Sashe 4
Aisha Saddiqah Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
ya aje kofin hannunsa, yace Aisha wait, ya taso ya isa gareta ya kamo hannunta ya shigo da ita cikin dakin yana cewa. "Ya kinzo turakar miji neman albarka kuma zaki koma?" Aisha duk ta daburce ta rikice tarude, sabida yanayin da Hamma ke mata magana yau ya sha banban dana koyaushe. Ba don ta kasance mai karfin ji bama, da bazata ji shi ba. "Dama-dama... zuwa nayi ince maka Hamma saida safe". Hamma ya dora hannuwansa biyu bisa kafadun Aisha hagu da dama yana murzawa. Ya dan mutstsuka jijiyar wuyanta cikin wani salo na tasowar muguwar sha'awar da baisan akwai a tareda shi ba, saida Aisha ta runtse ido sabida tasowar tata sha'awar ta diya mace, kafin hannunsa ya kai kansa saman kirjinta. Yace "saida safe dinma ai irin haka ake fadarsa Ayshahhh, ba da fatar baki ba. You my dear I want to kiss you again today!". Hamma ya fada admiringly idanunsa akan siraran lips din Aisha, yana musu wani inviting looks. Aisha ta kusa narkewa bakidayanta domin a lokacin Hamma ya matsota sosai ne a jikinsa, ya isa cikin nutsuwa ya hade bakinsu wurin guda ya soma sumbatar Aisha a tsanake, sannan ya koma kissing hungrily. Ashe namiji duk dadewar sa babu aure, ba sai an koya masa sumba ta auratayya ba? Ko da kuwa ya fidda rai da ita, ko bashi da sha'awar ta, sanda zata sameshi zai ji tane tana sarrafashi. To hakan ce ta faru da Prince Abdulrasheed yau. Da ya samu kissable lips din Aisha yau ya dinga tsotso tamkar Allah ya aikoshi, saida ya ajiye kishirwar shekaru masu yawa na kuruciya dana shiga girma. Aisha kyale Prince tayi ya yi yadda duk yake so yau, ya jagwalgwala ta iya son ransa a duk ta inda yake so. Ya tsotse duk abinda yake so. Kuma shi da kansa yayiwa kansa limit. Don yana ganin in ya kauda budurcinta any moment zata iya conceiving, shikuma yana ganin kamar bata yi kwarin da zata haihu ba. Tunda har ya samu wannan access din zai iya karawa Aisha lokaci. A kwanaki goma da suka biyo bayan wannan ranar, wata wawuyar shakuwa ce ta shiga tsakanin Hamma da Aisha. Suna kwana a gado guda, Hamma saida ya san yadda yayi ya fara raba Aisha da dukkan sittirun jikinta in zasu kwanta, yana rabar Aisha da dabara da wayau da simple hugs, da light kiss masu sawa ta saki jiki da shi, su yi barci manne da juna. Tun Aisha matukar jin nauyi da tsoro har ta soma sakewa da Hamma sosai. Don ta lura ba shi da nufin abinda take tsoro. Kusan sati biyu kenan irin rayuwar da suke yi a cikin gidan kenan, full of understanding, intimacy and love, Hamma ya zama baya iya barci bai raba jikinsa dana Aisha ba, bai sumbaci bakinta da kirjinta yadda yake so ba amma bai taba wuce hakan ba yake takawa kansa birki, don a ganinsa har lokacin Aisha bata yi girman data isa ya dora mata hidimar dake cikin aure yanzu ba kada tazo haihuwa ta samu matsala. Amma me? A na I gobe zasu tafi Lagos komai kwace masa yayi, ya kasa controlling kansa yadda ya saba duk kuwa da yana tausayawa Aisha, da kyar da roko da magiya harda kuka Aisha ta kwaci kanta a hannun Prince domin kuwa gani take duk ranar da hakan ta faru ba wata wata mutuwa zatayi, in tayi la'akari da irin yanayin da Prince ke shiga a irin wadannan lokutan akanta. A satin dasu Prince zasu dawo Lagos Dade yasa aka je aka shirya gidan Prince na Banana Island, wanda ke daura da gidan mahaifinsa, Prince ya jima da sayen gidan bai taba amfani dashi ba, tun kafin saukarsu Dade ya gayawa Nenne in sun zo a gidansu zasu sauka. Yasa aka gyara gidan aka shigar komai da zasu bukata. Tun saura kwana uku daurin aure suka sauka a Lagos. Gidan ya debi murnar zuwan su ba babba ba yaro, kowa murnar zuwan Hamma yake yi, ga ‘yan biki sun soma isowa daga sauran jihohi. Kiki ce kawai bata samu zuwa bikin Aunties dinta Princesses ba, don tana shirin rubuta jarrabawarta ta karshe a Informatics a lokacin. Aunty Murjanatu Taiwo tana Ilorin, sai bayan addu’a zata taho Lagos tare dasu Nenne in sun je. Dade yace su Hamma su fara sauka a Lagos su huta kwana biyu, in yaso sai su dunguma duk gidan zuwa Ilorin su samu adddu’ar Sarki ranar asabar, wadda ta kasance kuma ranar daurin auren su Fatima. Nenne ta rasa ina taka saka ina taka aje da surukarta Aisha, wata sabuwar kauna da soyayya Nenne take yiwa Siddiqah musamman data gane suna zaman lafiya itada Hamma, Aisha ta samo kansa shima ya samo nutsuwarta, Nenne bata taba jin Hamma cikin farin ciki da nishadin data ji shi ciki ranar da suka yi waya itada su, tana tsammanin Siddiqah ciki gareta ba. don haka tun kafin saukarsu a Lagos yau Nenne da kanta ta shiga kitchen ta shirya abincin tarbar Hamma da Aisha, ta hada dana Dade, girki tayi masa na musamman data tabbatar Hamma ya dade bai samu irinsa ba, wato (Locust Beans Stew) da suke kira Dindin da (Ofada Rice). Bayan saukarsu da kadan Dade yace ma Prince a gidansu zasu tare, yasa an shirya musu komai da zasu bukata. Don haka ana gama cin abincin dare Dade yace Firdausi ta dauko keys din gidan ta baiwa Hamma, ta yiwa Aisha rakiya kuma. Anan Nenne tace “a’ah Dade, ita kam Aisha ta zauna ta huta anan, a bari sai bayan biki sannan ayi tarewar. Ta jima bata nan akwai bukatar ta huta tukunna”. Ai kuwa nan da nan Prince ya canza fuska. Domin a yau kam yayi niyyar angwancewa da amaryarsa Siddiqah babu daga kafa. In yaso idan ciki ya samu ya tayata nakudar. Yanzu kuma Nenne tana wani zance wanda zuciyarsa ta gaza dauka, wai Aisha ta zauna da ita har bayan biki, duk kokarinsa na rainon da yayi tayi wata da watanni ba’a gani ba, sai rana daya da ya saka ran hutawa. Har dai rashin jin dadin hakan ya gaza boyuwa a fuskarsa, ‘yar damuwa ta nuna a fuskar Prince, amma dai bai yi magana ba. saidai tuni Dade da yake shi namiji ne ya ramfo shi. Lura da yanayinsa da Dade yayi, sai yace. “Kehinde kodai kafi so ku tafi tare yanzu ne?” Zuruf! Aisha tayi tace “Dade ayi hakuri don Allah ni nan zan zauna gun Nenne har a gama biki, nayi kewar Nenne for long”. Taki dago ido balle Prince ya kalli kwayar idanunta. Domin ta riga ta san Prince ya gama kaiwa kul a a dalcinsa. Daren tahowarsu da yaya ta tsira? Balle yanzu a gidansa na gado? Takaicin abinda Ausha tace yasa shima ya hadiye, yace “a’ah Dade, ba wata matsala a kyaleta ta sha zamanta”. Amma Kai da ji kasan shagube ne yayi. Ya ajje spoon ba don ya koshi ba, sai don bazai iya cigaba da ci ba’a gane ransa ya baci ba, da abinda Aisha tayi masa a gaban kowa ta nuna bata damu dashi ba, ya mike yace zai je gidansa ya huta. Bai sake kallon inda Aisha take ba ya nufi hanyar fita falon. Anan ne Nenne ta dubi Aisha tace “raka shi zuwa mota mana Aisha” Hamma, wanda a lokacin har ya kai bakin kofa cikin matukar kulewa zai fice, yace. “A’ah Nenne na yafe, ta zauna kawai, na gode”. Wannan gwasalen da Hamma yayiwa rakiyar Aisha, duk ya faru akan idon amare Princess Fatima da Princess Firdausi, don tare aka zauna cin abincin har dasu gabadaya. Abin yayi matukar yiwa Fatima dadi, na yadda Prince ya nuna bai damu da Aisha a gaban kowa ba. ita bata fahimci haushi yaji don Aisha tace da bakinta bazata bishi ba. Har ta samu abin adarwa a gaba. Fatima na komawa dakinta ta kira Aunty Taiwo, tana mayar mata da yadda aka yi, da irin gwasale tayin binsa gidansa da Prince yayi ga Nenne da Aisha, sai Taiwo tace da Fatima, “ewo, to dama nifa na san Kehinde sarai, nafi kowa saninsa, saninda ko Nenne bata yi masa ba, ba son zama da yarinyar nan yake ba, biyayya yake yi musu don a rabu lafiya da kafaffun iyayenmu da basa shawara, su Nenne ke faman cusa masa ita kamar dusa, kamar ance lafiyayyun mata ‘yan asali na manyan gida sun gama karewa a duniya. Na rantse idona idonta a Lagos ko Ilorin in ta sake tazo, sai nayi mata wulakanci da kaskancin da bazata kara kuskuren zuro jiki cikin zuri’ar Akanni ba, balle ta wani kwashi siraran kafafunta tazo mana biki irin wannan na girma”. A dakinta na baya wato dakin Kiki aka sauketa, kafin ta kwanta saida ta kira Ummanta ta gaya mata saukarsu lafiya a Lagos, sannan ta kira Hamma don tayi masa saida safe ta kuma bashi hakuri da kalamai, amma sai ta samu ya kashe dukka wayoyinsa. Haka ta kwana da tunani da damuwar Hamma a ranta. Washegari da safe ita da Nenne ne suka shirya abin karin Dade da Hamma, sai wajen karfe goma na safe Prince yazo gidan kuma a gurguje suka karya shida Dade zasu fita, bayan yabi Nenne dakinta sun gaisa, yanaso ya tambayi Aisha amma ya dake. Sai gata tana shigowa dakin Nennen dauke da lemun tuffah da sassanyar madarada tanbulan na tangaran akan karamin tray, ta gefensa ta wuce zuwa ciki, taci ado har ta gaji gabadaya ta saje da ‘yammatan amarya da suka cika gidan tun jiya. Ta ajiye a gabansa, don tun safe take dakon shigowarsa duk ta damu, tace a ladabce “Hamma ina kwana?” Yayi mata wani kallo yace “lafiya kalau, yaya gajiyarki?” Nenne aka kirata a waya sai ta fita daga dakin tana amsa wayar. Aisha bata yi aune ba taji Prince ya kamata ya mikar daga durkuson data yi a gabansa ya jata zuwa kusurwar dakin ya matseta sosai a jikinsa, sannan ya manne ta a kirjinsa da wata zazzafar hug, ya rage tsaho ya sumbaci lips dinta lightly, yace, “Aisha jiya banyi barci ba isashshe saboda rashin ki a gadona Aisha, I missed you and your sweet lips, me yasa kika yimin hakane wai?” Ya yi mata