Sashe 7
Zama Da Madaukin Kanwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Anaam...... Wannan kuma fa? Rashin kunyar taka har ya kai haka?"
"mommy itace fa babe din da nace miki ina son zan aura kiyi min aure kika ki....."
"ke.... Tashi ki fita, kar na sake ganin kafarki acikin gidan nan..... Marar tarbiyya, marar mutunci,wadda bata san ciwon kanta ba, a hakan kake so in barka ka auri wannan abar? Ke tashi ki fita....."
Fuuhhhh Najla ta tashi Anaam na riketa amma ta fusge ta wuce cikin bedroom dinsa ta janyo trolley dinta tazo ta fita,
" haba mommy... Yanzu da kika koreta ina zata je da wannan daren? "
" koma ina ne taje, sannan kai kuma ina son ka sani daga yau sai yau duk ranar da ka sake yarda ka kuskura ka kawo min wata ballagaza gidan nan wallahi sai naci mutuncinka..... Shashasha wanda bai san ciwon kansa ba.... " daga haka mommy din ta juya ta fita, shima cikin sauri ya tashi ya fita domin bin bayan Najla............ ✍🏻
Ku garzayo kar ayi babu ku domin samun labaranmu guda biyu wadanda zasu nishadantar daku kuma su ɗebe muku kewa,
FARAR TASKA (600) tare da alƙalamin FATYMA XARAH
ZAMA DA MAƊAUKIN KANWA (600) daga alƙalamin UMMI A'ISHA
Dukka wadannan Labaran guda biyu zaku samesu kan naira ɗari shida shida, ga mai bukatar biya sai ya tura kudinsa ta 7044644433 Aisha Ibrahim Moniepoint micro finance bank sai a tura evidence of payment ta wannan no 07044644433 ko kuma recharge card na mtn ta wannan no 08169334980 da shaidar biya.
*_Ummi Shatu_*👌🏻
[8/6, 9:30 AM] Baby Aysher: https://chat.whatsapp.com/ER26gPFC7iT6v26Jyz8hCt?mode=ac_t
©️Love story 2025
*ZAMA DA MAƊAUKIN KANWA...!*
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
*6*
***Duk irin rarrashi da ban bakin da Anaam ke yiwa Najla bata saurare shi ba har suka je hotel inda suka saba zama, zama yayi gefen ta inda ta juya masa baya tana jin kamar ta rufe shi da duka ko zata samu ta huce daga haushin abinda mommynsa tayi mata, ta yaya zata farfada mata wadannan maganganun kuma ta kirata da sunaye kala kala marassa kyau dan kawai taje dakin shi ta zauna?
"baby..... Please here me out at least baby....."
"wai mai kake so in ji daga gareka? A gabanka fa komai ya faru Anaam, ashe ni duk zamana da kai bata lokaci na nake yi? How could I be so foolish...... For all this time I been wasting my time....." ta fada idanuwan ta na cika da kwalla,
"am very sorry baby, you know i love you right? Kiyi hakuri ki kyale maganar mommy, kawai bacin rai ne but I promise you she will come around.... Zata so ki kuma zata kaunaceki....."
Shuru tayi masa bata tanka ba saboda bata da abin cewa sai dai amma tana jin dadin kalamansa.
Rai a ɓace mommy ta koma part dinta tana kokarin shiga bedroom dinta Imaan na shirin fitowa, saurin matsawa Imaan din tayi mommy ta shiga ciki ba tare da tayi magana ba, shuru ta zauna ta gagara bacci sai faman tunane tunanen da basa karewa take ta faman yi a haka har asubah tayi gari ya waye, sam bata da niyyar fita ko falo dan gaba daya ta gaji da komai bata son ganin kowa bare magana,
Imaan tun bayan da ta tashi take ta faman aikace aikacenta har tayi ta gama bata ji motsin mommy ba bare taga fitowar ta, breakfast din mommy din ta shirya kan tray ta bita dashi cikin bedroom inda mommy ke zaune idanuwanta biyu amma ta tafi duniyar tunani,
"mommy ina kwana....."
Sai lokacin ta san cewa Imaan ta shigo cikin ɗakin, cikin sanyin murya ta amsawa Imaan gaisuwar,
"mommy breakfast dinki ne na kawo miki tunda naga baki fito ba, kici ki sha maganin ki....."
Girgiza kai mommy tayi cike da takaici tace "a wanne dalili zan sha magani Imaan?"
"mommy dan lafiyarki mana...."
Sake girgiza kai mommy tayi ta kalleta "bani da bukatar shan wani magani a halin yanzu Imaan, ai ina shan maganin ne dan in samu lafiya kuma in rayu ko? To na gaji da rayuwar gara in koma ga Mahalicci na ta yuyu acan in samu hutu....."
"innalillahi haba mommy.... Da rayuwa da mutuwa ai duk na Allah ne" Imaan ta fada jikin ta na rawa,
"Imaan bana son in cigaba da rayuwa ina kallon wannan bakin cikin da Anaam ke ƙunsa min...... Bin mata? Koda yaushe yana tare da mace...... Abin nashi yanzu har yayi tsananin da zai shigo da mace cikin gidan nan babu kunyar idona? This is very unfortunate........"
"to ai mommy in dai hakane kamata yayi kici ki koshi kisha magani dan ki samu lafiyar da zaki yaƙi wadannan muyagun halayen nasa tunda ke kadai zaki iya tsawatar masa haka kuma ke kadai zaki iya hana shi ya hanu......"
"Imaan na gaji..... Na gaji gaba daya da halayen Anaam....."
"kiyi hakuri mommy.... Muci gaba da yi masa addu'a Insha Allah wata rana sai labari, Insha Allah ba zai dawwama ahaka ba Allah zai ganar dashi gaskiya kuma zai daina duk wadannan abubuwan, zai zamo miki ɗa na gari kuma sanyin idaniya, da yardar Allah sai kinyi dariya kuma sai kinyi alfahari da shi"
Cigaba da bata baki tayi har ta sauko domin cin breakfast din bayan ta umarce ta akan ta dauko nata itama su ci tare, murmushi Imaan tayi ta dauko natan ta zo ta zauna kusa da mommy suka fara karyawa, tana jin mommy tamkar uwar da ta haife ta saboda kyawawan halaye da kuma nagartattun dabi'u irin na mommyn. Tunda Anaam yayi fushi ya bar gidan sai da yayi kwana biyu sannan ya dawo nan mommy ta sake saka shi a gaba tayi masa faɗa tamkar zata doke shi, ransa yayi mutukar baci saboda a gaban Imaan ne shi kuma ya tsani yarinyar nan ya sake kulewa da ita kuma daga ranar bai sake fita ba saboda mommy tace kar ya kuskura ya sake saka ƙafarsa ya fita waje, ya za ayi shi ba mace ba a fara yi masa kulle a hana shi fita? Yana tsaka da wannan haushi da bakin cikin mommy ta kira shi a waya yana kwance ya rasa me yake yi masa dadi wai yazo yanzu yanzun nan,
"Imaan me da me kika ce ana da bukata a kitchen?"
"mommy shinkafarki ta kare, sannan babu wake sai dan kadan, semovita saura leda daya sai kuma sauran abubuwan bukata irin su spices da sauransu....."
"ok babu matsala zaku je yanzu ki siyo duk abinda babu...... Yau Kinga Anaam ya fita kuwa?"
"mommy gaskiya banga fitar shi ba, kuma ina ganin kamar wannan matakin da kika dauka a kansa yayi daidai saboda idan bai fita ba to ba zai hadu da abokai ko sauran yan matan dake zuga shi yana dauko magana ba...."
Shuru tayi sakamakon jiyo kamshinsa da tayi wanda ya gauraye cikin bedroom din cikin kankanin lokaci,
" ke....... Ke...... Ke yar aiki " ta jiyo yana kwala mata kira, babu shiri ta fita, yana zaune falon mommy ya dora kafa daya akan daya fuskar shi a daure,
"gani"
"ke ya sunanki ne? Indo kike ko inna.....?"
"Imaan..."
"whatever, kawo min ruwa mai sanyi...."
Kitchen ta shiga ta dauko masa ruwan ta kawo, kallon sama da kasa yayi mata kafin yace,
"maida wannan ruwan, ɗauko min coke mai sanyi...." Juyawa ta sake yi zuwa kitchen ta mayar da ruwan ta dauko masa Coke din kamar yadda ya bukata ta kawo ta ajiye a gabansa kuma daidai lokacin mommy ta fito daga cikin bedroom dinta,
"Anaam kuje da Imaan zata iyo min cefanen gida......"
Gyara zamansa yayi kafin ya fara magana cikin kunar rai bayan ya ajiye Coke din dake hannunsa,
"mommy yanzu nine zan dauki yar aiki in tafi in kaita kasuwa dan kawai zata iyo cefane? Yanzu mommy kaskancin nawa har ya kai haka? Me su malam bala suke yi da su ba zasu kaita ba ko kuma ta hau taxi amma sai ace ni....."
"saurara, malam bala tun jiya baya nan ko ka ganshi a gidan nan? Ai ba ita zaka yiwa ba ni zaka yiwa saboda abinda zanci zata je ta siyo min...." shuru yayi yana kunkuni sai kace karamin yaro,
"ta fito mu tafi...." daga haka ya tashi ya fice ita dai Imaan duk a tsorace take dashi dan harga Allah ba dan ba zata iya yiwa mommy musu ba da wallahi ba zata yarda ta bishi ba saboda tun tana yar karama take bala'in tsoron yan shaye Shaye kuma ta tsane su ko inda suke zama bata yarda tabi ta hanyar amma yanzu gashi zata fita tare da Anaam, wadatattun kudi mommy ta bata wadanda zasu isa ta siyo duk abubuwan da zata siyo, a cikin motar shi ta hango shi zaune amma yabar kofar a bude bai rufe ba, diriricewa tayi ta rasa ina zata shiga ta zauna gaba ko baya saboda bata son tayi laifi,
"ke zaki shigo ne ko yaya?"
"mommy itace fa babe din da nace miki ina son zan aura kiyi min aure kika ki....."
"ke.... Tashi ki fita, kar na sake ganin kafarki acikin gidan nan..... Marar tarbiyya, marar mutunci,wadda bata san ciwon kanta ba, a hakan kake so in barka ka auri wannan abar? Ke tashi ki fita....."
Fuuhhhh Najla ta tashi Anaam na riketa amma ta fusge ta wuce cikin bedroom dinsa ta janyo trolley dinta tazo ta fita,
" haba mommy... Yanzu da kika koreta ina zata je da wannan daren? "
" koma ina ne taje, sannan kai kuma ina son ka sani daga yau sai yau duk ranar da ka sake yarda ka kuskura ka kawo min wata ballagaza gidan nan wallahi sai naci mutuncinka..... Shashasha wanda bai san ciwon kansa ba.... " daga haka mommy din ta juya ta fita, shima cikin sauri ya tashi ya fita domin bin bayan Najla............ ✍🏻
Ku garzayo kar ayi babu ku domin samun labaranmu guda biyu wadanda zasu nishadantar daku kuma su ɗebe muku kewa,
FARAR TASKA (600) tare da alƙalamin FATYMA XARAH
ZAMA DA MAƊAUKIN KANWA (600) daga alƙalamin UMMI A'ISHA
Dukka wadannan Labaran guda biyu zaku samesu kan naira ɗari shida shida, ga mai bukatar biya sai ya tura kudinsa ta 7044644433 Aisha Ibrahim Moniepoint micro finance bank sai a tura evidence of payment ta wannan no 07044644433 ko kuma recharge card na mtn ta wannan no 08169334980 da shaidar biya.
*_Ummi Shatu_*👌🏻
[8/6, 9:30 AM] Baby Aysher: https://chat.whatsapp.com/ER26gPFC7iT6v26Jyz8hCt?mode=ac_t
©️Love story 2025
*ZAMA DA MAƊAUKIN KANWA...!*
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
*6*
***Duk irin rarrashi da ban bakin da Anaam ke yiwa Najla bata saurare shi ba har suka je hotel inda suka saba zama, zama yayi gefen ta inda ta juya masa baya tana jin kamar ta rufe shi da duka ko zata samu ta huce daga haushin abinda mommynsa tayi mata, ta yaya zata farfada mata wadannan maganganun kuma ta kirata da sunaye kala kala marassa kyau dan kawai taje dakin shi ta zauna?
"baby..... Please here me out at least baby....."
"wai mai kake so in ji daga gareka? A gabanka fa komai ya faru Anaam, ashe ni duk zamana da kai bata lokaci na nake yi? How could I be so foolish...... For all this time I been wasting my time....." ta fada idanuwan ta na cika da kwalla,
"am very sorry baby, you know i love you right? Kiyi hakuri ki kyale maganar mommy, kawai bacin rai ne but I promise you she will come around.... Zata so ki kuma zata kaunaceki....."
Shuru tayi masa bata tanka ba saboda bata da abin cewa sai dai amma tana jin dadin kalamansa.
Rai a ɓace mommy ta koma part dinta tana kokarin shiga bedroom dinta Imaan na shirin fitowa, saurin matsawa Imaan din tayi mommy ta shiga ciki ba tare da tayi magana ba, shuru ta zauna ta gagara bacci sai faman tunane tunanen da basa karewa take ta faman yi a haka har asubah tayi gari ya waye, sam bata da niyyar fita ko falo dan gaba daya ta gaji da komai bata son ganin kowa bare magana,
Imaan tun bayan da ta tashi take ta faman aikace aikacenta har tayi ta gama bata ji motsin mommy ba bare taga fitowar ta, breakfast din mommy din ta shirya kan tray ta bita dashi cikin bedroom inda mommy ke zaune idanuwanta biyu amma ta tafi duniyar tunani,
"mommy ina kwana....."
Sai lokacin ta san cewa Imaan ta shigo cikin ɗakin, cikin sanyin murya ta amsawa Imaan gaisuwar,
"mommy breakfast dinki ne na kawo miki tunda naga baki fito ba, kici ki sha maganin ki....."
Girgiza kai mommy tayi cike da takaici tace "a wanne dalili zan sha magani Imaan?"
"mommy dan lafiyarki mana...."
Sake girgiza kai mommy tayi ta kalleta "bani da bukatar shan wani magani a halin yanzu Imaan, ai ina shan maganin ne dan in samu lafiya kuma in rayu ko? To na gaji da rayuwar gara in koma ga Mahalicci na ta yuyu acan in samu hutu....."
"innalillahi haba mommy.... Da rayuwa da mutuwa ai duk na Allah ne" Imaan ta fada jikin ta na rawa,
"Imaan bana son in cigaba da rayuwa ina kallon wannan bakin cikin da Anaam ke ƙunsa min...... Bin mata? Koda yaushe yana tare da mace...... Abin nashi yanzu har yayi tsananin da zai shigo da mace cikin gidan nan babu kunyar idona? This is very unfortunate........"
"to ai mommy in dai hakane kamata yayi kici ki koshi kisha magani dan ki samu lafiyar da zaki yaƙi wadannan muyagun halayen nasa tunda ke kadai zaki iya tsawatar masa haka kuma ke kadai zaki iya hana shi ya hanu......"
"Imaan na gaji..... Na gaji gaba daya da halayen Anaam....."
"kiyi hakuri mommy.... Muci gaba da yi masa addu'a Insha Allah wata rana sai labari, Insha Allah ba zai dawwama ahaka ba Allah zai ganar dashi gaskiya kuma zai daina duk wadannan abubuwan, zai zamo miki ɗa na gari kuma sanyin idaniya, da yardar Allah sai kinyi dariya kuma sai kinyi alfahari da shi"
Cigaba da bata baki tayi har ta sauko domin cin breakfast din bayan ta umarce ta akan ta dauko nata itama su ci tare, murmushi Imaan tayi ta dauko natan ta zo ta zauna kusa da mommy suka fara karyawa, tana jin mommy tamkar uwar da ta haife ta saboda kyawawan halaye da kuma nagartattun dabi'u irin na mommyn. Tunda Anaam yayi fushi ya bar gidan sai da yayi kwana biyu sannan ya dawo nan mommy ta sake saka shi a gaba tayi masa faɗa tamkar zata doke shi, ransa yayi mutukar baci saboda a gaban Imaan ne shi kuma ya tsani yarinyar nan ya sake kulewa da ita kuma daga ranar bai sake fita ba saboda mommy tace kar ya kuskura ya sake saka ƙafarsa ya fita waje, ya za ayi shi ba mace ba a fara yi masa kulle a hana shi fita? Yana tsaka da wannan haushi da bakin cikin mommy ta kira shi a waya yana kwance ya rasa me yake yi masa dadi wai yazo yanzu yanzun nan,
"Imaan me da me kika ce ana da bukata a kitchen?"
"mommy shinkafarki ta kare, sannan babu wake sai dan kadan, semovita saura leda daya sai kuma sauran abubuwan bukata irin su spices da sauransu....."
"ok babu matsala zaku je yanzu ki siyo duk abinda babu...... Yau Kinga Anaam ya fita kuwa?"
"mommy gaskiya banga fitar shi ba, kuma ina ganin kamar wannan matakin da kika dauka a kansa yayi daidai saboda idan bai fita ba to ba zai hadu da abokai ko sauran yan matan dake zuga shi yana dauko magana ba...."
Shuru tayi sakamakon jiyo kamshinsa da tayi wanda ya gauraye cikin bedroom din cikin kankanin lokaci,
" ke....... Ke...... Ke yar aiki " ta jiyo yana kwala mata kira, babu shiri ta fita, yana zaune falon mommy ya dora kafa daya akan daya fuskar shi a daure,
"gani"
"ke ya sunanki ne? Indo kike ko inna.....?"
"Imaan..."
"whatever, kawo min ruwa mai sanyi...."
Kitchen ta shiga ta dauko masa ruwan ta kawo, kallon sama da kasa yayi mata kafin yace,
"maida wannan ruwan, ɗauko min coke mai sanyi...." Juyawa ta sake yi zuwa kitchen ta mayar da ruwan ta dauko masa Coke din kamar yadda ya bukata ta kawo ta ajiye a gabansa kuma daidai lokacin mommy ta fito daga cikin bedroom dinta,
"Anaam kuje da Imaan zata iyo min cefanen gida......"
Gyara zamansa yayi kafin ya fara magana cikin kunar rai bayan ya ajiye Coke din dake hannunsa,
"mommy yanzu nine zan dauki yar aiki in tafi in kaita kasuwa dan kawai zata iyo cefane? Yanzu mommy kaskancin nawa har ya kai haka? Me su malam bala suke yi da su ba zasu kaita ba ko kuma ta hau taxi amma sai ace ni....."
"saurara, malam bala tun jiya baya nan ko ka ganshi a gidan nan? Ai ba ita zaka yiwa ba ni zaka yiwa saboda abinda zanci zata je ta siyo min...." shuru yayi yana kunkuni sai kace karamin yaro,
"ta fito mu tafi...." daga haka ya tashi ya fice ita dai Imaan duk a tsorace take dashi dan harga Allah ba dan ba zata iya yiwa mommy musu ba da wallahi ba zata yarda ta bishi ba saboda tun tana yar karama take bala'in tsoron yan shaye Shaye kuma ta tsane su ko inda suke zama bata yarda tabi ta hanyar amma yanzu gashi zata fita tare da Anaam, wadatattun kudi mommy ta bata wadanda zasu isa ta siyo duk abubuwan da zata siyo, a cikin motar shi ta hango shi zaune amma yabar kofar a bude bai rufe ba, diriricewa tayi ta rasa ina zata shiga ta zauna gaba ko baya saboda bata son tayi laifi,
"ke zaki shigo ne ko yaya?"