Sashe 9
Zabin Mahaifiyata Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read
A'UZUBILLAHI. Abinda na furta kenan, dama su 'yan lesbian ne? A guje na juya na bar musu d'akin ina nema musu shiriya,
Bayan sun gama watsewar su, lina ta fito ta tafi tana jaddadawa humaira akan tasan yanda zatayi ta bata maganin taci
MENENE DANGANTAKAR LINA DA HUMAIRA???
Humaira sun had'u da lina ne a wajen party, asalin lina bayarbiya ce amma ba musulma ba ce.
tun tashin lina yarinya ce hatsabibiya tun wana k'aramar ta take bin maza, data girma ta zama budurwa ne idanunta suka dad'a bud'ewa, daga k'arshe tattarawa tayi tabar garinsu OYO ta biyo saurayinta suka zo BAUCHI.
Tunda tazo ta bud'e bariki kala-kala ba iya bin maza ta tsaya ba, hatta hajiyoyi d'aukanta sukeyi
sun had'u da humaira ne a wajen birthday partyn da saurayinta ya had'a mata, tun daga lokacin suka k'ulla k'awance, ita ta koyama humaira lesbian da bin bokaye,(ALLAh ka had'amu da k'awaye nagari AMEENðŸ™ðŸ™)
Da daddare bayan A.A ya dawo yana zaune a falo, humaira ta fito cikin shigar riga da skert english wears, sun kamata se dai ko kadan basuyi mata kyauba, kasancewarta siririyar mace da bata da shape ko kad'an, se tayi kamar an d'aura wa muciya zani.😜😜
Kusa dashi tazo ta zauna tana mishi barka da dawowa kamar ba abinda ya faru(duk plan d'in lina ne). Ya amsa mata cikin jin dad'i, saboda shima fargaba ce ta hana shi dawowa gidan tun da ya fita da safe.
tace mishi su tashi suje suci abinci, wanda me aikinta blessing ta girka ta jera akan dining table. mik'ewa yayi suka nufi kan dining d'in, bayan sun kammala cin abincin suka dawo falon suka ci gaba da hiransu suna kallo kamar yanda suka saba.
Humaira ne ta dubi A.A tace babyna daman akwai maganar da nake son muyi dakai, ina jinki ya amsa mata ba tare daya kalle ta ba.('yan mulkin sun juyo kanta kenan).
Naga har yanzu baka kirata ka fada mata yanda tsarin gidan nan yake ba. Kallonta yayi sannan yace wani tsari kenan??? had'e rai tayi tace ina so ne ka fad'a mata duk wacce take da girki ta fito a dinga cin abinci tare da ita, ban yarda kowa ta dinga yin nata ba.
kauda kanshi yayi cikin jinkai yace kije ki kirata, tashi humaira tayi ta nufi part d'in salma.
k'wank'wasa k'ofar tayi, salma dake zaune tana kallon tashar Arewa 24 ta taso ta bud'e k'ofar, tana ganin humaira ta b'ata fuska tace lafiya?
murmushin mugunta humaira tayi, tace "kizo mijina yana kiranki" ta juya tayi tafiyarta. d'an tsaki salma taja tace da wayace ba mijinki bane? (ina fatan salma ba haushi kikaji ba😃😃) juyawa tayi ta Koma cikin daki ta dad'a gyara fuskarta ta fesa turare me dad'in k'amshi, ko hijab bata d'auka ba ta nufi falon da suke.
Tunda ta doso wajen yake binta da kallo, kasancewar kayan baccine a jikinta riga da wando cotton, sun kamata tsam rigan me hannun shimi ne, wandon a iya guiwa ya tsaya mata, ta saka hulan turban kalan kayan pink.
tana zuwa ta nemi waje ta zauna ba tare data ce musu komai ba, humaira da tun fitowar salma tayi dana sanin kiranta da tace ayi ganin irin kallon da A.A yake mata. Gashi ba daman tayi magana kar plan d'inta yargaje🤣🤣🤣🤣
Ta wurga ma salma harara sannan ta juya ta kalli A.A daya maida hankalinsa ga kallon t.v ta daure tace "babyna gatanan ta fito ka fad'a mata" beko kalle ta ba yace ki fad'a mata mana tunda tsarinki ne hakan.
Da sauri ta dube shi jin tana mishi magana yana bata amsa wani iri. wai meke faruwa ne kodai asirin da namishi ya fara warwarewa ne? daga zuwan ta komai ya fara warware wa, aikuwa zanyi saurin aikata lahira tun kafin komai ya kmab'e min, tayi maganar cikin zuciyarta.
duban salma tayi dakanta yake kallon wani gefe na falon tace "to amarya dama maganar girki ne, kinsan hajiya tace yayi miki kwana 7 d'inki kafin araba kwana bibbiyu. saboda haka yanzu duk wacce take da girki zata fito a had'u a dinga cin abinci tare. Akwai wacce take yi mana girki, ina fatan ba matsala?" ta k'arasa tana murmushin yak'e
mamaki ne ya kama salma,tabbas akwai abinda take shiryawa dan tasan ruma baya tsami banza, ita zata nuna ma kirsa? wato dan tana gaban mijinta shine zata nuna ita na ALLAh ne, aikuma zata nuna mata itama macece tana da irin nata salon.
Murmushi salma tayi tace "haba Aunty ai duk abinda kika yanke dai-dai ne, amma ni inso samune nafison na dinga yima mijina abinci, dan banason masu aiki su dinga yima mijina hidima.....
Tun kan salma ta k'arasa humaira tayi saurin katseta, ganin tana neman wargaza mata plan. tace"haba k'anwata kamar ke kina auren Alh. A.A me dala ace kina girki da kanki. ai wannan abin kunya ne a gare mu.
girgiza kai salma tayi tace ba abin kunya bane Aunty tunda aikin ladane kuma wa mijina zan yima, ni inaga ai ba lefi aciki.
A.A da yake kallon news a t.v amma hankalinsa yana wajensu,yana jin maganganun da sukeyi, ya juyo ya kalli humaira yace "tunda tace zata iya ki rabu da ita mana, kun cika min kunne da surutunku, kun hana na fahimci abinda ake fad'a a news d'in. Yana maganar yana satan kallon salma da take jifansa da murmushi duk dan ta k'ular da humaira.
humaira da ranta ya gama b'aci ta kalle shi ta fara magana ta ma manta da batun wani plan tace "wallahi duk abinda na tsara shi za'abi, koka manta haka akeyi aduk lokacin da kayi aure? kaine ka bani damar tsara duk yanda nake so dan haka yanzuma haka nake buk'atar ayi.
kallonta salma tayi tana murmushi tace "Aunty menene abin d'aga hankali anan? kawai dan zan dinga yima mijina hidima ai ba wani abu bane....
Keeeï¼... Badake nake yiba da wanda ya ajiyeki nake magana. humaira ta fad'a tana huci kamar kububuwa
Look humaira kinsan fa ban cika son hayaniya ba, please kowa ta tafi d'akinta banson tashin hankali.
Mik'ewa salma tayi fuskarta cike da murmushi ta wuce d'akinta. itama humaira tashi tayi ta dube shi tace, "Abdul nika wulak'anta a gaban wancan banzan ko? to wallahi se nayi maganinku daga kai har ita. ta wuce shi ta shige d'aki"
Tsaki yaja ya kashe kallon ya nufi d'akin salma, hakanan yake jin ya rage tsoron humaira yana ganin yanzu bazai d'auki rashin mutuncin ta ba.
kuyi hakuri da wannan wallahi har nayi ya goge.
Readers naji k'orafin ku zan dingayi kullum insha ALLAhu, wanda ba'abi ra'ayin ku ba ina me baku hak'uri.
🌳🌳UMMU AFFAN🌳🌳
[1:36PM, 2/7/2018] ‪+234 808 677 7945‬: 🌳🌳🌳🌳🌳
ZAB'IN MAHAIFINA
🌳🌳🌳🌳🌳
Written by SADIYA ALHASSAN (Ummu Affan)
ðŸŒHAJOW ðŸ“ðŸŒ
ðŸŒðŸ‘©â€ðŸ‘§â€ðŸ‘§ðŸ‘©â€ðŸ‘§â€ðŸ‘§ðŸ‘©â€ðŸ‘§â€ðŸ‘§HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS âœðŸ¾âœðŸ¾âœðŸ¾ðŸŒ
Dedicated to PRINCESS ESHAT AYSM
AYSHA BICHIKI
Page 21
Sistr eyshert Aysm ina miki murna da fara sabon novel d'inki (WAZAN SO) ALLAh ya k'ara d'aukaka,yanda kika fara lafiya ALLAh yasa ki gama lafiya. Inayin ki sistr irin sosai d'innan.😘
Akashe ya samu wutan falon amma yana iya hango d'an haske ta cikin bedroom d'in. Sallama yayi sannan ya shiga d'akin a kwance ya sameta ta bama k'ofar baya, tayi nisa a tunani da alama batasan mutum ya shigo d'akin ba.
Gefenta yaje ya kwanta ya juya mata baya,sannan yaja bargo ya lullube jikinsa. ya kashe bedsite lamp dake gefenshi, se a lokacin salma tasan ya shigo d'akin. Cikin sauri ta mik'e zaune ta ce mallam lafiya zaka shigo min d'aki ba ko sallama,
Ko juyowa beyiba bare ya nuna yasan tana magana. duk da haka batayi shiru ba, gaskiya ka tashi ka koma d'ayan d'akin dan ni bansa ba kwana da wani namiji a cikin d'aki d'aya ba.
Batare daya juyo ba ya fara magana "Nan gidana ne ina da ikon shiga duk inda naso a kowani lokaci, kuma ya kamata kisan banbancin dake tsakanin da da kuma yanzu, ki iya bakinki saboda yanzu a k'ark'ashin iko na kike, ba k'ark'ashin ikon iyayenki ba. Agidana kike ba gidanku naje ba.
Shiru salma tayi batare da ta sake cewa komai ba ta mik'e domin ta koma d'ayan d'akin. Muryar shi taji yana bata umurni koma ki kwanta, dan ni bana raba makwanci da matata ki kiyaye ko saboda gaba, komawa salma tayi ta kwanta amma ta gagara runtsawa saboda fargaba da rashin sabo, ga sanyi da takeji.
Shima ba baccin yakeyi ba, tunani ne ya cika kwakwalwar sa, ya rasa me yake damunsa ga wani feeling dayake ji wanda be tab'a jin irinsa akan wata 'ya mace ba.
Sauk'ar numfashinta yaji abayansa alamar bacci ya d'auketa, juyowa yayi yana kallonta tana baccinta cikin kwanciyar hankali, ta dunk'ule jikinta waje d'aya. Tsintar kansa yayi da rungumota zuwa jikin sa, a tare suka sauk'e ajiyar zuciya, itakam cikin bacci ne ba tare datasani ba, yayin dashi kuma najin dad'in jinta dayayi ajikinsa ne.
Kallonta yakeyi be tab'a sanin tana da kyau sosai haka ba, tayi mishi kyau datake bacci, sleeping beauty ya furta a hankali.
Jawo bargon yayi ya lullub'a musu gaba d'aya, yayi addua ya shafa musu. abinda ya juma beyi ba wato addu'an kwanciya.
Cikin dare salma ta farka tajita a jikin mutum, hannu takai ta kunna lamp d'in dake gepenta, zuba mishi ido tayi tana kallon fuskarshi ga kwantaccen sajen shi wanda ya kwanta a fuskar shi, ya k'arama fuskar shi kyau da kamala gaskiya ta yarda Abdul me kyau ne.
Hannun shi ta kalla wanda ya zagayeta dashi tunani takeyi ta yanda zata cire hannun batare data tashe shi, gashi so take yi ta tashi ta d'auro alwala tayi sallan nafila.
A hankali ta zare jikinta a cikin nashi ta nufi toilet domin ta d'auro alwala, k'aran bud'e kofar toilet d'inne ya tashe shi. Yana kallonta ta cikin hasken dayake d'akin, ta fito ta d'auki hijab d'inta ta tada kabbara.
Raka'a hud'u tayi tadad'e a sujjadarta ta k'arshe tana kaima ALLAh kukanta kafin ta d'ago ta sallame.
Bayan sun gama watsewar su, lina ta fito ta tafi tana jaddadawa humaira akan tasan yanda zatayi ta bata maganin taci
MENENE DANGANTAKAR LINA DA HUMAIRA???
Humaira sun had'u da lina ne a wajen party, asalin lina bayarbiya ce amma ba musulma ba ce.
tun tashin lina yarinya ce hatsabibiya tun wana k'aramar ta take bin maza, data girma ta zama budurwa ne idanunta suka dad'a bud'ewa, daga k'arshe tattarawa tayi tabar garinsu OYO ta biyo saurayinta suka zo BAUCHI.
Tunda tazo ta bud'e bariki kala-kala ba iya bin maza ta tsaya ba, hatta hajiyoyi d'aukanta sukeyi
sun had'u da humaira ne a wajen birthday partyn da saurayinta ya had'a mata, tun daga lokacin suka k'ulla k'awance, ita ta koyama humaira lesbian da bin bokaye,(ALLAh ka had'amu da k'awaye nagari AMEENðŸ™ðŸ™)
Da daddare bayan A.A ya dawo yana zaune a falo, humaira ta fito cikin shigar riga da skert english wears, sun kamata se dai ko kadan basuyi mata kyauba, kasancewarta siririyar mace da bata da shape ko kad'an, se tayi kamar an d'aura wa muciya zani.😜😜
Kusa dashi tazo ta zauna tana mishi barka da dawowa kamar ba abinda ya faru(duk plan d'in lina ne). Ya amsa mata cikin jin dad'i, saboda shima fargaba ce ta hana shi dawowa gidan tun da ya fita da safe.
tace mishi su tashi suje suci abinci, wanda me aikinta blessing ta girka ta jera akan dining table. mik'ewa yayi suka nufi kan dining d'in, bayan sun kammala cin abincin suka dawo falon suka ci gaba da hiransu suna kallo kamar yanda suka saba.
Humaira ne ta dubi A.A tace babyna daman akwai maganar da nake son muyi dakai, ina jinki ya amsa mata ba tare daya kalle ta ba.('yan mulkin sun juyo kanta kenan).
Naga har yanzu baka kirata ka fada mata yanda tsarin gidan nan yake ba. Kallonta yayi sannan yace wani tsari kenan??? had'e rai tayi tace ina so ne ka fad'a mata duk wacce take da girki ta fito a dinga cin abinci tare da ita, ban yarda kowa ta dinga yin nata ba.
kauda kanshi yayi cikin jinkai yace kije ki kirata, tashi humaira tayi ta nufi part d'in salma.
k'wank'wasa k'ofar tayi, salma dake zaune tana kallon tashar Arewa 24 ta taso ta bud'e k'ofar, tana ganin humaira ta b'ata fuska tace lafiya?
murmushin mugunta humaira tayi, tace "kizo mijina yana kiranki" ta juya tayi tafiyarta. d'an tsaki salma taja tace da wayace ba mijinki bane? (ina fatan salma ba haushi kikaji ba😃😃) juyawa tayi ta Koma cikin daki ta dad'a gyara fuskarta ta fesa turare me dad'in k'amshi, ko hijab bata d'auka ba ta nufi falon da suke.
Tunda ta doso wajen yake binta da kallo, kasancewar kayan baccine a jikinta riga da wando cotton, sun kamata tsam rigan me hannun shimi ne, wandon a iya guiwa ya tsaya mata, ta saka hulan turban kalan kayan pink.
tana zuwa ta nemi waje ta zauna ba tare data ce musu komai ba, humaira da tun fitowar salma tayi dana sanin kiranta da tace ayi ganin irin kallon da A.A yake mata. Gashi ba daman tayi magana kar plan d'inta yargaje🤣🤣🤣🤣
Ta wurga ma salma harara sannan ta juya ta kalli A.A daya maida hankalinsa ga kallon t.v ta daure tace "babyna gatanan ta fito ka fad'a mata" beko kalle ta ba yace ki fad'a mata mana tunda tsarinki ne hakan.
Da sauri ta dube shi jin tana mishi magana yana bata amsa wani iri. wai meke faruwa ne kodai asirin da namishi ya fara warwarewa ne? daga zuwan ta komai ya fara warware wa, aikuwa zanyi saurin aikata lahira tun kafin komai ya kmab'e min, tayi maganar cikin zuciyarta.
duban salma tayi dakanta yake kallon wani gefe na falon tace "to amarya dama maganar girki ne, kinsan hajiya tace yayi miki kwana 7 d'inki kafin araba kwana bibbiyu. saboda haka yanzu duk wacce take da girki zata fito a had'u a dinga cin abinci tare. Akwai wacce take yi mana girki, ina fatan ba matsala?" ta k'arasa tana murmushin yak'e
mamaki ne ya kama salma,tabbas akwai abinda take shiryawa dan tasan ruma baya tsami banza, ita zata nuna ma kirsa? wato dan tana gaban mijinta shine zata nuna ita na ALLAh ne, aikuma zata nuna mata itama macece tana da irin nata salon.
Murmushi salma tayi tace "haba Aunty ai duk abinda kika yanke dai-dai ne, amma ni inso samune nafison na dinga yima mijina abinci, dan banason masu aiki su dinga yima mijina hidima.....
Tun kan salma ta k'arasa humaira tayi saurin katseta, ganin tana neman wargaza mata plan. tace"haba k'anwata kamar ke kina auren Alh. A.A me dala ace kina girki da kanki. ai wannan abin kunya ne a gare mu.
girgiza kai salma tayi tace ba abin kunya bane Aunty tunda aikin ladane kuma wa mijina zan yima, ni inaga ai ba lefi aciki.
A.A da yake kallon news a t.v amma hankalinsa yana wajensu,yana jin maganganun da sukeyi, ya juyo ya kalli humaira yace "tunda tace zata iya ki rabu da ita mana, kun cika min kunne da surutunku, kun hana na fahimci abinda ake fad'a a news d'in. Yana maganar yana satan kallon salma da take jifansa da murmushi duk dan ta k'ular da humaira.
humaira da ranta ya gama b'aci ta kalle shi ta fara magana ta ma manta da batun wani plan tace "wallahi duk abinda na tsara shi za'abi, koka manta haka akeyi aduk lokacin da kayi aure? kaine ka bani damar tsara duk yanda nake so dan haka yanzuma haka nake buk'atar ayi.
kallonta salma tayi tana murmushi tace "Aunty menene abin d'aga hankali anan? kawai dan zan dinga yima mijina hidima ai ba wani abu bane....
Keeeï¼... Badake nake yiba da wanda ya ajiyeki nake magana. humaira ta fad'a tana huci kamar kububuwa
Look humaira kinsan fa ban cika son hayaniya ba, please kowa ta tafi d'akinta banson tashin hankali.
Mik'ewa salma tayi fuskarta cike da murmushi ta wuce d'akinta. itama humaira tashi tayi ta dube shi tace, "Abdul nika wulak'anta a gaban wancan banzan ko? to wallahi se nayi maganinku daga kai har ita. ta wuce shi ta shige d'aki"
Tsaki yaja ya kashe kallon ya nufi d'akin salma, hakanan yake jin ya rage tsoron humaira yana ganin yanzu bazai d'auki rashin mutuncin ta ba.
kuyi hakuri da wannan wallahi har nayi ya goge.
Readers naji k'orafin ku zan dingayi kullum insha ALLAhu, wanda ba'abi ra'ayin ku ba ina me baku hak'uri.
🌳🌳UMMU AFFAN🌳🌳
[1:36PM, 2/7/2018] ‪+234 808 677 7945‬: 🌳🌳🌳🌳🌳
ZAB'IN MAHAIFINA
🌳🌳🌳🌳🌳
Written by SADIYA ALHASSAN (Ummu Affan)
ðŸŒHAJOW ðŸ“ðŸŒ
ðŸŒðŸ‘©â€ðŸ‘§â€ðŸ‘§ðŸ‘©â€ðŸ‘§â€ðŸ‘§ðŸ‘©â€ðŸ‘§â€ðŸ‘§HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS âœðŸ¾âœðŸ¾âœðŸ¾ðŸŒ
Dedicated to PRINCESS ESHAT AYSM
AYSHA BICHIKI
Page 21
Sistr eyshert Aysm ina miki murna da fara sabon novel d'inki (WAZAN SO) ALLAh ya k'ara d'aukaka,yanda kika fara lafiya ALLAh yasa ki gama lafiya. Inayin ki sistr irin sosai d'innan.😘
Akashe ya samu wutan falon amma yana iya hango d'an haske ta cikin bedroom d'in. Sallama yayi sannan ya shiga d'akin a kwance ya sameta ta bama k'ofar baya, tayi nisa a tunani da alama batasan mutum ya shigo d'akin ba.
Gefenta yaje ya kwanta ya juya mata baya,sannan yaja bargo ya lullube jikinsa. ya kashe bedsite lamp dake gefenshi, se a lokacin salma tasan ya shigo d'akin. Cikin sauri ta mik'e zaune ta ce mallam lafiya zaka shigo min d'aki ba ko sallama,
Ko juyowa beyiba bare ya nuna yasan tana magana. duk da haka batayi shiru ba, gaskiya ka tashi ka koma d'ayan d'akin dan ni bansa ba kwana da wani namiji a cikin d'aki d'aya ba.
Batare daya juyo ba ya fara magana "Nan gidana ne ina da ikon shiga duk inda naso a kowani lokaci, kuma ya kamata kisan banbancin dake tsakanin da da kuma yanzu, ki iya bakinki saboda yanzu a k'ark'ashin iko na kike, ba k'ark'ashin ikon iyayenki ba. Agidana kike ba gidanku naje ba.
Shiru salma tayi batare da ta sake cewa komai ba ta mik'e domin ta koma d'ayan d'akin. Muryar shi taji yana bata umurni koma ki kwanta, dan ni bana raba makwanci da matata ki kiyaye ko saboda gaba, komawa salma tayi ta kwanta amma ta gagara runtsawa saboda fargaba da rashin sabo, ga sanyi da takeji.
Shima ba baccin yakeyi ba, tunani ne ya cika kwakwalwar sa, ya rasa me yake damunsa ga wani feeling dayake ji wanda be tab'a jin irinsa akan wata 'ya mace ba.
Sauk'ar numfashinta yaji abayansa alamar bacci ya d'auketa, juyowa yayi yana kallonta tana baccinta cikin kwanciyar hankali, ta dunk'ule jikinta waje d'aya. Tsintar kansa yayi da rungumota zuwa jikin sa, a tare suka sauk'e ajiyar zuciya, itakam cikin bacci ne ba tare datasani ba, yayin dashi kuma najin dad'in jinta dayayi ajikinsa ne.
Kallonta yakeyi be tab'a sanin tana da kyau sosai haka ba, tayi mishi kyau datake bacci, sleeping beauty ya furta a hankali.
Jawo bargon yayi ya lullub'a musu gaba d'aya, yayi addua ya shafa musu. abinda ya juma beyi ba wato addu'an kwanciya.
Cikin dare salma ta farka tajita a jikin mutum, hannu takai ta kunna lamp d'in dake gepenta, zuba mishi ido tayi tana kallon fuskarshi ga kwantaccen sajen shi wanda ya kwanta a fuskar shi, ya k'arama fuskar shi kyau da kamala gaskiya ta yarda Abdul me kyau ne.
Hannun shi ta kalla wanda ya zagayeta dashi tunani takeyi ta yanda zata cire hannun batare data tashe shi, gashi so take yi ta tashi ta d'auro alwala tayi sallan nafila.
A hankali ta zare jikinta a cikin nashi ta nufi toilet domin ta d'auro alwala, k'aran bud'e kofar toilet d'inne ya tashe shi. Yana kallonta ta cikin hasken dayake d'akin, ta fito ta d'auki hijab d'inta ta tada kabbara.
Raka'a hud'u tayi tadad'e a sujjadarta ta k'arshe tana kaima ALLAh kukanta kafin ta d'ago ta sallame.