen summa amen"
Cewar Usman, cikin ran sa kuwa Zainab ya ke hangowa. Tunanin ko ta cigaba da rayuwar ta yanda ta ke a da ya ratsa zuciyar sa, be san sanda ya furta
"Innalillahi wainnailaihi rajiun! Allahumma ajirni fi masibati haza wakallifni khairan minha!"
A tsorace Umar ke kallan sa ya na tambayar lafiya? Me ya faru. Shi kuwa Usman bakin kishi ne da ya taso ma sa ya turnuke kirjin sa ya sanya shi salati. Amsawa Umar yayi da babu komai, kawai ya tuna wani abu ne. Yayi saurin barin wajen gudun kar Umar ya gane halin da ya ke ciki, dan kuwa sirri irin na Usman ya sa har yanzu be taba bawa Umar labarin Zainab ba.
*****
Sanda cikin Zainab ya cika wata tara chif, ya rage saura sati biyu EDD din ta ya cika Halitta ta dawo Nigeria. Ganin yanda Zainab ta bude ta zama katuwa zama da kyar ta shi da kyar Halitta ta sako ta a gaba da tsokana, duk dai ita ma din dauke ta ke da na ta yaron cikin wata uku cif.
Wata ranar lahadi da yamma likis, Zainab da Halitta sun dawo daga strolling, Halitta ke raka ta kusan kullum safe da yamma. Su ka tadda Anty Sauda zaune gaban Ammy ta hada kai da gwiwa ta na ta sharbar kuka. Hankalin su ba karamin tashi yayi ba dan kuwa a tunanin su ko General ne ya mutu. Muryar Halitta na rawa ta furta
"Anty Sauda lafiya? Ammy lafiya? Wani abu ya sami Genaral ne?"
"Ba gwara wani abu ya same shi ba da cin fuskar da ya min! Ni General zai ci Amana?"
Jin haka Zainab ta samu waje ta zauna cike da mamaki, shin dama akwai ranar da Anty Sauda za ta kuka da General? Mutumin da ta ke ikirarin ta gama da shi ko tsinke ta aje be isa ya tsallake ba sai da izinin ta. Zainab ba ta yi mutuwar zaune ba sai da ta ji Anty Sauda ta furta
"Wai Genaral ya rasa wacce zai auro min sai yar aiki! Da ilimi na! Da wayewa ta! Da arziki na amma ya auri yar aiki na? Wata jaka yar kauyen kayayau! Har ya na ikirarin matukar ba zan iya zama ba toh kofa bude ta ke!"
Jikin Halitta yayi sanyi kwarai, haka ma Falmat wacce shigowar ta kenan ita ma ta tsinci maganar. Ammy kuwa ta dade da kasa magana tsabagen al'ajabi. Zainab ce kadai ta furta
"Tooooh yar kauye fa Anty Sauda? Ki na nufin yar kauye dai kamar miji na Shehu?"
Ta yi maganar da manufa biyu wanda in aka dauki Anty Sauda babu wanda be fahimci in da Zainab ta dosa ba, Anty Sauda ta furta
"Irin su fa tsinannun tsintattun mage! Kuma ita ma din bafulatana ce waya sani ma ko Rugar su daya shi ne ya min shune tsinannun! Sai na yi maganin su! Wallahi bokan ta ya mata karya yanda na sha wahalar mallakar Malam sai ba ta isa ta zo da ruguje min ba! Yarinya ce fa kankanuwa! Ga ta bagidajiya! Kin san mazan nan daga na barta ta na masa girki saboda business ya dan fara hawa kai na, shi ne ta yi amfani da damar ta ta masa barbade...."
"Assha kin ga inda kuskuren na ki ya ke Anty Sauda, wayewa da ganin ke kin isa ya sanya ki ka bari wacce ki ke tunanin bagidajiya ce kuma yar kauye ta aure mutum mai daraja kamar General! Kenan akwai lokacin da wayewar ba ta amfani...!"
"Yakura!!!"
Ammy ta dakawa Zainab tsawa, in da Anty Sauda ta saki baki ta na duban ta. Zainab ta dubi Ammy ta furta
"Ammy kar ki hana ni magana! Ranar wanka ba a boye cibi! Ina ga nan Anty Sauda ta zauna ta gama kare min tatas! Har fadi ta ke ilimi na da jami'a ta be amfana min komai ba na rasa wanda zan so sai dan kauye! Da ke da na shiga jami'ar ko wayewar ita ce mizanin auna darajar dan adam ko azanci na dan adam! Ita ya aka yi ga shekarun, ga wayewar, ga arzikin ga ilimin amma ta yi sakaci irin wannan? Da wayewa, ilimin boko ko shiga jami'a shi ne mizani azancin dan Adam da wayyayu dayawa ba su halaka ba! Da yan kauye dayawa ba su cigaba ba! Wannan abun da ya faru da ke kukan kurciya ne Anty Sauda!"
Kuka Anty Sauda ta saka, fadi ta ke
"Ni Yakura? Ni ki ke gasawa maganganu haka? Na dade da sanin ba ki da kunya amma ban taba tunanin za ki iya shafawa idanun ki toka ki gasa min cin kashi haka ba!"
"Yakura ki bata hakuri! Ba ki kyauta ba!"
Cewar Ammy cikin tsawatarwa. Sai da ta yunkurin tashi da kyar, ta dubi Anty Sauda ta ce
"Allah ya ba ki hakuri tunda Ammy ta ce na baki hakuri, Amma sam ban yi dana sanin maganar da fada mi ki ba, rayuwa dai is a circle, na dade da gane haka ina kuma fatan ke ma za ki gane"
Ta wuce ciki ba tare da ta damu da kukan da Anty Sauda ta ke yi ba, bare fadan da Ammy ta bita da shi. Nan ta ke Anty Sauda ta ja jakar ta tace ta fasa zama gidan Ammy. Sai da su ka yi da gaske sannan ta hakura, ta ce amma Ammy ta mata tsakani da mara kunyar diyar ta. Ita kan ta Ammy mamakin yanda rayuwa ta juya ta ke, Halitta da Zainab wanda da ba sa ga maciji ne yau su ka zama tamkar aminan juna, Anty Sauda da Zainab wanda su ka saba kullawa su kunce babu wanda ya sani ne yau kuma ba sa ga maciji. Lalle kam rayuwa na da ban mamaki.
Tun kafin EDD din Zainab ya cika, ana sauran sati guda Zainab ta tashi da nakuda, wuni daya ta yi cur ta na yi sannan Allah ya sauke ta lafiya ta haifo dan ta namiji mai kama da Shehu sak tamkar yayi kaki ya tofar. Ita kan ta Zainab da aka daga mata shi sai da gaban ta ya fadi kasancewar shi jinjiri be sa ta kasa ganin Usman a fuskar sa da komai na sa ba.
Ko da aka miko sa hannun ta, ta na hawaye ta masa huduba ta saka masa suna Usman. Yanda ta ke yi ya sanya nurse din tambayar ta ko dai uban dan ya rasu ne? Zainab na duban Usman junior ta furta
"Eh ya rasu tun kafin na san ina dauke da cikin dan sa, Amma gashi Allah ya kara dawo min dashi, sai dai wannan karan jini na ne, tsatso na"
Cike da tausayawa nurse ta furta
"Allah sarki, Allah ya ji kan sa ya kuma raya dan sa"
Zainab ta amsa da "amen"
Babu wanda be yi murna da haihuwar Zainab ba, hatta Anty Sauda sai da ta aje fushin ta gefe da ta ga dan da Zainab ta haifa. yaro sak uban sa, kai ka ce balarabiya ta haifo sa. Jin Zainab ta saka sunan Usman ba Malam da kowa yayi zato ba sai da aka yi dan kananan maganganu. Zainab kuwa ta ce da dai ita ta haifo kayan ta, kuma Usman ta ga daman saka masa, za kuma ta kira shi Shehu, ta ga wanda ya ke da ikon canzawa dan ta suna.
Ranar suna aka sha shagali, Hajja Kilishi da na ta ayarin sun yiwa Ammy kara kwarai dan kuwa sai bayan suna da kwana biyu su ka tafi.
****
Bangaran Usman kuwa ya na can ya na hidamar kafa Rugar Shehu cikin saban gidan gonar da ya ke ginawa sam be san an masa takwara ba. Umar ya mayar da shi dan zamani, dake dama mutum ne mai ilimin addini gashi ya hada da zamananci nan da nan ya zama goge. Kullum cikin masa tayin aure ake, abokan sana'ar su ne, mata masu kawo kan su kai har ma daga bangaran Alhaji Ibrahim Balla, Amma kullum Usman cikin zillewa ya ke. Har Umar ya gaji ya fito ya tambayi Usman shin lafiyar sa kalau kuwa? Usman ya bashi amsa da kada ya damu, dake su na shirin zuwa Rugar Shehu domin taho da wasu daga cikin shanun Usman, ya ce ya bari idan su ka dawo zai masa bayanin komai. Da haka su ka dauki hanyar su na Rugar Shehu.
Amma ko da su ka isa Mambila, aka yiwa Umar bayanin tafiyar kasa da za su yi kafin su karasa Rugar Shehu nan yayi kememe ya ce ba shi iyawa. Usman dai ya je ya dawo shi zai yi tsimayin shi nan Mambila. Hakan ko aka yi, Usman shi kadai ya niki hanya har Rugar Shehu.
Ganin yanda Usman ya canza kasa gasgata zatan su na Shehun na su ne da gaske. Nan fa Usman ya zama abin kallo kamar yanda Zainab ta zama farkon zuwan ta Rugar Shehu, bambamcin dai shi wannan mamakin yanda Usman ya canza gaba daya ne ya rufe su. Kowa burin sa ya taba Usman. Shaddar da ke sanye jikin sa, hular kan sa kai hatta takalmin kafarsa abin kallo ne gare su. Cikin su har da masu fadin babu shakka cikin wannan injin kyera mutane da aka ce akwai a birni aka sanya Usman, ya zama dan birni tamkar kado.