Sashe 17
Aisha Siddiqa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duka wannan ma a rashin saninsu a kunnen Prince Abdulrasheed, domin ya kasa nisa da dakin Aisha, bayan jin maganarta ta dazu, sai ya zama glued ga son jin me zata ce kuma, bayan data fahimci ya ji kallon Babanta take masa, don haka a jikin tagar dakin Aisha wadda kuma take a bude yake tsaye yana jiran isowar Pareto inda yake, domin su karasa su zaga cikin ‘Ranch’ don tabbatar da lafiyar Dawakan, don Pareto ya gaya masa a waya cewa Saheeb ba ya jin dadi.
Shiyasa ma ya kasa kwanciya ba tare da ya zo ya duba lafiyarshi ba.
Hasken fitilun lantarki na alfarma manya da kanana sun taimaka sun maida daren kamar tsakar rana a hamshakin ‘Ranch House’ din na Prince Abdurrasheed (Kehinde) Idris Akanni.
Ga dukkan mamakin Abdurrasheed, sai ya ji ransa ya sosu matuka, yana kuma cigaba da sosuwa da wannan labarin da Aisha take baiwa Kiki a kan ‘Ex’ dinta Ishaq Nafada. A ransa ya ce, ashe ma tana tsaka a kogin soyayya da wani banza can aka tsigota ni aka ba ni? Saboda cewa nayi na rasa matar aure ko? Bayan an san bata da gurbin saka kowa a zuciyarta shine ni aka bani? Irin wannan soyayyar ta kuruciya wuyar mantawa ne da ita a zuciyar mace.
Ga shi nan da aurensa ma kuma a gidansa take ci gaba da bada labarin tsohon saurayinta cikin bege mai tsanani.
Abdurrasheed ya ji wani irin bacinrai na taso masa, kafin haushin kansa mai tsanani ya kama shi, ina ruwansa da yarinyar nan nema? Balle Ex BF dinta ya dame shi? Ya girgiza kai yana ce da kansa, to tun farkoma meye nasa na jin haushi don yayi musu laben da shi yasa kansa? Allah ma ai ya hana labe.
A take Prince ya baima kansa amsa da cewa, ai ko babu komai shine mijinta a yanzu, akwai igiyar aurensa har ukku rus a kanta, wadda ko babu So, tabbas akwai ta. Aure kuma girman matsayinsa da martabarsa ya wuce duk yadda za’a kwatantashi. Darajarsa dole a jita a rai ko da So ko ba So. Ba wai don wani abu daban ba yaji haushin maganar saurayin Aisha sai don cewa shine mijinta yanzu short and simple. Kwarai kalmar nan ta Aisha “Babanta/Babban Yayanta/Uncle dinta” ta zafafe shi a rai.
Wato shi ga shi tsoho ko? Irin sa’an Babanta dinnan, don haka yaro sabon jini can shi ta ke tunawa da bege da soyayya a matsayin daidai ita. To shi yanzu in ma ba ya fada da bakinsa ba wa zai ce shekarunsa 42? Yau da babu Kiki a gidannan sai Aisha ta farraqe banbancin aya da tsakuwa, don sai ta gaya masa da bakinta yaushe ya haifeta, don kawar da komai zaiyi a tsakaninsu na rashin sabo da rashin soyayya ya nemi hakkinsa na aure, ta hakanne zai nuna mata miji ko dogara sanda yake yi don tsufa sunansa miji ne ba “Uncle” ba a gun matarsa koda kuwa ace ita matar jaririya ce don yarinta.
Isowar Pareto ne ya katse masa zazzafan tunanin, amma yaji dadin isowar tasa koba komai ya ceceshi daga sauraron Kiki da Aisha, don baya son cigaba da jin muryar Aisha, kasancewar ta jefashi a tunani da bacin rai, kuma tunaninta da Ex dinta zafi yake masa a rai, don bai saba da irinsa ba. Karfi da yaji maganganun Aisha da sanyin muryar tannan so suke yi su jefa shi a wani hali na jin radadin kishi wanda bai saba da shi ba.
Da Pareto ya iso inda yake sai Prince ya taka ya wuce gaba. Pareto na binsa a baya, suka karasa stable din Saheeb, don abinda ya fito da shi cikin daren kenan, wato ya duba lafiyarsa sosai don shima ya tabbatar Dokin ya rage walwala a satinnan.
Yace da Pareto dole da safe yayi gaggawar kiran Vetrenary Doctor din Saheeb ya bashi allura da magani.
Daga nan ya rufe ko’ina na gidan ya kashe wutar falon ya sa kai zuwa dakin barcinsa, yana shiga ya maida kofa ya rufe kansa. Lokacin kusan karfe goma na dare. A dakinma Prince kasa barci yayi akan lokacin da ya saba, Aisha’s low tone voice mai nuna tayi rashin abinda bazata iya mayarwa ba wato soyayyarta da Ishaq Nafada, ya tsaya masa a rai. Bai so aka hado shi da wadda zuciyarta na tareda waninsa ba.
Amma yanata sharewa da baiwa kansa tabbacin ba kishi bane ke damunsa, it’s just normal ai aure ne, tunda koma meye aurenta yake yi shiyasa yaji ba dadi, ya kuma ji tana zancen waninsa a gidansa ko wanene dole zuciyarsa ta motsa.
Duk yadda Kiki ta yi kokarin wai Aisha ta tafi ‘master-bedroom’ din Hamma ta tayashi kwana, har tana gaya mata cewa ta dinga kokarin yi masa tausa da kanta zata samu lada, don ta ga da injin tausa yakewa kansa messege, dan Polo ne dole zai bukaci yawan tausa kullum, tace ta tafi don Allah ta samu ladansa ta bar mata dakin ita kadai, Aisha tayi fumfurus ta ki amincewa, ta ce,
“Kiki ki rage karambani, da kaini inda Allah bai kai ni ba, ki bar mu yadda ki ka same mu kin ji ko malama, har gobe zamu cigaba da zamanmu ne irin wanda kika zo kika taras, a matsayin ‘Diya da Ubanta”.
Sai Kiki ta kule, dama tana da saurin shaka, ta jefa pillow a kan gado ta haye can karshen gadon, ta ja duvet din bisa gadon ta rufe rabin jikinta ta juyawa Aisha baya, tana cewa.
“Zauna nan wayiya, ki ci gaba da maida shi Baba, in kinso ma kice masa Kaka, har ranar da zai samo wadda za ta dauke shi Darling, duk girman nasa.
A gefe guda kuma mala’ikun rahma sunata kwashe miki albarka!”.
Aisha ta zaro ido tace,
“Kiki!”.
Kikin tace daga kwance, tana kara jan duvet ta rufe har saman kanta,
“Yess, gaskiyar maganar kenan. Mala’iku nata tsine miki. Kina kwarar Babana Aisha me yayi miki? Baki duba shekarun da ya kwashe babu aure ba haba, yayi auren ma bada son ransa ba amma kina raba daki da shi ba wata kulawa ba tarairaya. Ina gani fa ko magana ba kya son yi masa shikuma duk ya damu da rashin kula shi da kike yi
Am sure ba haka Nenne ta zata zaki yi ba”.
Daga haka Kiki bata kara magana ba ta soma jan rago (minshari) ta bar Aisha a zaune dungurgur, tana tunani da jin ba dadin hakan a zuciyarta. Musamman data ambato Nenne. Ta kuma tuna amanar da Nennen ta bata akansa na ta yi kokari ta canza shi daga yadda ta same shi.
Amma ba abinda zata iya a cikin abinda Kiki ke so tayi wato tafiya (master bedroom) da sunan ta biyo miji turaka. Ko wanda Nenne ke so tayi, wato ta dinga shiga rayuwarsa tana motsi, alhalin shi da yake namiji bai nemi faruwar hakan ba in one way or the other.
“Kiki kuma sai in tafi uninvited? Walk before you run Dear. Komai dan a hankali ne, kuma komai da lokacinsa, amma ni bazan je ba tareda ya nemi zuwana ba”.
Kiki da farko ta yi mata shiru, don minsharin karya take yi, tasan ta hada mata zafi, amma don Aisha ta san ta jita kulata ne bazata yi ba, sai ta kware bargon ta mike ta dauko wayarta a caji, ta kunna ta zauna gefen ta soma kiran layin Tosin AbdulNaseer, ta murguda baki tana cewa,
“ni in ki ka kara kula ni Allah ya isa, tunda ba kya son Babana”.
Kiki sai ta koma bata dariya rigimarta da giringidishinta Allah yayi yawa dasu, kamar ‘yar fari ba uata ba, ta kuma yarda kaunarta da Uncle dinnata mai girma ce don tsakaninta da Allah tayi Allah ya isan.
Washegari da safe ma sun sha gardama ita da Kiki, don Kiki ta dage sai ta bi Uncle daki ta gaishe shi da safiya.
Aisha ta ce, “Kiki ki bari sai ya fito (sitting room), ki fahimceni bana son wuce gona da iri, tukunnama kan ki zo kin san ya muke zaune da yanzu za ki bi ki dame ni a kan abinda bazan iya ba, ba kuma zai taba yiwuwa tsakaninmu ba?”
Kiki ta shaka, ta yi kwafa ta kyale ta, ko girkin safe da Aisha ta fara Kiki wanka ta shige ta ki taya ta, ta ce tunda ba ta je ta gaida Babanta ba bazata kuma taya ta girki ba.
Da misalin karfe goma na safe Prince Abdulrasheed ya fito (sitting raoom) din. Yana sanye da kayan barci farare sol. Daren yau ne zai tashi zuwa kasar France wasan tseren Doki na Concacap Polo Championship.
Aisha ya hango a kitchennette ita kadai, tana kai da komowa, don kokarin hada musu karin kumallo.
Motsin Uncle da kamshin turarensa ta ji a bayanta yana shigowa madafin. Da hanzari ta juyo sai ta ga Uncle ne cikin kayan barcinsa, da alama ko wankan safe bai kai ga yi ba. Aisha sai ta tsugunna ta gaishe shi, ya amsa a dake yana cewa,
“Ina bakuwar taki ta barki da aiki ke kadai?”
Aisha ta amsa da cewa, “Kiki ta shiga wanka”.
Ya ce, “Yau zan yi tafiya zuwa tournament, zan yi akalla sati guda kafin na juyo.
Kiki ta gaya min ta fasa tafiya gobe za ta zauna dake har sai na dawo.
Sai ki kula da gidan, da komai, kada ki manta ban da zuwa wajen Horses don suna harbi da kafafunsu.
Musamman Saheeb, ba ya so kowa ya je inda yake in ba ni ko Pareto ba, he is very Anti Social”.
Shiyasa ma ya kasa kwanciya ba tare da ya zo ya duba lafiyarshi ba.
Hasken fitilun lantarki na alfarma manya da kanana sun taimaka sun maida daren kamar tsakar rana a hamshakin ‘Ranch House’ din na Prince Abdurrasheed (Kehinde) Idris Akanni.
Ga dukkan mamakin Abdurrasheed, sai ya ji ransa ya sosu matuka, yana kuma cigaba da sosuwa da wannan labarin da Aisha take baiwa Kiki a kan ‘Ex’ dinta Ishaq Nafada. A ransa ya ce, ashe ma tana tsaka a kogin soyayya da wani banza can aka tsigota ni aka ba ni? Saboda cewa nayi na rasa matar aure ko? Bayan an san bata da gurbin saka kowa a zuciyarta shine ni aka bani? Irin wannan soyayyar ta kuruciya wuyar mantawa ne da ita a zuciyar mace.
Ga shi nan da aurensa ma kuma a gidansa take ci gaba da bada labarin tsohon saurayinta cikin bege mai tsanani.
Abdurrasheed ya ji wani irin bacinrai na taso masa, kafin haushin kansa mai tsanani ya kama shi, ina ruwansa da yarinyar nan nema? Balle Ex BF dinta ya dame shi? Ya girgiza kai yana ce da kansa, to tun farkoma meye nasa na jin haushi don yayi musu laben da shi yasa kansa? Allah ma ai ya hana labe.
A take Prince ya baima kansa amsa da cewa, ai ko babu komai shine mijinta a yanzu, akwai igiyar aurensa har ukku rus a kanta, wadda ko babu So, tabbas akwai ta. Aure kuma girman matsayinsa da martabarsa ya wuce duk yadda za’a kwatantashi. Darajarsa dole a jita a rai ko da So ko ba So. Ba wai don wani abu daban ba yaji haushin maganar saurayin Aisha sai don cewa shine mijinta yanzu short and simple. Kwarai kalmar nan ta Aisha “Babanta/Babban Yayanta/Uncle dinta” ta zafafe shi a rai.
Wato shi ga shi tsoho ko? Irin sa’an Babanta dinnan, don haka yaro sabon jini can shi ta ke tunawa da bege da soyayya a matsayin daidai ita. To shi yanzu in ma ba ya fada da bakinsa ba wa zai ce shekarunsa 42? Yau da babu Kiki a gidannan sai Aisha ta farraqe banbancin aya da tsakuwa, don sai ta gaya masa da bakinta yaushe ya haifeta, don kawar da komai zaiyi a tsakaninsu na rashin sabo da rashin soyayya ya nemi hakkinsa na aure, ta hakanne zai nuna mata miji ko dogara sanda yake yi don tsufa sunansa miji ne ba “Uncle” ba a gun matarsa koda kuwa ace ita matar jaririya ce don yarinta.
Isowar Pareto ne ya katse masa zazzafan tunanin, amma yaji dadin isowar tasa koba komai ya ceceshi daga sauraron Kiki da Aisha, don baya son cigaba da jin muryar Aisha, kasancewar ta jefashi a tunani da bacin rai, kuma tunaninta da Ex dinta zafi yake masa a rai, don bai saba da irinsa ba. Karfi da yaji maganganun Aisha da sanyin muryar tannan so suke yi su jefa shi a wani hali na jin radadin kishi wanda bai saba da shi ba.
Da Pareto ya iso inda yake sai Prince ya taka ya wuce gaba. Pareto na binsa a baya, suka karasa stable din Saheeb, don abinda ya fito da shi cikin daren kenan, wato ya duba lafiyarsa sosai don shima ya tabbatar Dokin ya rage walwala a satinnan.
Yace da Pareto dole da safe yayi gaggawar kiran Vetrenary Doctor din Saheeb ya bashi allura da magani.
Daga nan ya rufe ko’ina na gidan ya kashe wutar falon ya sa kai zuwa dakin barcinsa, yana shiga ya maida kofa ya rufe kansa. Lokacin kusan karfe goma na dare. A dakinma Prince kasa barci yayi akan lokacin da ya saba, Aisha’s low tone voice mai nuna tayi rashin abinda bazata iya mayarwa ba wato soyayyarta da Ishaq Nafada, ya tsaya masa a rai. Bai so aka hado shi da wadda zuciyarta na tareda waninsa ba.
Amma yanata sharewa da baiwa kansa tabbacin ba kishi bane ke damunsa, it’s just normal ai aure ne, tunda koma meye aurenta yake yi shiyasa yaji ba dadi, ya kuma ji tana zancen waninsa a gidansa ko wanene dole zuciyarsa ta motsa.
Duk yadda Kiki ta yi kokarin wai Aisha ta tafi ‘master-bedroom’ din Hamma ta tayashi kwana, har tana gaya mata cewa ta dinga kokarin yi masa tausa da kanta zata samu lada, don ta ga da injin tausa yakewa kansa messege, dan Polo ne dole zai bukaci yawan tausa kullum, tace ta tafi don Allah ta samu ladansa ta bar mata dakin ita kadai, Aisha tayi fumfurus ta ki amincewa, ta ce,
“Kiki ki rage karambani, da kaini inda Allah bai kai ni ba, ki bar mu yadda ki ka same mu kin ji ko malama, har gobe zamu cigaba da zamanmu ne irin wanda kika zo kika taras, a matsayin ‘Diya da Ubanta”.
Sai Kiki ta kule, dama tana da saurin shaka, ta jefa pillow a kan gado ta haye can karshen gadon, ta ja duvet din bisa gadon ta rufe rabin jikinta ta juyawa Aisha baya, tana cewa.
“Zauna nan wayiya, ki ci gaba da maida shi Baba, in kinso ma kice masa Kaka, har ranar da zai samo wadda za ta dauke shi Darling, duk girman nasa.
A gefe guda kuma mala’ikun rahma sunata kwashe miki albarka!”.
Aisha ta zaro ido tace,
“Kiki!”.
Kikin tace daga kwance, tana kara jan duvet ta rufe har saman kanta,
“Yess, gaskiyar maganar kenan. Mala’iku nata tsine miki. Kina kwarar Babana Aisha me yayi miki? Baki duba shekarun da ya kwashe babu aure ba haba, yayi auren ma bada son ransa ba amma kina raba daki da shi ba wata kulawa ba tarairaya. Ina gani fa ko magana ba kya son yi masa shikuma duk ya damu da rashin kula shi da kike yi
Am sure ba haka Nenne ta zata zaki yi ba”.
Daga haka Kiki bata kara magana ba ta soma jan rago (minshari) ta bar Aisha a zaune dungurgur, tana tunani da jin ba dadin hakan a zuciyarta. Musamman data ambato Nenne. Ta kuma tuna amanar da Nennen ta bata akansa na ta yi kokari ta canza shi daga yadda ta same shi.
Amma ba abinda zata iya a cikin abinda Kiki ke so tayi wato tafiya (master bedroom) da sunan ta biyo miji turaka. Ko wanda Nenne ke so tayi, wato ta dinga shiga rayuwarsa tana motsi, alhalin shi da yake namiji bai nemi faruwar hakan ba in one way or the other.
“Kiki kuma sai in tafi uninvited? Walk before you run Dear. Komai dan a hankali ne, kuma komai da lokacinsa, amma ni bazan je ba tareda ya nemi zuwana ba”.
Kiki da farko ta yi mata shiru, don minsharin karya take yi, tasan ta hada mata zafi, amma don Aisha ta san ta jita kulata ne bazata yi ba, sai ta kware bargon ta mike ta dauko wayarta a caji, ta kunna ta zauna gefen ta soma kiran layin Tosin AbdulNaseer, ta murguda baki tana cewa,
“ni in ki ka kara kula ni Allah ya isa, tunda ba kya son Babana”.
Kiki sai ta koma bata dariya rigimarta da giringidishinta Allah yayi yawa dasu, kamar ‘yar fari ba uata ba, ta kuma yarda kaunarta da Uncle dinnata mai girma ce don tsakaninta da Allah tayi Allah ya isan.
Washegari da safe ma sun sha gardama ita da Kiki, don Kiki ta dage sai ta bi Uncle daki ta gaishe shi da safiya.
Aisha ta ce, “Kiki ki bari sai ya fito (sitting room), ki fahimceni bana son wuce gona da iri, tukunnama kan ki zo kin san ya muke zaune da yanzu za ki bi ki dame ni a kan abinda bazan iya ba, ba kuma zai taba yiwuwa tsakaninmu ba?”
Kiki ta shaka, ta yi kwafa ta kyale ta, ko girkin safe da Aisha ta fara Kiki wanka ta shige ta ki taya ta, ta ce tunda ba ta je ta gaida Babanta ba bazata kuma taya ta girki ba.
Da misalin karfe goma na safe Prince Abdulrasheed ya fito (sitting raoom) din. Yana sanye da kayan barci farare sol. Daren yau ne zai tashi zuwa kasar France wasan tseren Doki na Concacap Polo Championship.
Aisha ya hango a kitchennette ita kadai, tana kai da komowa, don kokarin hada musu karin kumallo.
Motsin Uncle da kamshin turarensa ta ji a bayanta yana shigowa madafin. Da hanzari ta juyo sai ta ga Uncle ne cikin kayan barcinsa, da alama ko wankan safe bai kai ga yi ba. Aisha sai ta tsugunna ta gaishe shi, ya amsa a dake yana cewa,
“Ina bakuwar taki ta barki da aiki ke kadai?”
Aisha ta amsa da cewa, “Kiki ta shiga wanka”.
Ya ce, “Yau zan yi tafiya zuwa tournament, zan yi akalla sati guda kafin na juyo.
Kiki ta gaya min ta fasa tafiya gobe za ta zauna dake har sai na dawo.
Sai ki kula da gidan, da komai, kada ki manta ban da zuwa wajen Horses don suna harbi da kafafunsu.
Musamman Saheeb, ba ya so kowa ya je inda yake in ba ni ko Pareto ba, he is very Anti Social”.