Sashe 13
Zama Da Madaukin Kanwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"Ubangiji Allah ya jikan Hajiya Batool yayi mata rahama, halin ta na gari ya bita, Allah ya yafe mata ya bata aljanna madaukakiya, hakika ita din ta kasance mace ta kwarai kuma ta gari mai son mutane da kuma son zumunci, wannan takardar ta bani ita watannin baya lokacin da zata yi wata tafiya zuwa Kasar chairo domin duba lafiyarta sannan kuma ta umarceni da duk lokacin da ta Allah ya kasance idan har ta rigani rasuwa to inzo in tara ku kai Anaam da kuma ke Imaan domin in isar muku da wani saƙo ko kuma ince wasiyya kamar yadda ta rubuta gashi da hannunta sannan kuma taje har gidana ƙafa da ƙafa ta bani ta kuma barmin wasinci na in daure in isar da wannan sako zuwa gareku tun kafin ta cika kwana 40 da komawa ga Mahaliccinta...... "
Daga Imaan din har Anaam kowannensu ya ƙosa yaji kowanne irin wasiyya mommy ta bari kuma, sannan me yasa ta zabi sai iya su biyu za a sanarwa da wasiyyar bayan ita Imaan matsayin hadima take gareta, duka tunaninsu ne ya katse saboda jin Alhaji nura yaci gaba da kora jawabinsa kamar haka,
"kamar yadda muka sani ita wasiyya wajibi ne a cika ta matsawar mamaci ya rubuta ko kuma ya fada da bakinsa, to ita dinma ta fada da baki ta sanar min sannan kuma saboda gudun samun zargi ko kuma kaucewa jita jita shiyasa ta rubuta ta da hannunta kamar yadda kuke gani, kafin hajiya ta rasu ta taba samuna da wata magana wacce ta sakani cikin fargaba da kuma rudani domin tace min idan har Allah yasa ta rigani rasuwa to inzo in isar da wannan sako kamar haka, duka dukiyar da ta ta bari a duniya wadda ta mallaka kama tun daga kan gidaje, filaye, company, motoci da duk wani abu wanda yake mallakinta ta mallaka muku ku biyu wato kai Anaam da kuma ke Imaan amma kuma bisa wani sharadi guda daya....... "
Daga Imaan har Anaam kowanne maganar ta bashi mamaki to ita kuma Imaan a gayyar wa da har mommy zata bata rabin dukiyarta?
" Sharadin shine..... Za a daura muku aure cikin nan da sati biyu sai a baku dukiyarku gaba daya sannan babu saki duk rintsi zaku rayu tare....."
Wadannan kalaman nasa sune suka sake jefa su cikin mamaki da al'ajabi, "aure kuma?" Anaam ya bukata batare da yasan ma lokacin da yayi tambayar ba,
"tabbas.... Kwarai da gaske aure ta bada wasiyyar a daura muku koda kuwa bakwa son juna........"
"Innalillahi wa inna ilaihir rajiun......." shine kawai abinda Imaan ke maimaitawa cikin ranta saboda ita dai duk duniya idan akwai mutumin da bata kauna to Anaam ne amma kuma sai gashi ana maganar mommy tabar wasiyyar su rayu tare har karshen rayuwarsu ita kuwa mommy saboda me? Me yayi zafi da har zata bar wannan wasiyyar mai mutukar wahala bayan ta san yana da wacce yake son zai aura itama take sonshi sannan banda wannan ma ita sam baiyi mata ba a matsayin mijin da zata aura saboda ba irin shi take so ba sam bai yi ko kama da irin namijin da take so ba domin ita nagartaccen namiji take so ba sangartacce ba sannan hali take nema ba kyale kyalen duniya ba haka kuma kamili take nema komai muninsa ba wanda yayi kyan dan maciji ba, tafi son miji na gari ɗan gaske wanda zata ƙaru dashi ta kowanne fanni wanda zai so ta ya nuna mata ƙauna ako ina, wanda yasan farillai da sunnonin aure wanda zai kare mata mutuncinta ya tsare mata kansa wanda zai sauke duk wani nauyi nata wanda ya rataya a wuyan sa, shi dai Anaam shuru yayi yana nazari dan gaba daya ya rasa me ma zai ce aure? Kuma auren ma da wannan kidahumar marar wayewa, yar aiki wadda ba kowan kowa ba kuma ba yar kowa ba, inaah ai ba zata taba sabuwa ba wai bindiga a ruwa, idan sama da kasa zata hade ba zai taba auren wannan kaskantacciyar yarinyar ba,
"haba mommy..... Why?? Why? Why??" shine abinda yake ta sakawa yana fada a cikin ransa amma a fili yarasa da wacce kalma ko da wanne yare zai yi amfani wurin nunawa Alhaji nura sam wannan maganar da ya zo da ita bazai amince da ita ba,
"Dan haka idan Allah ya nuna mana sati mai zuwa za a daura muku aure amma kuma ku tuna babu maganar saki ko rabuwa bayan anyi muku aure domin wannan shine wasiyyar mahaifiyarka....."
Dafe kansa yayi da dukkanin hannayensa guda biyu wanda ke barazanar fashewa, wannan wacce irin masifa ce kuma? Wannan wanne irin bala'i ne yake shirin faruwa dashi yanzu duk duniya mommy ta rasa wadda zata bar wasiyyar a daura masa aure da ita sai ƴar aikin gidan su? Boyi boyi marar gata yarinyar da ko asalin ta basu sani ba, yanzu shi da wanne idon zai kalli duniya ya nuna musu wannan bagidajiyar yarinyar da har yanzu babu alamar wayewa a tare da ita? Yar aiki?,
"am... Am.... Am nace dama..... Idan ban amince da maganar auren ba akwai wata matsala ne?" ya tambayi Alhaji Nura zuciyarsa na bugawa tara tara tamkar zata fashe dan fargaba da tashin hankali,
"ehh gaskiya akwai dan hajiya tace idan har baka amince ba to a raba dukiyarta gida biyu daya akai gidan marayu daya kuma a zuba cikin gidauniyar da ta bude ta marayu da gajiyayyu.... Gashi dai karanta da kanka ka gani..... Have it..."
Karɓa yayi hannunsa yana rawa ya soma karanta wasiyyar mommy wadda gashi nan da hannunta ta rubuta ba wai wani ne ya rubuta mata ba saboda ga rubutun ta nan rangadadau kamar yanzu ne tayi shi da kuma sa hannunta, ɗago kan shi yayi idanuwansa jajur bayan ya gama karanta wasiyyar mommy........
Tirƙashi wannan shine ga ƙoshi ga kwanan yunwa, shin ya zata kasance? Anaam zai yarda da wannan auren? Idan har anyi auren wacce waina za a toya a gidan auren nasa? Shin Najla zata bari auren nasa ya tabbata? Ƙiyayya da Ƙiyayya basa taɓa haduwa har su zauna inuwa ɗaya, Amsoshin wadannan tambayoyi da ma wadanda ba a san su ba suna cikin cigaban labarin wanda zaku sameshi kan naira dari shida 600 kacal, kar ku bari ayi babu ku sannan kar ku bari a baku labari,Ku garzayo kar ayi babu ku domin samun labaranmu guda biyu wadanda zasu nishadantar daku kuma su ɗebe muku kewa,
FARAR TASKA (600) tare da alƙalamin FATYMA XARAH
ZAMA DA MAƊAUKIN KANWA (600) daga alƙalamin UMMI A'ISHA
Dukka wadannan Labaran guda biyu zaku samesu kan naira ɗari shida shida, ga mai bukatar biya sai ya tura kudinsa ta 7044644433 Aisha Ibrahim Moniepoint micro finance bank sai a tura evidence of payment ta wannan no 07044644433 ko kuma recharge card na mtn ta wannan no 08169334980 da shaidar biya.
*_Ummi Shatu_*👌🏻
Daga Imaan din har Anaam kowannensu ya ƙosa yaji kowanne irin wasiyya mommy ta bari kuma, sannan me yasa ta zabi sai iya su biyu za a sanarwa da wasiyyar bayan ita Imaan matsayin hadima take gareta, duka tunaninsu ne ya katse saboda jin Alhaji nura yaci gaba da kora jawabinsa kamar haka,
"kamar yadda muka sani ita wasiyya wajibi ne a cika ta matsawar mamaci ya rubuta ko kuma ya fada da bakinsa, to ita dinma ta fada da baki ta sanar min sannan kuma saboda gudun samun zargi ko kuma kaucewa jita jita shiyasa ta rubuta ta da hannunta kamar yadda kuke gani, kafin hajiya ta rasu ta taba samuna da wata magana wacce ta sakani cikin fargaba da kuma rudani domin tace min idan har Allah yasa ta rigani rasuwa to inzo in isar da wannan sako kamar haka, duka dukiyar da ta ta bari a duniya wadda ta mallaka kama tun daga kan gidaje, filaye, company, motoci da duk wani abu wanda yake mallakinta ta mallaka muku ku biyu wato kai Anaam da kuma ke Imaan amma kuma bisa wani sharadi guda daya....... "
Daga Imaan har Anaam kowanne maganar ta bashi mamaki to ita kuma Imaan a gayyar wa da har mommy zata bata rabin dukiyarta?
" Sharadin shine..... Za a daura muku aure cikin nan da sati biyu sai a baku dukiyarku gaba daya sannan babu saki duk rintsi zaku rayu tare....."
Wadannan kalaman nasa sune suka sake jefa su cikin mamaki da al'ajabi, "aure kuma?" Anaam ya bukata batare da yasan ma lokacin da yayi tambayar ba,
"tabbas.... Kwarai da gaske aure ta bada wasiyyar a daura muku koda kuwa bakwa son juna........"
"Innalillahi wa inna ilaihir rajiun......." shine kawai abinda Imaan ke maimaitawa cikin ranta saboda ita dai duk duniya idan akwai mutumin da bata kauna to Anaam ne amma kuma sai gashi ana maganar mommy tabar wasiyyar su rayu tare har karshen rayuwarsu ita kuwa mommy saboda me? Me yayi zafi da har zata bar wannan wasiyyar mai mutukar wahala bayan ta san yana da wacce yake son zai aura itama take sonshi sannan banda wannan ma ita sam baiyi mata ba a matsayin mijin da zata aura saboda ba irin shi take so ba sam bai yi ko kama da irin namijin da take so ba domin ita nagartaccen namiji take so ba sangartacce ba sannan hali take nema ba kyale kyalen duniya ba haka kuma kamili take nema komai muninsa ba wanda yayi kyan dan maciji ba, tafi son miji na gari ɗan gaske wanda zata ƙaru dashi ta kowanne fanni wanda zai so ta ya nuna mata ƙauna ako ina, wanda yasan farillai da sunnonin aure wanda zai kare mata mutuncinta ya tsare mata kansa wanda zai sauke duk wani nauyi nata wanda ya rataya a wuyan sa, shi dai Anaam shuru yayi yana nazari dan gaba daya ya rasa me ma zai ce aure? Kuma auren ma da wannan kidahumar marar wayewa, yar aiki wadda ba kowan kowa ba kuma ba yar kowa ba, inaah ai ba zata taba sabuwa ba wai bindiga a ruwa, idan sama da kasa zata hade ba zai taba auren wannan kaskantacciyar yarinyar ba,
"haba mommy..... Why?? Why? Why??" shine abinda yake ta sakawa yana fada a cikin ransa amma a fili yarasa da wacce kalma ko da wanne yare zai yi amfani wurin nunawa Alhaji nura sam wannan maganar da ya zo da ita bazai amince da ita ba,
"Dan haka idan Allah ya nuna mana sati mai zuwa za a daura muku aure amma kuma ku tuna babu maganar saki ko rabuwa bayan anyi muku aure domin wannan shine wasiyyar mahaifiyarka....."
Dafe kansa yayi da dukkanin hannayensa guda biyu wanda ke barazanar fashewa, wannan wacce irin masifa ce kuma? Wannan wanne irin bala'i ne yake shirin faruwa dashi yanzu duk duniya mommy ta rasa wadda zata bar wasiyyar a daura masa aure da ita sai ƴar aikin gidan su? Boyi boyi marar gata yarinyar da ko asalin ta basu sani ba, yanzu shi da wanne idon zai kalli duniya ya nuna musu wannan bagidajiyar yarinyar da har yanzu babu alamar wayewa a tare da ita? Yar aiki?,
"am... Am.... Am nace dama..... Idan ban amince da maganar auren ba akwai wata matsala ne?" ya tambayi Alhaji Nura zuciyarsa na bugawa tara tara tamkar zata fashe dan fargaba da tashin hankali,
"ehh gaskiya akwai dan hajiya tace idan har baka amince ba to a raba dukiyarta gida biyu daya akai gidan marayu daya kuma a zuba cikin gidauniyar da ta bude ta marayu da gajiyayyu.... Gashi dai karanta da kanka ka gani..... Have it..."
Karɓa yayi hannunsa yana rawa ya soma karanta wasiyyar mommy wadda gashi nan da hannunta ta rubuta ba wai wani ne ya rubuta mata ba saboda ga rubutun ta nan rangadadau kamar yanzu ne tayi shi da kuma sa hannunta, ɗago kan shi yayi idanuwansa jajur bayan ya gama karanta wasiyyar mommy........
Tirƙashi wannan shine ga ƙoshi ga kwanan yunwa, shin ya zata kasance? Anaam zai yarda da wannan auren? Idan har anyi auren wacce waina za a toya a gidan auren nasa? Shin Najla zata bari auren nasa ya tabbata? Ƙiyayya da Ƙiyayya basa taɓa haduwa har su zauna inuwa ɗaya, Amsoshin wadannan tambayoyi da ma wadanda ba a san su ba suna cikin cigaban labarin wanda zaku sameshi kan naira dari shida 600 kacal, kar ku bari ayi babu ku sannan kar ku bari a baku labari,Ku garzayo kar ayi babu ku domin samun labaranmu guda biyu wadanda zasu nishadantar daku kuma su ɗebe muku kewa,
FARAR TASKA (600) tare da alƙalamin FATYMA XARAH
ZAMA DA MAƊAUKIN KANWA (600) daga alƙalamin UMMI A'ISHA
Dukka wadannan Labaran guda biyu zaku samesu kan naira ɗari shida shida, ga mai bukatar biya sai ya tura kudinsa ta 7044644433 Aisha Ibrahim Moniepoint micro finance bank sai a tura evidence of payment ta wannan no 07044644433 ko kuma recharge card na mtn ta wannan no 08169334980 da shaidar biya.
*_Ummi Shatu_*👌🏻