Sashe 18
Aisha Siddiqa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kafin Aishata bashi amsa Kiki ta fito ta sha gayunta kamar koyaushe, ta tadda su suna maganar tafiyar tasa. Ta ce,
“Uncle sai ka bamu kudi, kudi sosai fa, muna da activities masu yawa nida Pretty. Kama daga Shopping, zuwa su Hiking da Camel Riding. Tunda Aisha ta zo na tabbata ko sau daya ba ka fita da ita ta ga kasar nan ba”.
“Ke ba sai ki fito da itan ba, uwar ‘yan kankanba da kilbibi, baki kamar na Aku-kuturu, halan ba’a gasa bakinki yayin omogwu ba?”.
Kiki tasa dariya tace, “ka tambayi Maman Hakeem (Aunty Taiwo). Nidai kawai Uncle ka yi mana izini muna da wuraren zuwa mu mike kafa tunda baka nan”.
Katin cirar kudinshi na daya daga cikin bankunan da yake ajiya ya ciro ya mika ma Kiki, ya ce, su sayi ko me suke so har ya dawo.
Sannan zai bar masu mukullin mota daya Kiki ta kai su ‘tour round the city’.
“Banda kai wa dare Kiki, kin ji na gaya miki”.
Kiki ta amshi credit card din ta yi godiya, ta ce, “Insha Allahu Uncle ba za mu dinga yin dare ba”.
Aisha dai tana gefe tana jera abincin da ta gama bisa tebir ba ta saka musu baki ba.
Kiki ta ce, “Aisha ki yi mana godiya mana, an bamu dama mu je shopping, kuma in kai ki tour cikin gari”.
Dan murmushin gefen baki Aisha ta yi ta ce, “Kiki ni ba abinda zan saya, sannan kuma bana son yawo, gajiya zan yi”.
Kiki ta ce, “Ai da ma ban tambaye ki ko za ki sai wani abu ba, ni na san duk abin da ki ke bukata kuma ni zan dauko miki”.
Hamma bai saurare su ba, ya ja kujerar dining daya ya zauna, yau ma a tsakiya suka saka shi, Aisha na dama Kiki na hagu, suka soma cin abincin.
Bayan Kiki ta yi serving dinsu kamar jiya. Jefi-jefi Kiki da Uncle dinta na magana cikin yarbanci akan abin da ya shafe su.
Maganar Kiki kullum guda daya ce, ‘yasa baki Maman Hakeem ta yarda Tosin ya iso gida, tunda dai shi da take kafa hujja da shi din yanzu ya kama Dahir”.
Aisha ta kudire a ranta zata kara zagewa wajen koyon harshen yarbanci da gaske daga ranar yau, don ta lura Prince ba ya so ta ji ko me suke tattaunawa, shi ya sa ma ya koma magana cikin kasaitaccen yarbancinsa.
Kiki ta ce,
“Uncle AK da ban zo ba kenan haka za ka tafi ka bar Aisha a gidan nan ita kadai?”
Prince ya harare ta, ya ce,
“Kiki ke ce uban ne ko ni ne?”
Dariya ta yi, Aishama saida ta murmusa, ta ce, “Amma dai Uncle amarya ba’a barinta ita kadai a gida, son samu a ce tafiyar nan France tare ku ka yi ta, (as in honeymoon a tsakiyar birnin masoya irin Paris) koh?”.
Kunya ta nuna a fuskar Uban Kiki. Yayi maza yace “na gaya miki amma tournament za ni je ko? Kiki why are you disturbing me?”
Kiki ta bar zancen don bata son bata masa rai, ta ce,
“Shi ke nan Uncle, Allah ya kiyaye hanya. ‘yar ka zata kula maka da Aisharka har sai ka dawo!”.
Prince ya tashi da daddare, Kiki ta tsara musu duk abubuwan da za su gudanar yadda za su mori satin sosai, kafin ya dawo.
Tana so Aisha ta san gari, ta kuma daina bakunta da rashin sakewa a gidanta.
Washegari suka shirya ko break fast ba su yi a gida ba, suka tafi shopping. Kiki ita ce mai diban kaya Aisha mai tarawa. Kiki ta daukar wa Aisha lingeries, English wears da nighties kala-kala data lura bata dasu, ta ce,
“Daga yau bake ba kara saka atamfa a cikin gida, musamman in yana gidan, sai wadannan da na zabar miki in dai kinason zaman lafiya da ni”. Aisha tayi dariya tace “wasa kike yi Kiki, kema kinsan bazan iya ba”. Kiki tace “to ki ajiye ki boye, can gaba in kin yi kilin zasu yi miki amfani”.
Sosai Kiki ta bata dariya.
Suka koma bangaren kayan wanka ta daukar mata su feminine wash, deosprays da su body scrub, daga nan suka je ‘sight seeing’.
Ba su dawo gida ba sai yamma lis.
Haka washegari suka sake ficewa zuwa ganin Penguins, waterfalls da wajen Camel Riding.
Ana saura kwana uku Prince zai dawo kiki ta kai ta aka yi mata SPA da Moroccan Hammam (wajen gyaran jiki na mata na Moroccan Hammam).
Nan aka wanke Aisha tas, aka yi mata spa, body scrubing, pedicure da manicure, har da gyaran gashi, aka wanke gashin Aisha aka yi steaming dinsa, sai ga fatar Aisha har sheki ta ke yi abin gwanin ban sha’awa, dama ga ta fara tas, to sai ta koma pinkish, har wani jaja-jaja fatarta ke yi.
Kiki da aka kammala gyaran Aisha ta saita camera ta kashe ta da kyawawan hotuna, kuma bada saninta ba kawai Kiki ta tura su wayar Uncle dinta, ta (whatsapp application) dinshi.
Saura kwana biyu Prince ya dawo da yammaci suka ga wani guri ana YOGA. Don haka washegari tun da safe suka shirya suka tafi YOGA.
A can suka wuni sur! Aisha ta ji dadin session din nasu a can, waje ne na motsa jikin mata zallah, sai yamma lis suka dawo gida.
A YOGA ma sun yi hotuna masu kyau, kawai Kiki ta hau turawa babanta hotunan da suka dauka na charming lady dinsa AISHA-SIDDIQAH ba tare da Aisha ta sani ba.
**** **** ****
Prince yana reception na hotel din da ya sauka a kasar France yana hutawa kafin ya haura sama zuwa dakinsa, kawai sakon Kiki ya cimmasa.
Yana budewa kyakkyawar surar ta bayyana kamar da an tabata jini zai yi tsartuwa. Gabadaya fatar jikin Aisha ta canza daga yadda ya santa. ‘Moroccan Hammam’ din da ta sha da SPA sun karbeta, gashin kanta ya sha steaming da gyara na musamman ya kwanta a dokin wuyanta, gashi bakikkirin da shi, sai sheki yake yi.
Wani bala’in murmushi da ta sakarwa Kiki a hoton, sai daya kusa kashe idon Prince Abdulrasheed Kehinde.
Bai taba yi mata kallon da har zai ga natural features dinta a fili ba, sai yau a hoton nan.
He was dumb founded, domin bai taba ganin abu mai kyau irin Aisha-Siddiqah ba.
Ga naivity ga innocence appearance dinta wadanda sune attributes dinta da ya fi so. Prince jinsa ya yi duk ya zama wani upset, a karshe ya kasa zaman reception din domin ji yake tamkar bafaranshan da ke bayanshi yana taya shi kallon hotunan matar tasa, sai kawai ya rufe ya tashi ya bar reception din, ya bi lift zuwa dakinsa. Kyawun wadannan hotunan ka kallesu daga kwance kuma bada alwallah ba.
Kwanciya yayi rigingine a gadon hotel din ya dora kafa daya a kan daya, ya ci gaba da bankado hotunan nan na Aisha da Kiki ta antayo masa, yayi ta kallo yana admiring kowacce kankanuwar halittar da ke tare da matarsa “Aisha Siddiqah Yunus”.
Alama ya gani na cewa Kiki ta saka sabon status, a kan whatsapps dinta.
Yana budewa ya ci karo again da zafafan hotunan nasu da suka fi wadanda ta turo masa haduwa da nuna natural beauty din Aisha. Prince har da zooming iya fuskar Aisha, yana kara kare mata kallo, wani irin abu na motsawa a zuciyarsa da illahirin gangar jikinsa, kawai sai ya samu kansa da kiran Kiki a waya ransa a mugun bace, da wani abu mai kama da allura da nan take ya soki zuciyarsa, (KISHI).
Ko mintuna biyar Kiki ba ta yi da dora status din nan ba ta ga kiran Uncle AK yana shigowa cikin wayarta kamar kiran kansa a fusace yake shiga wayarta.
Da murnarta ta daga zata soma yi masa karadinta da korafi da mita na rashin kiransu akai-akai tun tafiyarsa, Hamma yace a fusace.
“Kiki wait, ina so ki cire hotunan Aisha da ki ka dora a status yanzu, idan abokanki da samarinki maza suka gani fa? Ke ba ki san matar aure ba ce ne? Ko an ce miki daya kuke ke da ita?”
Kiki ta hau danne dariya, don bata taba jin Uncle AK na fada haka har da tada jijiyar wuya ba sai yau, fada sosai yake yi kamar ya ari baki ya kara akan nasa, bai ma dace dashi ba tunda sparking irin wannan ba halinsa bane.
“Na baki minti daya maza-maza ki sauke su duka”.
Kiki ta ce cikin kokarin boye dariyar da ta taho mata.
“Uncle I’am sorry zan sauke su yanzu”.
Hamma ya koma da baya ya kwanta, ya kasa ajiye wayar ya ci gaba da kallon matarsa Aisha-Siddiqah, wani kallo na kurillah da bai taba yi mata ba sai yau.
A zuciyarsa har tasbihi, yake domin Ubangiji ya yi halitta. Har gaya wa kansa yake wai wannan beautiful sweet 16 din matarsa ce, wane kyakkyawan aiki ya yi wa Ubangiji haka, da ya cancanci wannan kyautar da bai taba tsammanin samu ba?”.
Komawa ya yi kan status din Kiki yana saving kowanne cikin wayarsa. Sai kuma ya ga Kiki na sauke wa din. Uncle ya kasa karashe sauran kwana biyunsa a France, a kwanansa na shidda ya canza booking. Gara ya koma gida haka, kafin Kiki ta koyawa Aisha bariki. Don yaga gabadaya ta canza masa mata, fatar jikinta da tsarin kwalliyarta duk ya canza.
“Uncle sai ka bamu kudi, kudi sosai fa, muna da activities masu yawa nida Pretty. Kama daga Shopping, zuwa su Hiking da Camel Riding. Tunda Aisha ta zo na tabbata ko sau daya ba ka fita da ita ta ga kasar nan ba”.
“Ke ba sai ki fito da itan ba, uwar ‘yan kankanba da kilbibi, baki kamar na Aku-kuturu, halan ba’a gasa bakinki yayin omogwu ba?”.
Kiki tasa dariya tace, “ka tambayi Maman Hakeem (Aunty Taiwo). Nidai kawai Uncle ka yi mana izini muna da wuraren zuwa mu mike kafa tunda baka nan”.
Katin cirar kudinshi na daya daga cikin bankunan da yake ajiya ya ciro ya mika ma Kiki, ya ce, su sayi ko me suke so har ya dawo.
Sannan zai bar masu mukullin mota daya Kiki ta kai su ‘tour round the city’.
“Banda kai wa dare Kiki, kin ji na gaya miki”.
Kiki ta amshi credit card din ta yi godiya, ta ce, “Insha Allahu Uncle ba za mu dinga yin dare ba”.
Aisha dai tana gefe tana jera abincin da ta gama bisa tebir ba ta saka musu baki ba.
Kiki ta ce, “Aisha ki yi mana godiya mana, an bamu dama mu je shopping, kuma in kai ki tour cikin gari”.
Dan murmushin gefen baki Aisha ta yi ta ce, “Kiki ni ba abinda zan saya, sannan kuma bana son yawo, gajiya zan yi”.
Kiki ta ce, “Ai da ma ban tambaye ki ko za ki sai wani abu ba, ni na san duk abin da ki ke bukata kuma ni zan dauko miki”.
Hamma bai saurare su ba, ya ja kujerar dining daya ya zauna, yau ma a tsakiya suka saka shi, Aisha na dama Kiki na hagu, suka soma cin abincin.
Bayan Kiki ta yi serving dinsu kamar jiya. Jefi-jefi Kiki da Uncle dinta na magana cikin yarbanci akan abin da ya shafe su.
Maganar Kiki kullum guda daya ce, ‘yasa baki Maman Hakeem ta yarda Tosin ya iso gida, tunda dai shi da take kafa hujja da shi din yanzu ya kama Dahir”.
Aisha ta kudire a ranta zata kara zagewa wajen koyon harshen yarbanci da gaske daga ranar yau, don ta lura Prince ba ya so ta ji ko me suke tattaunawa, shi ya sa ma ya koma magana cikin kasaitaccen yarbancinsa.
Kiki ta ce,
“Uncle AK da ban zo ba kenan haka za ka tafi ka bar Aisha a gidan nan ita kadai?”
Prince ya harare ta, ya ce,
“Kiki ke ce uban ne ko ni ne?”
Dariya ta yi, Aishama saida ta murmusa, ta ce, “Amma dai Uncle amarya ba’a barinta ita kadai a gida, son samu a ce tafiyar nan France tare ku ka yi ta, (as in honeymoon a tsakiyar birnin masoya irin Paris) koh?”.
Kunya ta nuna a fuskar Uban Kiki. Yayi maza yace “na gaya miki amma tournament za ni je ko? Kiki why are you disturbing me?”
Kiki ta bar zancen don bata son bata masa rai, ta ce,
“Shi ke nan Uncle, Allah ya kiyaye hanya. ‘yar ka zata kula maka da Aisharka har sai ka dawo!”.
Prince ya tashi da daddare, Kiki ta tsara musu duk abubuwan da za su gudanar yadda za su mori satin sosai, kafin ya dawo.
Tana so Aisha ta san gari, ta kuma daina bakunta da rashin sakewa a gidanta.
Washegari suka shirya ko break fast ba su yi a gida ba, suka tafi shopping. Kiki ita ce mai diban kaya Aisha mai tarawa. Kiki ta daukar wa Aisha lingeries, English wears da nighties kala-kala data lura bata dasu, ta ce,
“Daga yau bake ba kara saka atamfa a cikin gida, musamman in yana gidan, sai wadannan da na zabar miki in dai kinason zaman lafiya da ni”. Aisha tayi dariya tace “wasa kike yi Kiki, kema kinsan bazan iya ba”. Kiki tace “to ki ajiye ki boye, can gaba in kin yi kilin zasu yi miki amfani”.
Sosai Kiki ta bata dariya.
Suka koma bangaren kayan wanka ta daukar mata su feminine wash, deosprays da su body scrub, daga nan suka je ‘sight seeing’.
Ba su dawo gida ba sai yamma lis.
Haka washegari suka sake ficewa zuwa ganin Penguins, waterfalls da wajen Camel Riding.
Ana saura kwana uku Prince zai dawo kiki ta kai ta aka yi mata SPA da Moroccan Hammam (wajen gyaran jiki na mata na Moroccan Hammam).
Nan aka wanke Aisha tas, aka yi mata spa, body scrubing, pedicure da manicure, har da gyaran gashi, aka wanke gashin Aisha aka yi steaming dinsa, sai ga fatar Aisha har sheki ta ke yi abin gwanin ban sha’awa, dama ga ta fara tas, to sai ta koma pinkish, har wani jaja-jaja fatarta ke yi.
Kiki da aka kammala gyaran Aisha ta saita camera ta kashe ta da kyawawan hotuna, kuma bada saninta ba kawai Kiki ta tura su wayar Uncle dinta, ta (whatsapp application) dinshi.
Saura kwana biyu Prince ya dawo da yammaci suka ga wani guri ana YOGA. Don haka washegari tun da safe suka shirya suka tafi YOGA.
A can suka wuni sur! Aisha ta ji dadin session din nasu a can, waje ne na motsa jikin mata zallah, sai yamma lis suka dawo gida.
A YOGA ma sun yi hotuna masu kyau, kawai Kiki ta hau turawa babanta hotunan da suka dauka na charming lady dinsa AISHA-SIDDIQAH ba tare da Aisha ta sani ba.
**** **** ****
Prince yana reception na hotel din da ya sauka a kasar France yana hutawa kafin ya haura sama zuwa dakinsa, kawai sakon Kiki ya cimmasa.
Yana budewa kyakkyawar surar ta bayyana kamar da an tabata jini zai yi tsartuwa. Gabadaya fatar jikin Aisha ta canza daga yadda ya santa. ‘Moroccan Hammam’ din da ta sha da SPA sun karbeta, gashin kanta ya sha steaming da gyara na musamman ya kwanta a dokin wuyanta, gashi bakikkirin da shi, sai sheki yake yi.
Wani bala’in murmushi da ta sakarwa Kiki a hoton, sai daya kusa kashe idon Prince Abdulrasheed Kehinde.
Bai taba yi mata kallon da har zai ga natural features dinta a fili ba, sai yau a hoton nan.
He was dumb founded, domin bai taba ganin abu mai kyau irin Aisha-Siddiqah ba.
Ga naivity ga innocence appearance dinta wadanda sune attributes dinta da ya fi so. Prince jinsa ya yi duk ya zama wani upset, a karshe ya kasa zaman reception din domin ji yake tamkar bafaranshan da ke bayanshi yana taya shi kallon hotunan matar tasa, sai kawai ya rufe ya tashi ya bar reception din, ya bi lift zuwa dakinsa. Kyawun wadannan hotunan ka kallesu daga kwance kuma bada alwallah ba.
Kwanciya yayi rigingine a gadon hotel din ya dora kafa daya a kan daya, ya ci gaba da bankado hotunan nan na Aisha da Kiki ta antayo masa, yayi ta kallo yana admiring kowacce kankanuwar halittar da ke tare da matarsa “Aisha Siddiqah Yunus”.
Alama ya gani na cewa Kiki ta saka sabon status, a kan whatsapps dinta.
Yana budewa ya ci karo again da zafafan hotunan nasu da suka fi wadanda ta turo masa haduwa da nuna natural beauty din Aisha. Prince har da zooming iya fuskar Aisha, yana kara kare mata kallo, wani irin abu na motsawa a zuciyarsa da illahirin gangar jikinsa, kawai sai ya samu kansa da kiran Kiki a waya ransa a mugun bace, da wani abu mai kama da allura da nan take ya soki zuciyarsa, (KISHI).
Ko mintuna biyar Kiki ba ta yi da dora status din nan ba ta ga kiran Uncle AK yana shigowa cikin wayarta kamar kiran kansa a fusace yake shiga wayarta.
Da murnarta ta daga zata soma yi masa karadinta da korafi da mita na rashin kiransu akai-akai tun tafiyarsa, Hamma yace a fusace.
“Kiki wait, ina so ki cire hotunan Aisha da ki ka dora a status yanzu, idan abokanki da samarinki maza suka gani fa? Ke ba ki san matar aure ba ce ne? Ko an ce miki daya kuke ke da ita?”
Kiki ta hau danne dariya, don bata taba jin Uncle AK na fada haka har da tada jijiyar wuya ba sai yau, fada sosai yake yi kamar ya ari baki ya kara akan nasa, bai ma dace dashi ba tunda sparking irin wannan ba halinsa bane.
“Na baki minti daya maza-maza ki sauke su duka”.
Kiki ta ce cikin kokarin boye dariyar da ta taho mata.
“Uncle I’am sorry zan sauke su yanzu”.
Hamma ya koma da baya ya kwanta, ya kasa ajiye wayar ya ci gaba da kallon matarsa Aisha-Siddiqah, wani kallo na kurillah da bai taba yi mata ba sai yau.
A zuciyarsa har tasbihi, yake domin Ubangiji ya yi halitta. Har gaya wa kansa yake wai wannan beautiful sweet 16 din matarsa ce, wane kyakkyawan aiki ya yi wa Ubangiji haka, da ya cancanci wannan kyautar da bai taba tsammanin samu ba?”.
Komawa ya yi kan status din Kiki yana saving kowanne cikin wayarsa. Sai kuma ya ga Kiki na sauke wa din. Uncle ya kasa karashe sauran kwana biyunsa a France, a kwanansa na shidda ya canza booking. Gara ya koma gida haka, kafin Kiki ta koyawa Aisha bariki. Don yaga gabadaya ta canza masa mata, fatar jikinta da tsarin kwalliyarta duk ya canza.