← Book details Aisha Saddiqah Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 25

Sashe 13

Aisha Saddiqah Part 4 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Kwanan sa biyu a Gombe. Rana ta farko da yaje ga yadda suka kwashe da Baba Barau, don haka ya sake kwana a Gombe. Washegari ya sake komawa wajen Baban Aisha da Umman ta, ya gaya musu yadda sukayi shi da Baba Barau, ya Kuma roki Abban Aisha don Allah ya taya shi baiwa Baba Barau haquri.
Malam Yunus ya lallashe shi ya ce ya koma gida zai ma Yayansa magana, dan har ga Allah yaji tausayin sa.
Prince ya saki jiki da iyayen Aisha kamar ba jiya ya fara zuwa ba. Sukayi developing good bond. He is open minded, ga kuma hankali. Amman kana ganin sa kaga damuwa.
Abban Aisha yace masa kar ya damu yaje gida zai saka baki. Kuma kada yaje gidan baba Barau yau tunda jiya ya je, zai neme shi da kansa, yace yayi haq9uri har ya neme shi din.
Prince ba yadda ya iya haka ya dawo Lagos bai san makomar aurensa ba.
A daren ranar yana tareda iyayen sa a falon gidansu. Dade ya tambaye shi "toh ya akayi a gomben?" Nan Prince ya fada masa komai, yace murya ba kuzari "nidai Dade ba don Taiwo yar uwata bace da na mata Allah ya isa, finally i have a glimpse of happiness, ta lalata min shi, wannan wani irin rashin sa’a ne?" Prince ya fadawa Babansa in a heartbreaking manner.
Yasa hannu ya dafe kan sa. Sai ya ba Dade tausayi matuka. Suna haka aka kira shi daga Qatar, Dade yana jin sa yace musu bashi da lafiya su qara mashi 2 weeks.
Sai bayan ya aje wayar ne Dade yace masa "toh ka koma mana sai ka dawo daga baya? By then itama ta huce Aysha din". Prince yace "Dade ko na koma bani da nitsuwar yin aikin, gara dai inyi ta fama ko zata haqura. in kuma taqi haqura sai na koma din.
It seems that’s the life my own twin thinks i deserve, a lonely, sad life, unworthy of pure happiness… and apparently you and Nenne too....".
Prince ya furzar da numfashi me daci a kasalance ya tashi zai wuce gidansa. Dade yace "why will u say that?" A marairaice Prince yace "toh ba cewa kukai ba ruwanku ba Dade? Ni iyayen aysha basu sanni ba ku suka sani. And if we are being honest I am nothing but good to Aysha.
Ita in yarinta ya debe ta ba se a duba ni ba. Ni da ba ni nayi laifin nan ba and also ba ni nasa Taiwo ba. Amman duk laifin ya dawo kaina kuma kunyi shiru kunce ba ruwanku. Gaskiya i won't forgive Taiwo for this Dade she really did hurt me…." ya tashi zai tafi ya juya kenan sai kuwa sukayi ido hudu da ita. Taiwo. Jikinta yai sanyi, tazo ne immediately don Dade ya aika a kirata dazu.
Ko kallonta Prince baiyi ba ya fita ya tafi gidan sa.
Nan iyayen sukayi mata tatasss, don Nenne ma taji me yace ma Dade tana daga dakin Dade din, kamar yadda Taiwo taji itama tana shigowa. A ranta ta fara nadama. Ga nasihar da iyayen ke mata suna kuma nuna mata ta butulcewa son da Kehinde yake mata in har itace zata saka shi a wannan halin.
To duk wannan ya taru yasa Taiwo ta damu, a lokacin ta baiwa iyayensu haquri ta koma gida ta wuce ta sai tiket din tafiya UK.
Bayan fitarta ne Dade da Nenne suka kara tattauna maganar, suka aje lallai Friday zasu je Gombe takanas suyi bikon nan da kansu. Alamu sun nuna fa Hamma yana ta iyo a kogin soyayya. Babansa kuma yasan basu iya so ba, gara ya taimaki magajin sa. Nenne har sallahr nafila tayi ranar ta godiya ga Allah ganewa data gama yi Hamma Abdulrasheed yana son Aisha, ga kuma irin matakin da ya dauka kan Twin dinshi Taiwo da cikinsu da ita kanta Taiwo din babu wanda ya zaci zai iya hakan akan Taiwo. Ta san ko da wasa bazai kara barin wani ya taba Aisha ba, dan haka zasu shirya nan da kwana uku suje Gombe, yau talata, toh ranar Friday ko Saturday zasu je gombe.
Shi Prince bai sani ba ya tafi gidansa haka ya kwana zuciya ba dadi. Sai asubahi ma bacci ya dauke shi, yana tashi yaga ba amfanin zaman Lagos. Bari kawai ya koma Gombe din sai yayi jiran hukuncin Baba Barau a can.
Nan Hamma ya hada 'yar akwatin tafiyarsa ya kira nenne a waya yace zai koma Gombe. Nenne tace ko lafiya ince ko? Prince yace "toh Nenne ai gara ina can in yi ta matsa musu kawai Nenne. Idan Kuma har lokacin basu yarda ba zan tafi inyi reporting wurin aiki…
Tawakkaltu Alallah… na fawwala wa Allah".
Nenne sai taji ta kuma jin tausayinsa masa je ka Hammansu Allah ya ba da sa’a kaji, Allah kuma yai albarka albarka Annabijo".
Prince yace amin Nenne". Ya tafi a ranar ya hau jirgin Gombe.
Chapter 13 · 0% Book details