Sashe 19
Auren Shehu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya na gama fadin haka ya fara kissing din ta, yanda ya ke saban shiga kuma bagidaje be kasa ruda Zainab ba, dan kuwa ta sha kissing samarin ta wayayyu, Amma babu wanda ya tafi da ita har ta kai ga mance in da ta ke face Usman.
Saukar assabari da alamar mutum ne ya daga yayi saurin saki ne ya dawo da su hayyacin su, yayinda Zainab ta yi saurin matsawa daga jikin sa. Usman kuwa juyawa yayi ya fice da sauri kamar yana tsoran abin d zaman sa dakin zai iya haifarwa.
Hannayen ta biyu rufe da fuskar ta ta zauna bakin gado ta na fadin
"Innalillahi wainnailaihi rajiun! Me ke damu na ni Zainab! What I'm doing to myself! This is not what I've been planning!"
Sallamar da ta ji an yi ya sanya ta daga kai ta kalli wacce ta shigo dauke da kwaryar nono. Yanda ta yi sin da kai ta gaishe da Zainab ba tare da ta bari sun hada ido ba cikin ta ya bata itace ta shigo dazu ta gan ta tare da Usman. Bayan ta aje kwaryar ta na shirin juyawa Zainab ta ce
"Rahila ki shedawa mijin ki Tanko na shirya! Na shirya damka masa Usman da Rugar nan mukar zai fitar da ni daga wannan kangin rayuwar!"
Cike da mamaki Rahila ta juyo ta na kallan ta ta na mai fadin
"Da gaske ki ke? Dama ba ki hakura ba? Yanda ki ka saki jiki da jama'ar Rugar nan har ki na koyarwa, na ji labarin Usman ya kauda budurcin ki...."
Zainab ta dago a razane ta na duban Rahila, wacce ganin haka ta girgiza kai cikin jaddawa ta ce
"Kwarai kuwa nan ya zo ya na fadawa kowa cikin fariya. Kuma yanda Raqeeba ta dawo jiki na rawa bayan ta ga Shehu ya na....."
Nauyin maganar ya sa Rahila karasawa yayinda ta ke tuno fuskar Raqeeba sanda ta nufo ta jiki na rawa idanu na fito da kwalla ta ke fadin
"Rahila Kado ta maishe da Shehu dan iska! Wallahi ganin su na yi bakin shi cikin na ta kamar za su cinye juna...."
"Duka shiri na Rahila!"
Maganar Zainab ne ya dawo da Rahila daga kogin tunanin da ta ke shirin fadawa. Zainab ba ta gushe ba ta kara da
"Duka na yi ne domin Usman ya saki jiki da ni, Amma zancen budurci kwata yayi! Fyade ya min kuma ba zan taba yafe mi shi ba shi ya sa na yanke hukunci bullo masa ta wannan sigar, Rahila ki taimaka ki fadawa Tanko ni Zainab zan bashi gudunmawa dari bisa bisa dari domin kawo karshen wannan azzalumin!"
Dan farin ciki jikin Rahila har rawa ya ke yayinda ta yiwa Zainab sallama ta fita, dan kuwa Allah Allah ta ke ta kaiwa Tanko sakon Zainab, ashe dai yau Tanko zai yi alfahari da ita, haka kuma takusa zama matar Shehu, mijin ta Tanko zai haye kujerar Usman.
Zainab kuwa tun fitar Rahila ba ta motsa ba, babban fargaban ta shi ne yanda Usman ya fara tasiri akan ta, dan bayan fitar shi ta gane ba wai kawai gangan jikin ta kadai Usaman ya mallaka ba, ya na neman ya mallaki zuciyar ta wanda hakan ta ke gani ba za ta iya bari ya faru ba, nan kuwa ba ta san bakin alkalami ya riga ya bushe, tsanar da ta ke ikirarin ta yiwa Usman ne ya sa ta kasa fahimtar hakan.
AUREN SHEHU 2
11
Rahila ba ta iya jiran dare yayi ba ta yi amfani da damar annushuwar da Usman ya ke ciki ta tambaye shi ko ya na da labarin in da Tanko ya ke ba tare da ta nuna dama ta san in da ya ke ba bare ma a gano ta saba satar hanya.
Tausayin Rahila ne ya kama Usman musammam yanzu da ya san darajar soyayya, Dan haka ya ce da Muhammad Bello ya raka Rahila ta ga mijin ta, idan ma ta na so ta koma wajen shi ne gaba daya ta na iya komawa babu laifi in ya so duk sanda ta ke da bukatar shigowa Rugar Shehu neman abinci ko wata bukatar mai muhummanci kofa a bude ta ke gare ta. Ta na murna ta yi bankwana da jama'ar rugar, in da ta yiwa Zainab alkawari cewar tafiyar ta ba ya na nufin lalacewar maganar su bane, shi ne ma dalilin da ya sa za ta wajan Tanko, duk yanda su ka yi da Tanko za ta dawo ta fada mata, haka kuma za ta na kawo mata ziyara a kan kari.
Cike da farin ciki ta riski mijin ta Tanko wanda sam be nuna farin cikin sa na ganin Rahila dauke da kaya niki niki ba, a tunanin sa Usman ya karota ne, sai da ta masa bayani tare da albishir da ta zo masa da shi sannan ya dan saki ran sa.
Bayan Bello ya masa sallama ya juya ne Tanko ya kada baki ya ce
"Ban so dawowar ki waje na ba, kamata yayi ki zauna can in da za ki fi ganin duk abin da ya ke faruwa, yanzu da ki ka kwaso kafa ki ka dawo uwar me za ki min a nan?"
Cikin sosuwar rai Rahila ta furta
"Kai kuwa Tanko ai zato na farin ciki za ka yi da zuwa na, na ga kowani namiji burin shi ya kasance tare da iyali saboda jiki da jini...."
"Toh yar jaraba! Jaraba ce dai ta dawo da ke! Ke jikin ki ma duk ya sake amma ba za ki hakura ba?"
Jiki sanyeye Rahila ta furta
"Haba kai kuwa, ai sai ana son ka ake mararin ka.."
"Toh uwar jaraba wuce mu je na mi ki abin da ki ke so, Amma dai zaman ki a nan ba zai yiyu ba! Dole ki koma Rugar Shehu!"
Rahila ba ta yi zuciya ba ta bi bayan Tanko, sai da ya ba ta hakkin ta sannan ya shiga zayyana mata yanda za a yi su cafke daga Usman har Zainab, in da ya ce ta shedawa Zainab yanda ta yi yayi daidai, ta kara dagewa wajan samin yardar Usman, hakan ne kadai zai sa su iya cin nasara. Su ka yi sallama Tanko na farin cikin burin su ya kusa cika, dadin dadawa kuma ya kusa samun Zainab, wacce tun da ya gan ta be da mafarki sai na ta, duniyar nan kab be da buri da ya wuce samin Zainab ko da kuwa na wuni daya ne.
Babu wanda be yi mamakin dawowar Rahila ba, cike da bakin cikin Tanko ya hana ta zama da shi, ta mu su karyar ga mata yan uwan ta me zai sa ta je can gefe ta ware kan ta, zaman cikin Rugar Shehu shi ya fi mata alkhairi. Sai da ta faki idanun matan Rugar sannan ta iske Zainab a daki, ta kwashe yanda ta yi da Tanko na game da Usman ta sheda ma ta, tare da sakon Tanko gare ta, kana ta kara da
"Kin ga kenan yanda ki ka yi ba karamin dabara ba ne, yanzu ki dada jan shi jiki, ki sa ya yarda da ke sosai ya saki jiki da ke, kya iya nuna masa ma kin kamu da son shi....."
"Mtswww Allah ya sauwake na kamu da san wannan bagidaje!"
Zainab ta katse ta a fusace. Jin haka Rahila ta dada godewa Allah, kenan hasashen ta ba daidai ba ne, Zainab dai ba ta fadama san Usman ba, gudun kar daga baya ta ba su matsala.
****
Can birnin Kano kuwa anyi cigiya da shelar neman Zainab, haka kuma an bi sahunta har Mambila amma an kasa gano takamamman in da ta ke, musammam yanda Jama'ar garin su ka yi kyameme su ka nuna ba su taba ganin Usman ba bare Zainab, hatta dajin Rugar Shehu sun shiga, amma gajen hakuri ya sa su ka juyo saboda yanda dajin ke da ban so tsoro, gani su ke bil'adama ba zai iya rayuwa ciki ba.
Kudin da Ammy ta kashe na sadaka da sauka ba adadi, tun tana sa rai ta na yarda da maganar yaran General da Anty Sauda, har ta fara karaya, ta yanke hukunci ziyartar kasa mai girma dakin Allah ta yi addua, idan har. Zainab na raye Allah ya bayyana ta, idan kuma ta mutu Allah ya nuna mata kabarin ta ko ta sami kwanciyar hankali.
Da wannan niyya, da kuma burin ganin Halitta Ammy da Falmat su ka tashi zuwa kasa mai tsarki.
***
Cikin kankanin lokaci jama'ar Rugar Shehu su ka kamu da kaunar Kado kamar yanda su ke kiran zainab, daga manyan su har zuwa yara. Ya kasance ko magana ta yi ya zaunu ba a mata musu, haka ma ta shige cikin zuciyar Usman ta zauna daram, Dan kuwa shawarar Rahila ta dauka, jan shi ta ke a jiki ta na masa soyayya irin ta yan birni musammam Zainab ta gama gogewa a wannan fanni.
Wani sabon al'amari shi ne yanda Usman ya tashi tsaye kan Muhammad Bello, duk wata hidima da ilimin tafiya da Rugar Shehu kokari ya ke ya koyawa Bello, haka kuma ya sanya ranar auren Bello da Raqeeba wata daya kacal, Allah ya so dama Bello ya jima ya na muradin Raqeeba duk da ya fahimci ba shi ne gaban ta ba, shi din ne ya ke san maso wani sai kuma faduwa to zo daidai da zama.
In da Bello da jama'ar Rugar Shehu aka shiga shirye shiryen biki, Amarya Raqeeba a nata bangaran bakin ciki ne ya mamaye zuciyar ta, ta na ji ta na ana gani za a daura mata Bello bayan Usman ta ke so, Kuma mahaifiyar ta ta san da haka amma ta ce ko da wasa kar da ta sake wani mahaluki ya ji zancen nan in ba haka ba sai ta tsine mata.
Saukar assabari da alamar mutum ne ya daga yayi saurin saki ne ya dawo da su hayyacin su, yayinda Zainab ta yi saurin matsawa daga jikin sa. Usman kuwa juyawa yayi ya fice da sauri kamar yana tsoran abin d zaman sa dakin zai iya haifarwa.
Hannayen ta biyu rufe da fuskar ta ta zauna bakin gado ta na fadin
"Innalillahi wainnailaihi rajiun! Me ke damu na ni Zainab! What I'm doing to myself! This is not what I've been planning!"
Sallamar da ta ji an yi ya sanya ta daga kai ta kalli wacce ta shigo dauke da kwaryar nono. Yanda ta yi sin da kai ta gaishe da Zainab ba tare da ta bari sun hada ido ba cikin ta ya bata itace ta shigo dazu ta gan ta tare da Usman. Bayan ta aje kwaryar ta na shirin juyawa Zainab ta ce
"Rahila ki shedawa mijin ki Tanko na shirya! Na shirya damka masa Usman da Rugar nan mukar zai fitar da ni daga wannan kangin rayuwar!"
Cike da mamaki Rahila ta juyo ta na kallan ta ta na mai fadin
"Da gaske ki ke? Dama ba ki hakura ba? Yanda ki ka saki jiki da jama'ar Rugar nan har ki na koyarwa, na ji labarin Usman ya kauda budurcin ki...."
Zainab ta dago a razane ta na duban Rahila, wacce ganin haka ta girgiza kai cikin jaddawa ta ce
"Kwarai kuwa nan ya zo ya na fadawa kowa cikin fariya. Kuma yanda Raqeeba ta dawo jiki na rawa bayan ta ga Shehu ya na....."
Nauyin maganar ya sa Rahila karasawa yayinda ta ke tuno fuskar Raqeeba sanda ta nufo ta jiki na rawa idanu na fito da kwalla ta ke fadin
"Rahila Kado ta maishe da Shehu dan iska! Wallahi ganin su na yi bakin shi cikin na ta kamar za su cinye juna...."
"Duka shiri na Rahila!"
Maganar Zainab ne ya dawo da Rahila daga kogin tunanin da ta ke shirin fadawa. Zainab ba ta gushe ba ta kara da
"Duka na yi ne domin Usman ya saki jiki da ni, Amma zancen budurci kwata yayi! Fyade ya min kuma ba zan taba yafe mi shi ba shi ya sa na yanke hukunci bullo masa ta wannan sigar, Rahila ki taimaka ki fadawa Tanko ni Zainab zan bashi gudunmawa dari bisa bisa dari domin kawo karshen wannan azzalumin!"
Dan farin ciki jikin Rahila har rawa ya ke yayinda ta yiwa Zainab sallama ta fita, dan kuwa Allah Allah ta ke ta kaiwa Tanko sakon Zainab, ashe dai yau Tanko zai yi alfahari da ita, haka kuma takusa zama matar Shehu, mijin ta Tanko zai haye kujerar Usman.
Zainab kuwa tun fitar Rahila ba ta motsa ba, babban fargaban ta shi ne yanda Usman ya fara tasiri akan ta, dan bayan fitar shi ta gane ba wai kawai gangan jikin ta kadai Usaman ya mallaka ba, ya na neman ya mallaki zuciyar ta wanda hakan ta ke gani ba za ta iya bari ya faru ba, nan kuwa ba ta san bakin alkalami ya riga ya bushe, tsanar da ta ke ikirarin ta yiwa Usman ne ya sa ta kasa fahimtar hakan.
AUREN SHEHU 2
11
Rahila ba ta iya jiran dare yayi ba ta yi amfani da damar annushuwar da Usman ya ke ciki ta tambaye shi ko ya na da labarin in da Tanko ya ke ba tare da ta nuna dama ta san in da ya ke ba bare ma a gano ta saba satar hanya.
Tausayin Rahila ne ya kama Usman musammam yanzu da ya san darajar soyayya, Dan haka ya ce da Muhammad Bello ya raka Rahila ta ga mijin ta, idan ma ta na so ta koma wajen shi ne gaba daya ta na iya komawa babu laifi in ya so duk sanda ta ke da bukatar shigowa Rugar Shehu neman abinci ko wata bukatar mai muhummanci kofa a bude ta ke gare ta. Ta na murna ta yi bankwana da jama'ar rugar, in da ta yiwa Zainab alkawari cewar tafiyar ta ba ya na nufin lalacewar maganar su bane, shi ne ma dalilin da ya sa za ta wajan Tanko, duk yanda su ka yi da Tanko za ta dawo ta fada mata, haka kuma za ta na kawo mata ziyara a kan kari.
Cike da farin ciki ta riski mijin ta Tanko wanda sam be nuna farin cikin sa na ganin Rahila dauke da kaya niki niki ba, a tunanin sa Usman ya karota ne, sai da ta masa bayani tare da albishir da ta zo masa da shi sannan ya dan saki ran sa.
Bayan Bello ya masa sallama ya juya ne Tanko ya kada baki ya ce
"Ban so dawowar ki waje na ba, kamata yayi ki zauna can in da za ki fi ganin duk abin da ya ke faruwa, yanzu da ki ka kwaso kafa ki ka dawo uwar me za ki min a nan?"
Cikin sosuwar rai Rahila ta furta
"Kai kuwa Tanko ai zato na farin ciki za ka yi da zuwa na, na ga kowani namiji burin shi ya kasance tare da iyali saboda jiki da jini...."
"Toh yar jaraba! Jaraba ce dai ta dawo da ke! Ke jikin ki ma duk ya sake amma ba za ki hakura ba?"
Jiki sanyeye Rahila ta furta
"Haba kai kuwa, ai sai ana son ka ake mararin ka.."
"Toh uwar jaraba wuce mu je na mi ki abin da ki ke so, Amma dai zaman ki a nan ba zai yiyu ba! Dole ki koma Rugar Shehu!"
Rahila ba ta yi zuciya ba ta bi bayan Tanko, sai da ya ba ta hakkin ta sannan ya shiga zayyana mata yanda za a yi su cafke daga Usman har Zainab, in da ya ce ta shedawa Zainab yanda ta yi yayi daidai, ta kara dagewa wajan samin yardar Usman, hakan ne kadai zai sa su iya cin nasara. Su ka yi sallama Tanko na farin cikin burin su ya kusa cika, dadin dadawa kuma ya kusa samun Zainab, wacce tun da ya gan ta be da mafarki sai na ta, duniyar nan kab be da buri da ya wuce samin Zainab ko da kuwa na wuni daya ne.
Babu wanda be yi mamakin dawowar Rahila ba, cike da bakin cikin Tanko ya hana ta zama da shi, ta mu su karyar ga mata yan uwan ta me zai sa ta je can gefe ta ware kan ta, zaman cikin Rugar Shehu shi ya fi mata alkhairi. Sai da ta faki idanun matan Rugar sannan ta iske Zainab a daki, ta kwashe yanda ta yi da Tanko na game da Usman ta sheda ma ta, tare da sakon Tanko gare ta, kana ta kara da
"Kin ga kenan yanda ki ka yi ba karamin dabara ba ne, yanzu ki dada jan shi jiki, ki sa ya yarda da ke sosai ya saki jiki da ke, kya iya nuna masa ma kin kamu da son shi....."
"Mtswww Allah ya sauwake na kamu da san wannan bagidaje!"
Zainab ta katse ta a fusace. Jin haka Rahila ta dada godewa Allah, kenan hasashen ta ba daidai ba ne, Zainab dai ba ta fadama san Usman ba, gudun kar daga baya ta ba su matsala.
****
Can birnin Kano kuwa anyi cigiya da shelar neman Zainab, haka kuma an bi sahunta har Mambila amma an kasa gano takamamman in da ta ke, musammam yanda Jama'ar garin su ka yi kyameme su ka nuna ba su taba ganin Usman ba bare Zainab, hatta dajin Rugar Shehu sun shiga, amma gajen hakuri ya sa su ka juyo saboda yanda dajin ke da ban so tsoro, gani su ke bil'adama ba zai iya rayuwa ciki ba.
Kudin da Ammy ta kashe na sadaka da sauka ba adadi, tun tana sa rai ta na yarda da maganar yaran General da Anty Sauda, har ta fara karaya, ta yanke hukunci ziyartar kasa mai girma dakin Allah ta yi addua, idan har. Zainab na raye Allah ya bayyana ta, idan kuma ta mutu Allah ya nuna mata kabarin ta ko ta sami kwanciyar hankali.
Da wannan niyya, da kuma burin ganin Halitta Ammy da Falmat su ka tashi zuwa kasa mai tsarki.
***
Cikin kankanin lokaci jama'ar Rugar Shehu su ka kamu da kaunar Kado kamar yanda su ke kiran zainab, daga manyan su har zuwa yara. Ya kasance ko magana ta yi ya zaunu ba a mata musu, haka ma ta shige cikin zuciyar Usman ta zauna daram, Dan kuwa shawarar Rahila ta dauka, jan shi ta ke a jiki ta na masa soyayya irin ta yan birni musammam Zainab ta gama gogewa a wannan fanni.
Wani sabon al'amari shi ne yanda Usman ya tashi tsaye kan Muhammad Bello, duk wata hidima da ilimin tafiya da Rugar Shehu kokari ya ke ya koyawa Bello, haka kuma ya sanya ranar auren Bello da Raqeeba wata daya kacal, Allah ya so dama Bello ya jima ya na muradin Raqeeba duk da ya fahimci ba shi ne gaban ta ba, shi din ne ya ke san maso wani sai kuma faduwa to zo daidai da zama.
In da Bello da jama'ar Rugar Shehu aka shiga shirye shiryen biki, Amarya Raqeeba a nata bangaran bakin ciki ne ya mamaye zuciyar ta, ta na ji ta na ana gani za a daura mata Bello bayan Usman ta ke so, Kuma mahaifiyar ta ta san da haka amma ta ce ko da wasa kar da ta sake wani mahaluki ya ji zancen nan in ba haka ba sai ta tsine mata.