Chapter 6
Wani Sharrin Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Ɗaya bayan ɗaya suka fito suna duƙar da kai, Baba ya kalli Ajwa ya ce.
"Ki shirya anjima zaki koma ɗakin ki."
Ta turo baki tana ɓata fuska ya yi kamar bai ganta ba, domin yanda yake ji wallahi zai iya zane ta saboda haushinta yake ji.
"Duk cikin ku babu wanda aka taɓa yiwa horan yunwa a gidan nan, amman shi ne zaku ringa hora ƙananun yara da yunwa koh.? Saboda kun zama mugaye marasu tausayi, to daga yau ba zan ƙara ɗaukar wannan iskancin ba, idan kuma kun ƙi ji wallahi zan ɗauki mummunar mataki akan ku." Ta inda yake shiga bata nan yake fita ba.
Daga ƙarshe ya jefa musu dubu ɗaya yana umartar su.
"A dafa mun macaroni da kifi yanzu." Yana gama faɗa ya bar gidan gaba ɗaya.
Ajwa ta riƙe baki tana cewa.
"Yaushe Baba ya zama hakan.?"
"Tun bayan tafiyar Inna." A'isha ta faɗa tana ɗaukar dubu ɗayan.
Suka dafa macaronin gaba ɗaya gida, saboda ba zasu iya tambayar shi kuɗin cefane ba.
A ɗan ƙaramin roba suka zubawa Yusra da ƙaninta.
Yusra ta fito tana raɓe raɓe Ajwa ta janyo ta.
"Shegiyya mai baƙin hali irin na uwarta." ta faɗa tana hararan ta, ita fa a rayuwar ta wallahi ta tsani wannan yarinyar.
Sai da ta gama zaginta sannan ta miƙa nuna mata robobin abincin su tana faɗin.
"Dangin mayu ɗauka kar ku cinye mu ɗanye."
"Sai dai ko ubanki shi ne dangin mayun." Baba ya faɗa yana shigowa gidan.
Yusra ta ɗau abincin ya kirata ya kalli ɗan abincin dake roban, ƙwafa ya yi yana shiga ɗakin shi.
Yusra data kusa shiga ɗakinsu Ajwa ta dakatar da ita tana faɗin.
"Dan ubanki zoki ɗauki abincin nan ki kai mishi." Ta ta dawo ta ɗau flask ɗin ta shiga ɗakin haɗe da sallama.
Baba ya ƙirƙiro murmushi yana tambayarta jikin Aysar, tayi murmushi tana cewa.
"Da sauƙi." ta ajiye ta flask ta fita.
Abincin su ta ɗauka ta shiga ɗaki Aysar yana kallon ɗan abincin ya fashe da kuka, ta ƙara mishi da nata sannan ya yi shiru, ta zuba mishi ido tana tuna maganar da Mamy ta gaya mata ranar da zata bar gidan, taji an dafa ta.
"Haba yarinyar kirki tunanin mai kike yi inata sallama ko motsi baki yi ba Aysar nata miki surutu kin yi banza dashi."
"Baba dan Allah ka kaimu gurin Mamy, ko kuma ka ce mata ta dawo." Yusra ta faɗa tana fashewa da kuka.
"Ko ɗazun naje gidan Mamyn kuma ta ce tana nan dawo in sha Allah." Bayan ya faɗi maganar ya kau da kai.
Sai da ya tabbatar sunyi shiru sannan ya ajiye musu flask ɗin abincin shi, Yusra ta ɗauko babban plate ta zuba musu abincin rabi, suka zauna suna ci Baba yana bawa Aysar a baki.
Hannu baka hannu ƙwarya haka ta ringa cin abincin, daga ƙarshe Baba ya cire hannunshi ya zubawa Yusra ido.
Kaɗan suka rage abincin Baba ya rufe ya ajiye ta gyara gurin Yusra.
"Kuje kuyi alwala kuyi sallah zan tafi masallaci, sannan ku rufe ƙofa idan na dawo zanyi magana sai ku buɗe." Baba ya ce yana fita daga ɗakin.
Bayan an idar da sallah ƴan uwan Baba suka kira shi a waya suka sanar dashi suna jiranshi a gida.
A zaure Baba ya gansu suna tsaye.
"Ya baku shiga gidan ba kuka tsaya a waje?."
Baba ya faɗa cike da mamaki.
"Daman akwai mutane a gidan.?"
Isiya ya faɗa cike da mamaki, Baba jin hakan bai ƙara cewa komai ba ya shiga gidan suka bishi a baya.
Bayan sun zazzauna suka faɗa mishi abin da ya faru, bayan sunje gidan iyayen Sa'idu.
"Yanzu babu yanda za a ɓullowa lamarin.?" Baba ya faɗa yana jin tashin hankalin sa na ƙaru, domin wallahi zaman Ajwa a gidan shi babu alkhairi.
"Duk yanda zamu shawo lamarin abin yaƙi domin mahaifiyar Sa'idu ta ɗauki zafi sosai, maganar gaskiya dole ne su ɗau zafi da lamarin, yarinya sai ka ce ana kaɗata da ruwan hanji." Isiya ya faɗa cike da takaici,
Baba dai ya yi shiru yana sauraron su.
Haka dai suka tafi babu wata magana mai daɗi, domin dai mahaifiyar Sa'idu ta ce lallai sai sun ko yawa ƴarsu hankali sannan zata cigaba da zaman aure da Sa'idu.
Ajwa duniya sabuwa ta buɗe da zaran Baba ya fita kasuwa zata fice maƙota, sai lokacin data san yana gab da shigowa gida take dawowa.
Hajiya ta turo ƴaƴanta su duba Aysar da jiki, lokacin da za su tafi yaran suka fashe da kuka suna roƙonsu dan Allah su tafi dasu, Baba yana kasuwa Hajiya ta kira shi ta faɗa mishi yanda ake ciki, sannan ta roƙi alfarmar ya barsu su zo suga mahaifiyarsu ƙila idan ta gansu hankalinta ya dawo jikinta.
Baba ya yi na'am da maganar surukar shi, suka haɗawa yaran kaya suka kulle ƙofar suka tafi dasu.
Lokacin da Mamy taga yanda yaran suka koma, kuka ta ringa yi domin gaba ɗaya sun fita hayyacinsu, lokacin l'''da suka zo cin abinci taga yanda suke ci kamar mayunwata, bata iya zama a gurin ba ɗaki ta koma.
Hajiya ta ɗibo abinci ta biyota dashi, sai da ta tabbatar taci abincin ta ƙoshi sannan ta ce.
"Kinga makomar rayuwar ƴaƴanki, kinga abin da nake ta gaya miki koh,? Bana matsa miki bane amman ina son ki gane gaskiya, duk lalacewar zubar ɗaki wallahi yafi waje."
Hajiya harta kai bakin ƙofa sannan ta tsaya.
"Idan kin zaɓi ki zubar da rayuwar yaranki, to shi kuma wanda bai zo duniyar ba yaya makomar tashi rayuwar." Hajiya ta faɗa tana janyo mata ƙofar .
Mamy a zabure ta miƙa tana maimaita zancen ƙarshe da taji Hajiya ta faɗa.
Tashin hankali wanda ba a saka mishi rana, shin mai Hajiya take nufi da wannan zancen, shine abin da Mamy take mai maitawa.
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un, ba dai ciki bane a jikina." Mamy ta faɗa tana tuna last period ɗinta.
Ta Batulu ce ✍️...............*WANI SHARRIN*
(Mutum ke nemowa kansa)
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6euGfDTkK50GtWht0G
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION (J.W.A)*
*TEAM JAJIRTATTUN MARUBUTA*
*ALLAHUMMA SALLI ALA SAYYADINA MUHAMMAD WASSALIM*
Written by ✍️
Sa'adatu Ta Batulu
(Jagabar Jajirtattu)
"Ki shirya anjima zaki koma ɗakin ki."
Ta turo baki tana ɓata fuska ya yi kamar bai ganta ba, domin yanda yake ji wallahi zai iya zane ta saboda haushinta yake ji.
"Duk cikin ku babu wanda aka taɓa yiwa horan yunwa a gidan nan, amman shi ne zaku ringa hora ƙananun yara da yunwa koh.? Saboda kun zama mugaye marasu tausayi, to daga yau ba zan ƙara ɗaukar wannan iskancin ba, idan kuma kun ƙi ji wallahi zan ɗauki mummunar mataki akan ku." Ta inda yake shiga bata nan yake fita ba.
Daga ƙarshe ya jefa musu dubu ɗaya yana umartar su.
"A dafa mun macaroni da kifi yanzu." Yana gama faɗa ya bar gidan gaba ɗaya.
Ajwa ta riƙe baki tana cewa.
"Yaushe Baba ya zama hakan.?"
"Tun bayan tafiyar Inna." A'isha ta faɗa tana ɗaukar dubu ɗayan.
Suka dafa macaronin gaba ɗaya gida, saboda ba zasu iya tambayar shi kuɗin cefane ba.
A ɗan ƙaramin roba suka zubawa Yusra da ƙaninta.
Yusra ta fito tana raɓe raɓe Ajwa ta janyo ta.
"Shegiyya mai baƙin hali irin na uwarta." ta faɗa tana hararan ta, ita fa a rayuwar ta wallahi ta tsani wannan yarinyar.
Sai da ta gama zaginta sannan ta miƙa nuna mata robobin abincin su tana faɗin.
"Dangin mayu ɗauka kar ku cinye mu ɗanye."
"Sai dai ko ubanki shi ne dangin mayun." Baba ya faɗa yana shigowa gidan.
Yusra ta ɗau abincin ya kirata ya kalli ɗan abincin dake roban, ƙwafa ya yi yana shiga ɗakin shi.
Yusra data kusa shiga ɗakinsu Ajwa ta dakatar da ita tana faɗin.
"Dan ubanki zoki ɗauki abincin nan ki kai mishi." Ta ta dawo ta ɗau flask ɗin ta shiga ɗakin haɗe da sallama.
Baba ya ƙirƙiro murmushi yana tambayarta jikin Aysar, tayi murmushi tana cewa.
"Da sauƙi." ta ajiye ta flask ta fita.
Abincin su ta ɗauka ta shiga ɗaki Aysar yana kallon ɗan abincin ya fashe da kuka, ta ƙara mishi da nata sannan ya yi shiru, ta zuba mishi ido tana tuna maganar da Mamy ta gaya mata ranar da zata bar gidan, taji an dafa ta.
"Haba yarinyar kirki tunanin mai kike yi inata sallama ko motsi baki yi ba Aysar nata miki surutu kin yi banza dashi."
"Baba dan Allah ka kaimu gurin Mamy, ko kuma ka ce mata ta dawo." Yusra ta faɗa tana fashewa da kuka.
"Ko ɗazun naje gidan Mamyn kuma ta ce tana nan dawo in sha Allah." Bayan ya faɗi maganar ya kau da kai.
Sai da ya tabbatar sunyi shiru sannan ya ajiye musu flask ɗin abincin shi, Yusra ta ɗauko babban plate ta zuba musu abincin rabi, suka zauna suna ci Baba yana bawa Aysar a baki.
Hannu baka hannu ƙwarya haka ta ringa cin abincin, daga ƙarshe Baba ya cire hannunshi ya zubawa Yusra ido.
Kaɗan suka rage abincin Baba ya rufe ya ajiye ta gyara gurin Yusra.
"Kuje kuyi alwala kuyi sallah zan tafi masallaci, sannan ku rufe ƙofa idan na dawo zanyi magana sai ku buɗe." Baba ya ce yana fita daga ɗakin.
Bayan an idar da sallah ƴan uwan Baba suka kira shi a waya suka sanar dashi suna jiranshi a gida.
A zaure Baba ya gansu suna tsaye.
"Ya baku shiga gidan ba kuka tsaya a waje?."
Baba ya faɗa cike da mamaki.
"Daman akwai mutane a gidan.?"
Isiya ya faɗa cike da mamaki, Baba jin hakan bai ƙara cewa komai ba ya shiga gidan suka bishi a baya.
Bayan sun zazzauna suka faɗa mishi abin da ya faru, bayan sunje gidan iyayen Sa'idu.
"Yanzu babu yanda za a ɓullowa lamarin.?" Baba ya faɗa yana jin tashin hankalin sa na ƙaru, domin wallahi zaman Ajwa a gidan shi babu alkhairi.
"Duk yanda zamu shawo lamarin abin yaƙi domin mahaifiyar Sa'idu ta ɗauki zafi sosai, maganar gaskiya dole ne su ɗau zafi da lamarin, yarinya sai ka ce ana kaɗata da ruwan hanji." Isiya ya faɗa cike da takaici,
Baba dai ya yi shiru yana sauraron su.
Haka dai suka tafi babu wata magana mai daɗi, domin dai mahaifiyar Sa'idu ta ce lallai sai sun ko yawa ƴarsu hankali sannan zata cigaba da zaman aure da Sa'idu.
Ajwa duniya sabuwa ta buɗe da zaran Baba ya fita kasuwa zata fice maƙota, sai lokacin data san yana gab da shigowa gida take dawowa.
Hajiya ta turo ƴaƴanta su duba Aysar da jiki, lokacin da za su tafi yaran suka fashe da kuka suna roƙonsu dan Allah su tafi dasu, Baba yana kasuwa Hajiya ta kira shi ta faɗa mishi yanda ake ciki, sannan ta roƙi alfarmar ya barsu su zo suga mahaifiyarsu ƙila idan ta gansu hankalinta ya dawo jikinta.
Baba ya yi na'am da maganar surukar shi, suka haɗawa yaran kaya suka kulle ƙofar suka tafi dasu.
Lokacin da Mamy taga yanda yaran suka koma, kuka ta ringa yi domin gaba ɗaya sun fita hayyacinsu, lokacin l'''da suka zo cin abinci taga yanda suke ci kamar mayunwata, bata iya zama a gurin ba ɗaki ta koma.
Hajiya ta ɗibo abinci ta biyota dashi, sai da ta tabbatar taci abincin ta ƙoshi sannan ta ce.
"Kinga makomar rayuwar ƴaƴanki, kinga abin da nake ta gaya miki koh,? Bana matsa miki bane amman ina son ki gane gaskiya, duk lalacewar zubar ɗaki wallahi yafi waje."
Hajiya harta kai bakin ƙofa sannan ta tsaya.
"Idan kin zaɓi ki zubar da rayuwar yaranki, to shi kuma wanda bai zo duniyar ba yaya makomar tashi rayuwar." Hajiya ta faɗa tana janyo mata ƙofar .
Mamy a zabure ta miƙa tana maimaita zancen ƙarshe da taji Hajiya ta faɗa.
Tashin hankali wanda ba a saka mishi rana, shin mai Hajiya take nufi da wannan zancen, shine abin da Mamy take mai maitawa.
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un, ba dai ciki bane a jikina." Mamy ta faɗa tana tuna last period ɗinta.
Ta Batulu ce ✍️...............*WANI SHARRIN*
(Mutum ke nemowa kansa)
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6euGfDTkK50GtWht0G
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION (J.W.A)*
*TEAM JAJIRTATTUN MARUBUTA*
*ALLAHUMMA SALLI ALA SAYYADINA MUHAMMAD WASSALIM*
Written by ✍️
Sa'adatu Ta Batulu
(Jagabar Jajirtattu)