Chapter 9
Wani Sharrin Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Ajwa tana kwance taji Sa'idu ya faɗo ɗakin da sauri ta manne ƙarshen gado jikinta na rawa, ganin bai ganta a parlour ba yasa ya shiga bedroom ɗin a can ƙarshen gado ya hangota.
Ganin yanda jikinta yake rawa yasa shi runtse ido yana cije baki, Ajwa ta firgita da yanda ta ganshi duk da cewar idan ran shi ya ɓaci daman hakan yana faruwa.
Ganin idon sa a rufe yasa ta lallaɓa ta fice a ɗakin, Sa'idu yaji fitar ta kuma bai hanata ba domin idan ya ce zai yi magana wallahi zai iya karyata ba tare da ya sani ba.
Bai ƙara bi ta kanta ba sai da yayi wanka ya shirya kwanciyar bacci, ya kira wayarta bata ɗaga ba kuma ya san tana ganin kiran, ya miƙe ya nufi bedroom ɗin da yake da ya ƙinin tana ciki, yana turawa ya ƙofar ya buɗe domin ta san kota kulle sai ya buɗe.
Tana kwance tana chart taji motsin shi da sauri ta kifa wayar ta rufe ido, ya zauna kusa da ita yana kiran sunanta.
Ganin zata ɓata mishi lokaci yasa ya fara abin da ya kawo shi, Ajwa da sauri ta miƙe tana ture shi cike da masifa.
Dambe iya dambe suka ci da Sa'idu kafin yasa mata ƙarfi ya danneta, ya gama abin da zaiyi ya tashi ya fita Ajwa na kwance tana tsine mishi, haka zaman nasu ya cigaba da kasancewa kullum cikin yawo take idan yayi magana ta ce kasuwanci take yi.
Inna ta sanja salo duk lokacin da taga Mamy ta fito zata shiga toilet ko ɗakin Baba, sai tazo da sauri ta bangajeta ta wuce wani lokacin tana zaune a parlour zata ji an watso mata ruwa ko kuma a turo mata da shara, idan tayi magana masifa domin Baba yanzu sai abin da Inna ta ce yake yi.
Bayan sallar azahar dukkan su suna zaune suna fira a tsakar gida, Inna ta kalle su ta ce.
"Ina son kuje gidan Tani kuja mata kunne, idan kuma taƙi ji kuyi mata kashedi yanda zata fahimta." Zainab ta riga su miƙewa ta ɗauko musu hijjabai suka fita Inna tana faɗin.
"Wallahi ku tabbatar kun nuna mata cewar ku jinin Talatu ce." Mamy na zaune a bakin ƙofar ɗakin ta, ta miƙe tana cewa.
"Allah ya kyauta." Inna daman jiran ƙiriss take yi ta fara masifa tana zage zage, Mamy ta janyo net ɗin ta rufe ta ciki.
Inna tana cigaba da masifa bakinta har kumfa yake yi, Zainab ta shigo ta zauna Inna tana shirin tambayarta sauran suka shigo, bayan sun zauna suka bata labarin abin da ya faru Inna ta kwashe da dariya suka tafa da yaran cike da alfahari.
Abin da ya faru bayan sunje gidan Tani cike da rashin kunya Zainab ta fara magana.
"Ke baƙar munafuka algunguma tsohuwar ala wadai, wallahi idan kika ƙara shiga sabgar uwar mu sai mun naɗa miki dukan da sai kin kusa zuwa lahira, tsohuwar kawai wacce bata kama girmanta." Kowanne da cin mutuncin da yayi mata, Asabe jikan Tani dake bacci ta fito tana mayar musu da amsa, suka haɗu su kai mata duka sai da suka ga bata motsi sannan suka fita Zainab ta lakace wa Tani hanci A'isha ta dungureta.
Inna sai da tayi rawa saboda murna Mamy tana bedroom bata san waina da ake soyawa ba, daddare Baba ya dawo gida daman girkin Mamy ne ta gama komai ta nufi ɗakin shi Inna na zaune tana kallo Baba yana cin abinci, Mamy ranta ya ɓaci domin idan ita ce wallahi babu zaman lafiya, amman haka ta daure tayi sallama ta shiga toilet.
Bayan ta fito daga toilet ta cire hijjab ɗin jikinta ta nun ke Baba da ya kalleta da sauri ya haɗiye abincin yana tari, Inna haushi kamar ya kashe ta ganin ɗan iskan shigar dake jikin Mamy.
Kiran wayar Baba ya dawo dashi cikin hankalinsa yana ɗaga kiran ya yanke, ya ajiye wayar ya shiga toilet bai jima da shigaba suka ji sallamar ɗan yaro a tsakar gida yana cewa.
"Zainab Khadijah A'isha an ce su zo ana kiransu a waje." Yaron yana faɗa ya zura da gudu, Inna tayi shewa tana faɗin.
"Ƴaƴa mata masu farin jini." Ta hararari Mamy ta fita, babu tambayar wanda yake kiran ta basu umarnin su fita bayan sun shafa turare da powder.
Har ƙarfe goma babu labarin yaran Inna hankalinta ya fara tashi amman ta ce bari zuwa sha ɗaya da rabi idan basu dawo ba sai taje ta duba ko lafiya, tana zaune tana zan cen zuci har sha biyu saura.
Inna ta fita zuwa ɗakin Baba tana zuwa ta shiga dukan ƙofar kamar ba dare ba, tana zaune a saman darduma tana karatun Qur'ani tayi banza da ita cike da takaicin wannan masifar, Baba ya ringa jin bugun ƙofa tun ana bugawa a hankali har ta fara bugawa da ƙarfi, yayi tsaki ya sauko daga gadon ya ɗau jallabiya yasa yana faɗin.
"Dan Allah ki bar dukan ƙofar nan karki karya, sai ka ce ba dare ba."
Inna tayi ƙwafa tana cigaba da dukkan ƙofar Baba ya buɗe yana ɗaure fuska, cikin tashin hankali ta fara magana.
"Tun ɗazun yara sun fita zan ce har yanzu basu dawo ba, kuma na leƙa ƙofar gida amman banga kowa ba."
Baba ya ce.
"Bangane yara sun fita zan ce basu dawo ba.?"
"Dan Allah kazo kaje ka dubo su, wallahi wannan shirun bana lafiya bane." Inna ta faɗa tana fashewa da kuka, Baba ya ture Inna ya fita.
Ƙarfe ɗaya dai-dai ya dawo gida hankalin shi duk ya tashi, Inna tana jin shigowar shi ta fito tana tambayar ko ya gansu, ya kwantar mata da hankali akan ta bari zuwa gobe idan Allah ya kaimu, Inna ta fara masifa tana kuka ita wallahi Mamy ce tasa a sace mata yara.
Ranar babu wanda yayi bacci saboda masifar Inna, Mamy data ga abin babu sauƙi ta koma ɗakinta gurin yaranta ta kwanta, Baba a zaune ya kwana yana rarrashin Inna.
Washegari Baba tun da ya tafi sallar asuba bai dawo gida ba, ƙarfe goma akai sallama a ƙofar gida Inna ta miƙe ido duk ya kumbura ga rashin bacci ga kuka.
Matashi ne sanye da uniform ɗin ƴan sanda Inna ta dafe ƙirji tana salati, matashin ya gaisheta bai jira amsarta ba ya buƙaci su tafi, officer ana nemanta Inna ta ruɗe tana faɗin wallahi babu inda zata je.
Ganin babu sauki kuma tana ta zagin shi ya ɗaga ya bayar da umarnin shigowa, matane guda uku sanye da uniform ɗin ƴan sanda suka tasa ƙeyar Inna, Mamy tana fitowa motar na tafiya koda ta leƙa bata ga kowa a ƙofar gidan ba.
Sai da akai la'asar Baba ya dawo gida yayi zuru-zuru da ido kamar wanda ya tashi daga jinya, Mamy ya umarta data juye mishi ruwan flask yayi wanka.
Sai da yayi wanka ya zauna yana tambayarta Inna, domin tunda ya shigo bai ji motsinta ba Mamy ta ce bata san inda take ba.
Baba ya kasa cin komai saboda tashin hankali, ya bayar da kuɗin cefane sannan ya miƙe ya fita.
Yana fita ya samu wani mutum tsaye yana neman yaron da zai aika, ganin Baba ya fito suka gaisa mutumin ya ce.
"Dan Allah ina neman Alhaji Usman ne."
"Lafiya dai koh.?" Baba ya faɗa yana ƙare mishi kallo.
Two days zazzabi kuyi maneji da wannan.
Ta Batulu ce ✍️*WANI SHARRIN*
(Mutum ke nemowa kansa)
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION (J.W.A)*
*TEAM JAJIRTATTUN MARUBUTA*
*ALLAHUMMA SALLI ALA SAYYADINA MUHAMMAD WASSALIM*
Free pages sun kusa ƙarewa.
Written by ✍️
Jagabar Jajirtattu
Ganin yanda jikinta yake rawa yasa shi runtse ido yana cije baki, Ajwa ta firgita da yanda ta ganshi duk da cewar idan ran shi ya ɓaci daman hakan yana faruwa.
Ganin idon sa a rufe yasa ta lallaɓa ta fice a ɗakin, Sa'idu yaji fitar ta kuma bai hanata ba domin idan ya ce zai yi magana wallahi zai iya karyata ba tare da ya sani ba.
Bai ƙara bi ta kanta ba sai da yayi wanka ya shirya kwanciyar bacci, ya kira wayarta bata ɗaga ba kuma ya san tana ganin kiran, ya miƙe ya nufi bedroom ɗin da yake da ya ƙinin tana ciki, yana turawa ya ƙofar ya buɗe domin ta san kota kulle sai ya buɗe.
Tana kwance tana chart taji motsin shi da sauri ta kifa wayar ta rufe ido, ya zauna kusa da ita yana kiran sunanta.
Ganin zata ɓata mishi lokaci yasa ya fara abin da ya kawo shi, Ajwa da sauri ta miƙe tana ture shi cike da masifa.
Dambe iya dambe suka ci da Sa'idu kafin yasa mata ƙarfi ya danneta, ya gama abin da zaiyi ya tashi ya fita Ajwa na kwance tana tsine mishi, haka zaman nasu ya cigaba da kasancewa kullum cikin yawo take idan yayi magana ta ce kasuwanci take yi.
Inna ta sanja salo duk lokacin da taga Mamy ta fito zata shiga toilet ko ɗakin Baba, sai tazo da sauri ta bangajeta ta wuce wani lokacin tana zaune a parlour zata ji an watso mata ruwa ko kuma a turo mata da shara, idan tayi magana masifa domin Baba yanzu sai abin da Inna ta ce yake yi.
Bayan sallar azahar dukkan su suna zaune suna fira a tsakar gida, Inna ta kalle su ta ce.
"Ina son kuje gidan Tani kuja mata kunne, idan kuma taƙi ji kuyi mata kashedi yanda zata fahimta." Zainab ta riga su miƙewa ta ɗauko musu hijjabai suka fita Inna tana faɗin.
"Wallahi ku tabbatar kun nuna mata cewar ku jinin Talatu ce." Mamy na zaune a bakin ƙofar ɗakin ta, ta miƙe tana cewa.
"Allah ya kyauta." Inna daman jiran ƙiriss take yi ta fara masifa tana zage zage, Mamy ta janyo net ɗin ta rufe ta ciki.
Inna tana cigaba da masifa bakinta har kumfa yake yi, Zainab ta shigo ta zauna Inna tana shirin tambayarta sauran suka shigo, bayan sun zauna suka bata labarin abin da ya faru Inna ta kwashe da dariya suka tafa da yaran cike da alfahari.
Abin da ya faru bayan sunje gidan Tani cike da rashin kunya Zainab ta fara magana.
"Ke baƙar munafuka algunguma tsohuwar ala wadai, wallahi idan kika ƙara shiga sabgar uwar mu sai mun naɗa miki dukan da sai kin kusa zuwa lahira, tsohuwar kawai wacce bata kama girmanta." Kowanne da cin mutuncin da yayi mata, Asabe jikan Tani dake bacci ta fito tana mayar musu da amsa, suka haɗu su kai mata duka sai da suka ga bata motsi sannan suka fita Zainab ta lakace wa Tani hanci A'isha ta dungureta.
Inna sai da tayi rawa saboda murna Mamy tana bedroom bata san waina da ake soyawa ba, daddare Baba ya dawo gida daman girkin Mamy ne ta gama komai ta nufi ɗakin shi Inna na zaune tana kallo Baba yana cin abinci, Mamy ranta ya ɓaci domin idan ita ce wallahi babu zaman lafiya, amman haka ta daure tayi sallama ta shiga toilet.
Bayan ta fito daga toilet ta cire hijjab ɗin jikinta ta nun ke Baba da ya kalleta da sauri ya haɗiye abincin yana tari, Inna haushi kamar ya kashe ta ganin ɗan iskan shigar dake jikin Mamy.
Kiran wayar Baba ya dawo dashi cikin hankalinsa yana ɗaga kiran ya yanke, ya ajiye wayar ya shiga toilet bai jima da shigaba suka ji sallamar ɗan yaro a tsakar gida yana cewa.
"Zainab Khadijah A'isha an ce su zo ana kiransu a waje." Yaron yana faɗa ya zura da gudu, Inna tayi shewa tana faɗin.
"Ƴaƴa mata masu farin jini." Ta hararari Mamy ta fita, babu tambayar wanda yake kiran ta basu umarnin su fita bayan sun shafa turare da powder.
Har ƙarfe goma babu labarin yaran Inna hankalinta ya fara tashi amman ta ce bari zuwa sha ɗaya da rabi idan basu dawo ba sai taje ta duba ko lafiya, tana zaune tana zan cen zuci har sha biyu saura.
Inna ta fita zuwa ɗakin Baba tana zuwa ta shiga dukan ƙofar kamar ba dare ba, tana zaune a saman darduma tana karatun Qur'ani tayi banza da ita cike da takaicin wannan masifar, Baba ya ringa jin bugun ƙofa tun ana bugawa a hankali har ta fara bugawa da ƙarfi, yayi tsaki ya sauko daga gadon ya ɗau jallabiya yasa yana faɗin.
"Dan Allah ki bar dukan ƙofar nan karki karya, sai ka ce ba dare ba."
Inna tayi ƙwafa tana cigaba da dukkan ƙofar Baba ya buɗe yana ɗaure fuska, cikin tashin hankali ta fara magana.
"Tun ɗazun yara sun fita zan ce har yanzu basu dawo ba, kuma na leƙa ƙofar gida amman banga kowa ba."
Baba ya ce.
"Bangane yara sun fita zan ce basu dawo ba.?"
"Dan Allah kazo kaje ka dubo su, wallahi wannan shirun bana lafiya bane." Inna ta faɗa tana fashewa da kuka, Baba ya ture Inna ya fita.
Ƙarfe ɗaya dai-dai ya dawo gida hankalin shi duk ya tashi, Inna tana jin shigowar shi ta fito tana tambayar ko ya gansu, ya kwantar mata da hankali akan ta bari zuwa gobe idan Allah ya kaimu, Inna ta fara masifa tana kuka ita wallahi Mamy ce tasa a sace mata yara.
Ranar babu wanda yayi bacci saboda masifar Inna, Mamy data ga abin babu sauƙi ta koma ɗakinta gurin yaranta ta kwanta, Baba a zaune ya kwana yana rarrashin Inna.
Washegari Baba tun da ya tafi sallar asuba bai dawo gida ba, ƙarfe goma akai sallama a ƙofar gida Inna ta miƙe ido duk ya kumbura ga rashin bacci ga kuka.
Matashi ne sanye da uniform ɗin ƴan sanda Inna ta dafe ƙirji tana salati, matashin ya gaisheta bai jira amsarta ba ya buƙaci su tafi, officer ana nemanta Inna ta ruɗe tana faɗin wallahi babu inda zata je.
Ganin babu sauki kuma tana ta zagin shi ya ɗaga ya bayar da umarnin shigowa, matane guda uku sanye da uniform ɗin ƴan sanda suka tasa ƙeyar Inna, Mamy tana fitowa motar na tafiya koda ta leƙa bata ga kowa a ƙofar gidan ba.
Sai da akai la'asar Baba ya dawo gida yayi zuru-zuru da ido kamar wanda ya tashi daga jinya, Mamy ya umarta data juye mishi ruwan flask yayi wanka.
Sai da yayi wanka ya zauna yana tambayarta Inna, domin tunda ya shigo bai ji motsinta ba Mamy ta ce bata san inda take ba.
Baba ya kasa cin komai saboda tashin hankali, ya bayar da kuɗin cefane sannan ya miƙe ya fita.
Yana fita ya samu wani mutum tsaye yana neman yaron da zai aika, ganin Baba ya fito suka gaisa mutumin ya ce.
"Dan Allah ina neman Alhaji Usman ne."
"Lafiya dai koh.?" Baba ya faɗa yana ƙare mishi kallo.
Two days zazzabi kuyi maneji da wannan.
Ta Batulu ce ✍️*WANI SHARRIN*
(Mutum ke nemowa kansa)
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION (J.W.A)*
*TEAM JAJIRTATTUN MARUBUTA*
*ALLAHUMMA SALLI ALA SAYYADINA MUHAMMAD WASSALIM*
Free pages sun kusa ƙarewa.
Written by ✍️
Jagabar Jajirtattu