Sashe 12
Aisha Saddiqah Part 4 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Baban Aisha nan take yace da Sunusi ya raka su gidan Baba Barau din. Sunusi ya saka takalmansa ya shiga gaban mota, Prince na owner’s side, Malam Buhari yaja motar suka tafi, don gidan Baba Barau ba nisa sosai, layi biyu ne tsakaninsa da dan uwansa.
A zaure suka tadda Baba Barau yana cin abinci, ga fura mai sanyi a gefe an ajiye masa a kwanon silba a gefe. A nutse Prince ya yi sallama a zauren. Baba Barau ya amsa duk da bai taba ganinsa ba, don haka da fara’a sosai Baba Barau yake wa hamshakin bakon nasa da bai san ko waye ba barka da zuwa, ya ce.
“Zo nan bisa buzuna ka zauna”.
Prince har da cire hula bayan ya cire takalmansa ya ki hawa buzun ya zauna a kan kafafunsa tankwashe a gabansa. Ya fara gaishe shi da hausarshi da ba ta da kwari.
Baba Barau ya ce, “Ban gane dan nawa ba, daga ina kenan?”
Nan Prince ya gabatar masa da kansa da cewa shine Abdulrasheed daga Lagos. Baba Barau ya kara neman karin haske, don har lokacin bai gane ba, Prince ya kasa magana sai da kyar ya iya cewa “Mijin Aisha-Siddiqah”. Ai nan da nan Baba Barau ya hadiye duk wani annuri da ke fuskarsa, Prince ya kara gaishe shi a ladabce, ya bashi hakuri akan zuwan Aisha. don yana da labarin Baba Barau a bakin Aisha, wani Yayan babanta da ba ya daukar wargi kuma ba ya yarda ko Babanta ya bata mata rai. Yadda Baba Barau ya maida walwalar fuskarsa ne ya sa Prince jin wata irin shakkarsa. Amma hakan bai hana shi fadan abin da ke gabansa ba, ya fara da bada hakuri sannan ya ce masa wallahil azeem shi Aysha tafi karfin wulakanci a garesa. Dalilin ma da ya bari sai yau ya taho kada cece-kuce yayi yawa ne cikin taron bikin. Ya kuma tabbatarwa Baba Barau ya magance matsalar Taiwo. Kuma yayi alkawarin baza’a kara ba. a wannnan gabar Baba Barau kansa ya yaba da hankalin Prince. Ya ce “naji, amma dai a hakura kawai da aurennan, kaima daman ba so kake ba itama haka, to kuma kaga akwai mutunci tsakanin iyayenku mata kada auren nan ya zama silar matsalarsa”.
Murya na rawa Prince yace “Baba ni ia son Aisha…” Baba Barau ya dakatar dashi yace “Abduulrasheed maganar gaskiya yaranmu basa auren wulakanci, munada hakuri amman banda wulakanci, kuma abinda yasa Aisha dawowa gida haka to babba ne, inda duk za’a taba maka iyaye bazakaso zama ba. so ina bayan Aisha kan duk abinda ta yanke, kaje zan neme ka zanyi shawara”.
Jiki a sanyaye Abdulrashid yace “toh Baba, nagode, zan iya ganinAisha yanzu?” Baba Barau yace “a’ah”. Sai yayi shiru na dan lokaci cikin damuwa daga bisani yace “to shikenan Baba zan tafi nagode”.
Suka koma gida, ya kwashe komai na yadda sukayi da Baba Barau ya gayawa Nani Oummana.
Da kyar Nani ta rarrashe shi ya dan ci abinci ya yi mata sallama ya wuce gidansa.
Nani sai ta dau waya ta kira Nenne suka gaisa, Nani ta yi mata ban gajiyar biki da ta hidima, Nenne ta ce, ai har sun dawo Legos, ta kansile da yawan events din bikin da ba su zama dole ba saboda Taiwo data bata ciwon kai. Tana son kashe auren Hammansu babu gaira babu dalili.
Nani ta ce, “Amma Dadensu ya kyauta min da ya wanke ja’ira mai halinsu na yarbawa, mu dai kam Murja ba ta dauko mu ba, can musu cikin Akannin”.
Nenne ta ce, “Ai ko a Akanni babu irin Taiwo. Ita kadai ce da halinta, mijinta ma hakuri yake da nature dinta ba tun yau ba. Tun yana kawo kararta ana sulhu har ya gaji ya yi nesa da ita, sai ya yi watanni uku bai waiwayo ta ba”.
Nani ta ce, “Addu’a za ku dinga yi mata da nasiha ba fushi da ita ba. A shekarunta dai ta yi girman banza”.
Sun dade suna tattaunawa a kan sha’anin Taiwo, har Nenne ta ce, “Ban da abin Murja ma Aisha ba ta ki Hammansu ba saboda ratar shekarun da ke a tsakaninsu sai shi ne zai ki Aisha?
Aisha son kowa kin wanda bai samu ba, na bi sarauta da kudi da gudu, na kama wa Hamma Aisha ne saboda nagarta da iyaye na gari, idan kuwa har Aisha ta fada wa iyayenta abin da Murja ta yi mata, to abu ya baci. Don ba kowa zai yarda a taba mutuncinsa a wanye lafiya ba, shi ya sa daga ni har Dade muka ce babu mu a 'yan biko wai ido da kunya. Shi da ya bar Murja ta ke taka rawa cikin rayuwarsa sai ya nemo ta ta yi masa biko”.
Nani kuma ta ce, “Hamma meye laifinsa? Ana hora shi ne kawai da laifin da ba nashi ba. Ya je bikon ai ga shi ya dawo ba nasara, ya yi min shame-shame a falo kamar gawa. Duk sonsa da fura tunda ya zo bai sha ba”.
Nenne ta ce, mu kyale shi ya yi ta bikonsa shi kadai, ya fi sanin darajar wahalar da aka yi masa aka yi masa aurenta babu ko kobonsa”.
Nani kuma ta ce, “A’a za ta sa uban kasa ya shiga maganar, idan Abdulrasheed ya kasa.
A zaure suka tadda Baba Barau yana cin abinci, ga fura mai sanyi a gefe an ajiye masa a kwanon silba a gefe. A nutse Prince ya yi sallama a zauren. Baba Barau ya amsa duk da bai taba ganinsa ba, don haka da fara’a sosai Baba Barau yake wa hamshakin bakon nasa da bai san ko waye ba barka da zuwa, ya ce.
“Zo nan bisa buzuna ka zauna”.
Prince har da cire hula bayan ya cire takalmansa ya ki hawa buzun ya zauna a kan kafafunsa tankwashe a gabansa. Ya fara gaishe shi da hausarshi da ba ta da kwari.
Baba Barau ya ce, “Ban gane dan nawa ba, daga ina kenan?”
Nan Prince ya gabatar masa da kansa da cewa shine Abdulrasheed daga Lagos. Baba Barau ya kara neman karin haske, don har lokacin bai gane ba, Prince ya kasa magana sai da kyar ya iya cewa “Mijin Aisha-Siddiqah”. Ai nan da nan Baba Barau ya hadiye duk wani annuri da ke fuskarsa, Prince ya kara gaishe shi a ladabce, ya bashi hakuri akan zuwan Aisha. don yana da labarin Baba Barau a bakin Aisha, wani Yayan babanta da ba ya daukar wargi kuma ba ya yarda ko Babanta ya bata mata rai. Yadda Baba Barau ya maida walwalar fuskarsa ne ya sa Prince jin wata irin shakkarsa. Amma hakan bai hana shi fadan abin da ke gabansa ba, ya fara da bada hakuri sannan ya ce masa wallahil azeem shi Aysha tafi karfin wulakanci a garesa. Dalilin ma da ya bari sai yau ya taho kada cece-kuce yayi yawa ne cikin taron bikin. Ya kuma tabbatarwa Baba Barau ya magance matsalar Taiwo. Kuma yayi alkawarin baza’a kara ba. a wannnan gabar Baba Barau kansa ya yaba da hankalin Prince. Ya ce “naji, amma dai a hakura kawai da aurennan, kaima daman ba so kake ba itama haka, to kuma kaga akwai mutunci tsakanin iyayenku mata kada auren nan ya zama silar matsalarsa”.
Murya na rawa Prince yace “Baba ni ia son Aisha…” Baba Barau ya dakatar dashi yace “Abduulrasheed maganar gaskiya yaranmu basa auren wulakanci, munada hakuri amman banda wulakanci, kuma abinda yasa Aisha dawowa gida haka to babba ne, inda duk za’a taba maka iyaye bazakaso zama ba. so ina bayan Aisha kan duk abinda ta yanke, kaje zan neme ka zanyi shawara”.
Jiki a sanyaye Abdulrashid yace “toh Baba, nagode, zan iya ganinAisha yanzu?” Baba Barau yace “a’ah”. Sai yayi shiru na dan lokaci cikin damuwa daga bisani yace “to shikenan Baba zan tafi nagode”.
Suka koma gida, ya kwashe komai na yadda sukayi da Baba Barau ya gayawa Nani Oummana.
Da kyar Nani ta rarrashe shi ya dan ci abinci ya yi mata sallama ya wuce gidansa.
Nani sai ta dau waya ta kira Nenne suka gaisa, Nani ta yi mata ban gajiyar biki da ta hidima, Nenne ta ce, ai har sun dawo Legos, ta kansile da yawan events din bikin da ba su zama dole ba saboda Taiwo data bata ciwon kai. Tana son kashe auren Hammansu babu gaira babu dalili.
Nani ta ce, “Amma Dadensu ya kyauta min da ya wanke ja’ira mai halinsu na yarbawa, mu dai kam Murja ba ta dauko mu ba, can musu cikin Akannin”.
Nenne ta ce, “Ai ko a Akanni babu irin Taiwo. Ita kadai ce da halinta, mijinta ma hakuri yake da nature dinta ba tun yau ba. Tun yana kawo kararta ana sulhu har ya gaji ya yi nesa da ita, sai ya yi watanni uku bai waiwayo ta ba”.
Nani ta ce, “Addu’a za ku dinga yi mata da nasiha ba fushi da ita ba. A shekarunta dai ta yi girman banza”.
Sun dade suna tattaunawa a kan sha’anin Taiwo, har Nenne ta ce, “Ban da abin Murja ma Aisha ba ta ki Hammansu ba saboda ratar shekarun da ke a tsakaninsu sai shi ne zai ki Aisha?
Aisha son kowa kin wanda bai samu ba, na bi sarauta da kudi da gudu, na kama wa Hamma Aisha ne saboda nagarta da iyaye na gari, idan kuwa har Aisha ta fada wa iyayenta abin da Murja ta yi mata, to abu ya baci. Don ba kowa zai yarda a taba mutuncinsa a wanye lafiya ba, shi ya sa daga ni har Dade muka ce babu mu a 'yan biko wai ido da kunya. Shi da ya bar Murja ta ke taka rawa cikin rayuwarsa sai ya nemo ta ta yi masa biko”.
Nani kuma ta ce, “Hamma meye laifinsa? Ana hora shi ne kawai da laifin da ba nashi ba. Ya je bikon ai ga shi ya dawo ba nasara, ya yi min shame-shame a falo kamar gawa. Duk sonsa da fura tunda ya zo bai sha ba”.
Nenne ta ce, mu kyale shi ya yi ta bikonsa shi kadai, ya fi sanin darajar wahalar da aka yi masa aka yi masa aurenta babu ko kobonsa”.
Nani kuma ta ce, “A’a za ta sa uban kasa ya shiga maganar, idan Abdulrasheed ya kasa.