Chapter 10
Wani Sharrin Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Mutumin ya ce.
"Ana nemanka a officer ɗin mu dake can kan tudu."
Baba zai yi magana mutumin ya katse shi ta hanyar faɗin.
"Ba wani abin damuwa bane." Baba yayi shiru suka nufi bakin titi suka hau napep, suna shiga cikin police station ɗin Baba ya dafe ƙirjin shi yana faɗin.
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un." Ya ringa mai mai tawa har sai da ya samu natsuwa sannan ya shiga officer ɗin da aka nuna mishi.
Wani babban mutum ne zaune a kujera yana sanye da uniform ɗin ƴan sanda Baba yayi sallama ya shigo, bayan sun gaisa cikin mutunci officer ya kalli mutumin da suka shigo da Baba ya ce.
"Shigo dasu."
10 minutes Zainab ta shigo Khadijah A'isha Inna suka shigo officer ɗin duk sunyi zuru zuru, Baba ya miƙe cike da mamakin abin da ya kawo su police station.
"Maine ne alaƙarka da wa in nan mutanen.?" Officer ya faɗa ba tare da ya ɗago ba.
"Iyalina ce da ƴaƴana." Baba ya faɗa muryan shi tana rawa.
"Sunje gidan mutane sunyi rigima har dambe." Officer ya faɗa yana tsare Baba da ido.
Kafin Baba yayi magana officer yaci gaba da cewa.
"Yanzu haka yarinyar da suka daka tana hospital akwance bata sanin wanda yake kanta."
An dinga ɗauki ba daɗi kafin Baba ya shawo kan officer ya bayar da belinsu, shima sai da aka kira saurayin Asabe domin shi ya shigar da ƙaran, bayan an bayar da belin officer yayi musu iyaka da gidan Tani, kuma dole Baba ya ɗau nauyin Asabe har zuwa lokacin da zata warke.
Suna fitowa daga police station ɗin yayi gaba abin shi duk yanda Inna take kiran shi bai tsaya ba napep ya tsayar zuwa gurin sana'ar shi.
Inna a ƙafa suka dawo gida suna tafe tana tsinewa Baba yaran suna taya ta, babu sallama suka faɗa gidan kowace tayi zuru zuru kamar masu ciwo.
Mamy tana zaune a ƙofar ɗakinta suna karatu da yara, bata ce musu komai ba suma basu kulata ba.
Inna ta kunna wuta ta ɗaura ruwan zafi domin tun a hanya Zainab ta bata labarin irin dukan da suka sha, kuma ko Zainab ɗin bata faɗa ba Inna taga tabon bulala ajikin yaran.
Kowacen su tayi wanka ta gasa jikinta bayan sun fito sun shirya Inna ta zubo musu taliya a babban plate, suka shimfida babban tabarma aka zauna suna cin abinci suna zagin Tani da Asabe.
Bayan sati ɗaya sun warware sun cigaba da harkokin su Inna ta ce su shirya ta aike su gidan ƙanwarta Ladi, bayan la'asar Mamy ta fito zata shiga toilet Inna tana zaune a tsakar gida ganin Mamy ta shiga toilet yasa ta miƙe ta ɗau buta ta tsaya a bakin ƙofa tana jiran ta fito.
Mamy na fitowa Inna ta bangajeta sai da ta kusa faɗuwa da sauri ta ce.
"A'uzubillahi minal shaiɗanin rajin." Inna dake cikin toilet ta fito da sauri tana cewa.
"Wanene shaiɗanin?."
Mamy ta raɓata zata huce Inna ta riƙota tana faɗin.
"Wallahi sai kin gayamun wanene shaiɗani."
"Sakin mun hannu bana son tashin hankali." Mamy ta faɗa fuska cike da ɓacin rai.
"Idan naƙi saki fa." Inna ta faɗa tana ƙara riƙe hannun da kyau
"Zan shayar dake mamakin da ba a taɓa shayar dake ba." Faɗin Mamy tana jin kamar ta rufe Inna da duka.
Kafin Mamy ta rufe baki Inna ta dunƙula hannu ta kai mata duka a ciki, da sauri Mamy ta tare tana ƙwace hannunta.
Inna ta ringa yunƙurin dukan cikin ganin abin bana hankali bane Mamy tasa dukka karfinta ta bangaji Inna ta huce ɗaki.
Tana shiga Inna na biyota dambe iya dambe, Mamy damuwarta karta illata mata cikin dake jikinta ganin dai ta kasa cin nasara akan Mamy yasa ta rarumo ludayi ta bugawa Mamy a kai gurin ya fashe jini ya fara fita, cikin ficewar hayyaci Mamy taji hannunta ya riƙo wani abu bata tsaya dubawa ta bugawa Inna a kai daga nan bata ƙara sanin abin da ya faru ba.
Bayan sallar isha'i Mamy ta buɗe idonta da taji yayi mata nauyi, Hajiya ta gani zaune a kusa da ita.
A hankali ta cigaba da buɗe ido Yusra Aysar suna ganin ta farka suka matsa gaban gadon suna mata sannu, a hankali abubuwan da suka faru suka cigaba da dawo mata daki daki, lokaci ɗaya ta ware ido tana ƙarema ɗakin kallo hospital ne take kwance a kai, ta shiga tambayar kanta waya kawo ta hospital.
Hajiya ta gama karantar tunaninta sannan ta dafa kafaɗarta tana yi mata sannu, Mamy ta shafa cikin jikinta taji yana nan tayi ajiyar zuciya, goshinta taji yana zafi kamar ana zuba garwashi ta rintse ido tana shafa gurin bandeji taji ta taɓa.
Hajiya ta taimaka mata ta rama sallolin dake kanta, sannan ta zauna a saman darduman tana jan charbi.
Mamy sai da ta kwana uku a hospital kafin a sallamota, lokacin da zasu shiga mota tayi tunanin gida Hajiya zata wuce da ita amman dai taga saɓanin haka, shiru tayi ta zubawa sarautar Allah ido har suka ƙarasa gidan, Mamy taji hawaye ya zubo mata ta kalli mahaifiyarta zata yi magana Hajiya ta rufe mata baki tana girgiza kai.
Suna shiga suka samu an shimfida babban tabarma da mutane a zaune Isma'il ya miƙe yana riƙo Mamy suka zauna sannan aka gaggaisa, iyayen Baba ne da iyayen Mamy Inna tana zaune rabin fuska manne da bandeji ita kaɗai sai uwar mijinta a gefenta.
Aka tattauna game da abin da ya faru kowa laifin Inna ya gani, amman Hajiya sai ta rufe Mamy da faɗa Isma'il yana bata haƙuri.
Mamy ta rarrafa gaban uwar mijinta ta riƙo hannayenta hawaye yana zuba a cikin idonta ta ce.
"Dan Allah Mama kisa Usman ya sakeni." Mutanen gurin kowa yayi tsit, an rasa wanda zai yi magana Isma'il ya buɗe baki zai magana Hajiya ta ɗaga mishi hannu.
Baba ya matsa gaban Mama yana faɗin.
" Wallahi Mama ba zan iya sakinta ba." Yana faɗan haka ya bar gurin, domin ko sama da ƙasa zata haɗu ba zai iya sakin Mamy ba.
Inna baƙin ciki kamar ya kasheta, domin taso Mama ta matsa mishi dole sai ya sake ta.
Da ƙyar Mama ta rarrashi Mamy tayi shiru sannan ta kama hannunta suka nufi bedroom ɗinta, bayan sun shiga ta zaunar da ita saman kujera ta bata ruwa tasha.
Sai da taga ta fara sauke ajiyar zuciya sannan ta zauna kusa da ita ta fara magana.
"Zaman aure ibada ne ba zaman jin daɗi ba zaman aure bauta ne ba zaman holewa ba."
"Tun da kika ji ance bauta kin san abin sai ka gamu da jarabawa iri iri, idan kasa haƙuri da tawakkali sai komai yazo maka da sauƙi, kuma ina son kisan abu guda ɗaya ubangiji yana jarabtar bayinsa wanda yake sone, dan Allah ki ƙara haƙuri akan wanda kike yi domin nasan zaman gidan Usman sai mace mai haƙuri da juriya."
Hajiya tana tsaye tana sauraron su ganin ma duk abin da zata faɗawa Mamy uwar mijinta ta gaya mata yasa ta koma, ta umarci Isma'il ya mayar da ita gida.
Mama ta daɗe a ɗakin Mamy tana kwantar mata da hankali kafin ta fito, koda ta fito babu kowa a tsakar gidan sai Yusra da Aysar suna wasa ɗakin Inna ta shiga bayan tayi sallama.
Itama ta jima a ɗakin tana yi mata nasiha kafin ta tambaye ta yara, Inna ta faɗa mata cewar ta aike su Mama tayi sallama ta tafi Inna tabi ta da harara tana jin hutar tsanar Mamy a ranta, domin idonta ne ya fashe lokacin da Mamy ta buga mata taɓarya a fuska ya sameta a ido, amman doctor ya ce babu wani matsala in sha Allah.
Lokacin da yaran suka dawo suka samu mahaifiyarsu a haka ɗakin Mamy suka nufa wai zasu zaneta, Inna ta hanasu tana ce musu ba yanzu bane lokacin da ya dace su rama mata ba su jira lokaci yana zuwa.
Gidan Ajwa.
Ta Batulu ce ✍️*WANI SHARRIN*
(Mutum ke nemowa kansa)
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION (J.W.A)*
*TEAM JAJIRTATTUN MARUBUTA*
Marubuciyar
*RAYUWAR MU*
*MA'EESHAT*
*WANI SHARRIN*
*ALLAHUMMA SALLI ALA SAYYADINA MUHAMMAD WASSALIM*
Written by ✍️
Jagabar Jajirtattu
"Ana nemanka a officer ɗin mu dake can kan tudu."
Baba zai yi magana mutumin ya katse shi ta hanyar faɗin.
"Ba wani abin damuwa bane." Baba yayi shiru suka nufi bakin titi suka hau napep, suna shiga cikin police station ɗin Baba ya dafe ƙirjin shi yana faɗin.
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un." Ya ringa mai mai tawa har sai da ya samu natsuwa sannan ya shiga officer ɗin da aka nuna mishi.
Wani babban mutum ne zaune a kujera yana sanye da uniform ɗin ƴan sanda Baba yayi sallama ya shigo, bayan sun gaisa cikin mutunci officer ya kalli mutumin da suka shigo da Baba ya ce.
"Shigo dasu."
10 minutes Zainab ta shigo Khadijah A'isha Inna suka shigo officer ɗin duk sunyi zuru zuru, Baba ya miƙe cike da mamakin abin da ya kawo su police station.
"Maine ne alaƙarka da wa in nan mutanen.?" Officer ya faɗa ba tare da ya ɗago ba.
"Iyalina ce da ƴaƴana." Baba ya faɗa muryan shi tana rawa.
"Sunje gidan mutane sunyi rigima har dambe." Officer ya faɗa yana tsare Baba da ido.
Kafin Baba yayi magana officer yaci gaba da cewa.
"Yanzu haka yarinyar da suka daka tana hospital akwance bata sanin wanda yake kanta."
An dinga ɗauki ba daɗi kafin Baba ya shawo kan officer ya bayar da belinsu, shima sai da aka kira saurayin Asabe domin shi ya shigar da ƙaran, bayan an bayar da belin officer yayi musu iyaka da gidan Tani, kuma dole Baba ya ɗau nauyin Asabe har zuwa lokacin da zata warke.
Suna fitowa daga police station ɗin yayi gaba abin shi duk yanda Inna take kiran shi bai tsaya ba napep ya tsayar zuwa gurin sana'ar shi.
Inna a ƙafa suka dawo gida suna tafe tana tsinewa Baba yaran suna taya ta, babu sallama suka faɗa gidan kowace tayi zuru zuru kamar masu ciwo.
Mamy tana zaune a ƙofar ɗakinta suna karatu da yara, bata ce musu komai ba suma basu kulata ba.
Inna ta kunna wuta ta ɗaura ruwan zafi domin tun a hanya Zainab ta bata labarin irin dukan da suka sha, kuma ko Zainab ɗin bata faɗa ba Inna taga tabon bulala ajikin yaran.
Kowacen su tayi wanka ta gasa jikinta bayan sun fito sun shirya Inna ta zubo musu taliya a babban plate, suka shimfida babban tabarma aka zauna suna cin abinci suna zagin Tani da Asabe.
Bayan sati ɗaya sun warware sun cigaba da harkokin su Inna ta ce su shirya ta aike su gidan ƙanwarta Ladi, bayan la'asar Mamy ta fito zata shiga toilet Inna tana zaune a tsakar gida ganin Mamy ta shiga toilet yasa ta miƙe ta ɗau buta ta tsaya a bakin ƙofa tana jiran ta fito.
Mamy na fitowa Inna ta bangajeta sai da ta kusa faɗuwa da sauri ta ce.
"A'uzubillahi minal shaiɗanin rajin." Inna dake cikin toilet ta fito da sauri tana cewa.
"Wanene shaiɗanin?."
Mamy ta raɓata zata huce Inna ta riƙota tana faɗin.
"Wallahi sai kin gayamun wanene shaiɗani."
"Sakin mun hannu bana son tashin hankali." Mamy ta faɗa fuska cike da ɓacin rai.
"Idan naƙi saki fa." Inna ta faɗa tana ƙara riƙe hannun da kyau
"Zan shayar dake mamakin da ba a taɓa shayar dake ba." Faɗin Mamy tana jin kamar ta rufe Inna da duka.
Kafin Mamy ta rufe baki Inna ta dunƙula hannu ta kai mata duka a ciki, da sauri Mamy ta tare tana ƙwace hannunta.
Inna ta ringa yunƙurin dukan cikin ganin abin bana hankali bane Mamy tasa dukka karfinta ta bangaji Inna ta huce ɗaki.
Tana shiga Inna na biyota dambe iya dambe, Mamy damuwarta karta illata mata cikin dake jikinta ganin dai ta kasa cin nasara akan Mamy yasa ta rarumo ludayi ta bugawa Mamy a kai gurin ya fashe jini ya fara fita, cikin ficewar hayyaci Mamy taji hannunta ya riƙo wani abu bata tsaya dubawa ta bugawa Inna a kai daga nan bata ƙara sanin abin da ya faru ba.
Bayan sallar isha'i Mamy ta buɗe idonta da taji yayi mata nauyi, Hajiya ta gani zaune a kusa da ita.
A hankali ta cigaba da buɗe ido Yusra Aysar suna ganin ta farka suka matsa gaban gadon suna mata sannu, a hankali abubuwan da suka faru suka cigaba da dawo mata daki daki, lokaci ɗaya ta ware ido tana ƙarema ɗakin kallo hospital ne take kwance a kai, ta shiga tambayar kanta waya kawo ta hospital.
Hajiya ta gama karantar tunaninta sannan ta dafa kafaɗarta tana yi mata sannu, Mamy ta shafa cikin jikinta taji yana nan tayi ajiyar zuciya, goshinta taji yana zafi kamar ana zuba garwashi ta rintse ido tana shafa gurin bandeji taji ta taɓa.
Hajiya ta taimaka mata ta rama sallolin dake kanta, sannan ta zauna a saman darduman tana jan charbi.
Mamy sai da ta kwana uku a hospital kafin a sallamota, lokacin da zasu shiga mota tayi tunanin gida Hajiya zata wuce da ita amman dai taga saɓanin haka, shiru tayi ta zubawa sarautar Allah ido har suka ƙarasa gidan, Mamy taji hawaye ya zubo mata ta kalli mahaifiyarta zata yi magana Hajiya ta rufe mata baki tana girgiza kai.
Suna shiga suka samu an shimfida babban tabarma da mutane a zaune Isma'il ya miƙe yana riƙo Mamy suka zauna sannan aka gaggaisa, iyayen Baba ne da iyayen Mamy Inna tana zaune rabin fuska manne da bandeji ita kaɗai sai uwar mijinta a gefenta.
Aka tattauna game da abin da ya faru kowa laifin Inna ya gani, amman Hajiya sai ta rufe Mamy da faɗa Isma'il yana bata haƙuri.
Mamy ta rarrafa gaban uwar mijinta ta riƙo hannayenta hawaye yana zuba a cikin idonta ta ce.
"Dan Allah Mama kisa Usman ya sakeni." Mutanen gurin kowa yayi tsit, an rasa wanda zai yi magana Isma'il ya buɗe baki zai magana Hajiya ta ɗaga mishi hannu.
Baba ya matsa gaban Mama yana faɗin.
" Wallahi Mama ba zan iya sakinta ba." Yana faɗan haka ya bar gurin, domin ko sama da ƙasa zata haɗu ba zai iya sakin Mamy ba.
Inna baƙin ciki kamar ya kasheta, domin taso Mama ta matsa mishi dole sai ya sake ta.
Da ƙyar Mama ta rarrashi Mamy tayi shiru sannan ta kama hannunta suka nufi bedroom ɗinta, bayan sun shiga ta zaunar da ita saman kujera ta bata ruwa tasha.
Sai da taga ta fara sauke ajiyar zuciya sannan ta zauna kusa da ita ta fara magana.
"Zaman aure ibada ne ba zaman jin daɗi ba zaman aure bauta ne ba zaman holewa ba."
"Tun da kika ji ance bauta kin san abin sai ka gamu da jarabawa iri iri, idan kasa haƙuri da tawakkali sai komai yazo maka da sauƙi, kuma ina son kisan abu guda ɗaya ubangiji yana jarabtar bayinsa wanda yake sone, dan Allah ki ƙara haƙuri akan wanda kike yi domin nasan zaman gidan Usman sai mace mai haƙuri da juriya."
Hajiya tana tsaye tana sauraron su ganin ma duk abin da zata faɗawa Mamy uwar mijinta ta gaya mata yasa ta koma, ta umarci Isma'il ya mayar da ita gida.
Mama ta daɗe a ɗakin Mamy tana kwantar mata da hankali kafin ta fito, koda ta fito babu kowa a tsakar gidan sai Yusra da Aysar suna wasa ɗakin Inna ta shiga bayan tayi sallama.
Itama ta jima a ɗakin tana yi mata nasiha kafin ta tambaye ta yara, Inna ta faɗa mata cewar ta aike su Mama tayi sallama ta tafi Inna tabi ta da harara tana jin hutar tsanar Mamy a ranta, domin idonta ne ya fashe lokacin da Mamy ta buga mata taɓarya a fuska ya sameta a ido, amman doctor ya ce babu wani matsala in sha Allah.
Lokacin da yaran suka dawo suka samu mahaifiyarsu a haka ɗakin Mamy suka nufa wai zasu zaneta, Inna ta hanasu tana ce musu ba yanzu bane lokacin da ya dace su rama mata ba su jira lokaci yana zuwa.
Gidan Ajwa.
Ta Batulu ce ✍️*WANI SHARRIN*
(Mutum ke nemowa kansa)
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION (J.W.A)*
*TEAM JAJIRTATTUN MARUBUTA*
Marubuciyar
*RAYUWAR MU*
*MA'EESHAT*
*WANI SHARRIN*
*ALLAHUMMA SALLI ALA SAYYADINA MUHAMMAD WASSALIM*
Written by ✍️
Jagabar Jajirtattu