Chapter 3
Wani Sharrin Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Baba ya zauna a kujera Khadijah ta zauna a ƙasa.
Mamy tayi sallama ta shigo hannunta ɗauke da babban plate mai ɗauke da plas ɗin abinci da jug ɗin ruwa ta aje.
"Khadijah ta lafiya.?" Baba ya faɗa yana tsare ta da ido.
"Yau ba a bamu abinci ba." Khadijah ta faɗa tana share hawaye.
Baba ya tsare Mamy dake zuba mishi abinci a plate, ya ce.
"Mai ya faru, kika hana su abinci.?"
"Nayi ta magana su zo su ɗau abinci, amman su kai banza dani." Mamy ta faɗa tana zama a kusa dashi.
"Ba muji kiran da tai mana ba." Khadijah ta faɗa tana share hawaye.
"Mai yasa da kika ji shiru baki ɗauki abincin kin kai musu ba.?" Baba ya faɗa yana ɗaure fuska.
"Saboda zaman su nake yi, dole in bisu da abinci ɗaki." Mamy ta faɗa cike da jin haushi.
"Wai dan Allah mai yasa bakya ƙaunar zaman lafiya ne.?" Baba ya faɗa yana tsareta da idanu Mamy tayi shiru, Baba ya kalli Khadijah dake zaune kamar munafuka.
"Jeki ɗauki abincin naku." Baba ya faɗa yana ɗaukar plate ɗin da aka zuba abinci, Khadijah ta fita tana tura baki.
Baba sai da ya gama cin abinci yasha ruwa sannan ya kalli Mamy.
"Wai dan Allah mai yasa bakya ƙaunar yaran nan.?" Baba ya faɗa cike da tausasawa.
"Yanzu kana nufin bana ƙaunar yaranka.?" Mamy ta faɗa cike da mamaki.
"Ƙwarai kuwa domin da kina ƙaunarsu baza ki barsu da yunwa ba." Baba ya faɗa yana fita a ɗakin.
"Allah ya kyauta." Mamy ta faɗa tana gyara gurin da Baba yaci abinci.
Haka zaman ya ka san ce tsakanin Mamy da su Khadijah, kullum da salon iskancin da zasu fito dashi, Mamy ko kallo basu isheta ba, idan Yusra ta fito su kama ta su daka Aysar tun da yaga hakan ya daina fitowa shi kaɗai, idan Baba ya yi magana su ce rashin kunya suke yi musu, Mamy data fahimci abin zalunci ne sai ta koma duk in da za suje zata rakasu, har toilet idan zasu shiga Mamy ke rakasu Mamy tana kawar da kai amman tana cutuwa, kuma Baba har kullum ganin laifinta yake yi akan bata ƙaunar ƴaƴanshi.
Mamy na zaune a parlour tana yan kewa Yusra ƙumba taji an yi sallama, A'isha dake zaune a tsakar gidan tana wanki ta amsa sallamar suka gaisa, sannan baƙuwar ta ce.
"Dan Allah umman Yusra tana nan.?"
"A'a bata nan." Khadijah dake fitowa daga ɗaki ta faɗa.
"Dan Allah ko tayi nisa ne.?" Baƙuwar ta faɗa tana shirin fita.
"Mu ma bamu san inda taje ba." A'ishah ta faɗa tana hararan ta.
Baƙuwar ta juya zata fita taji muryan Mamy a bayan ta tana faɗin.
"Maman Abdul." Cak baƙuwar ta tsaya ta juyo cike da mamaki, Mamy tayi murmushi ta riƙo hannun ta suka shige ɗaki.
Mamy da baƙuwar suka zauna a two seater Yusra ta ɗibo ruwa a jug ta ajiye mata, ta duƙa har ƙasa ta gaisheta sannan ta shige bedroom.
"Amman gaskiya yaran can basu da mutunci wallahi." Maman Abdul ta faɗa tana shan ruwan da Yusra ta ajiye.
"Uhm Allah ya kyauta." Mamy ta faɗa tana kawar da maganar.
Maman Abdul ƙanwar Mamy ne uwa ɗaya uba ɗaya.
Sai dare Maman Abdul ta tafi gida bayan anyi sallahr isha'i, Baba ya dawo gida kamar yanda ya saba Mamy ta tafi room ɗin Baba.
Yana zaune yana kaɗa ƙafa cike da rashin mutunci, tayi sallama ta shiga tayi mishi barka da zuwa, Baba ko kallon gurin da take bai yi ba, domin ƙiris yake jira daman.
Mamy ta shiga toilet tayi alwala tazo ta kwanta, Baba abin yaji ya ƙara ɓata mishi rai.
"Wai dan Allah mai ke damunki ne.?" Baba ya faɗa yana hararanta.
"Abban Yusra dan Allah maine ne lafina a gidan nan.?" Mamy ta faɗa hawaye na zubowa daga cikin idanunta.
"Saboda bakya sona, domin duk wanda baya son naka ai kai ne baya so a fakaice." Baba ya faɗa still yana hararanta.
"Yanzu kuma laifin mai na yi.?" Mamy ta faɗa tana jin zuciyarta na zafi.
"Ɗazun keda ƴar uwarki kun haɗu kun zage mun yara kunci musu mutunci, wannan abin kunya ne wallahi kema fa kina da yaran, sannan har kina hana su abinci bayan kuma ubansu ya nemo abincin." Baba ya faɗa a hassale.
"Zan jure duk wani cin mutunci da cin fuska daga gareka, amman wallahi ba zan lamunci hakan daga yaranka ba, abubuwa da yawa kayi mun wanda ya dace inyi zuciya in rabu dakai, amman ban yi hakan ba a cikin ƴan uwana babu wanda ya san halin da nake ciki, ka ƙwace girkina ka bata yaranka su zageni mahaifiyarsu tayi mun kaima kazo ka ɗaura daga inda suka tsaya, to wallahi ba zan ɗauka ba yanzu shirun da nayi ba tsoro nake ji ba." Mamy ta faɗa tana shirin barin ɗakin, daman da hijjab a jikin ta.
Baba ya riƙo ta yana faɗin.
"Haka kika ce koh.?"
Mamy cike da ɓacin rai ta ce.
"Eh haka na faɗa."
"Aiko zaki tafi gidan ubanki, domin wallahi ba a haifi matar da zata hora mun yara ba." Baba ya faɗa yana shigewa toilet.
Cike da furgicin furucin daya furta Mamy tabi shi da ido har ya shige.
Mamy ta share hawayen fuskan ta sannan ta ce.
"Aiko zan bar maka gidanka kamar yanda ka faɗa."
"Idan kin tashi tafiya karki tafi mun da yarana, domin ba a kawo ki dasu ba." Baba ya faɗa daga cikin toilet.
"Daman babu inda zanje maka da yara, dole su zauna a gidan ubansu." Daga hakan ta fita, ɗakinta ta koma ta ƙwanƙwasa Yusra ta buɗe mata ƙofa ta shiga, kai tsaye bedroom ta nufa ta sauko da akwati ta shirya kayanta, sannan ta zaunar da Yusra Aysar yana ta bacci abin shi.
"Duk rintsi duk wuya ki kula da ɗan uwanki, ki zame mishi innuwa a duk inda yake." Mamy ta faɗa hawaye masu zafi na zubowa daga idonta.
"Mamy ina za kije da daddaren nan.?" Yusra ta faɗa tana hawaye.
"Yusra zama na da mahaifinki ya ƙare, zan tafi namu gidan." Mamy ta faɗa tana tusayin rayuwar da zata bar ƴaƴanta.
"Mamy dan Allah ki tafi damu." Yusra ta ce tana fashewa da kuka.
Mamy ta rarrashi Yusra har sai dai ta yi bacci, sannan ta kwantar da ita ta kwashe akwatin ta fita, ta tsaya a bakin ƙofa ta kalli yaran.
"Allah ka tsare mun yarana a duk inda suke."
Mamy ta furta tana barin ɗakin, Khadijah da A'ishah na tsaye a window suna leƙen tsakar gidan, suna hango Mamy suka ce.
"Allah ya kiyaye hanya."
Mamy tayi murmushi ta ja akwatin tana faɗin.
"Ƴaƴa mata kuke masu rayuwa a ƙarƙashin wani."
Daga haka Mamy ta fita napep ta samu ta faɗa mishi inda zai kai ta.
Sun yi tafiya mai tsawo kafin ya tsaya a bakin wani babban gida, get ɗin gidan coffee ne.
Mamy ta fito mai napep ya ciro mata akwatin, ya ajiye mata kuɗi ta ɗauko masu yawa ta miƙa mishi, mai napep yana ta zabga godiya Mamy hankalinta baya jikinta, gaba ɗaya tunaninta na gurin yaranta.
Mai gadi ya buɗe kofar ta shiga ciki ya biyota da akwatin kayanta, babban gida ne part biyu ɗaya babba ɗaya ƙarami, sai rumfar ajiye motoci.*WANI SHARRIN*
(Mutum ke nemowa kansa)
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
*(J.W.A)*
*TEAM JAJIRTATTUN MARUBUTA✊*
Written by ✍️
Jagabar Jajirtattu
Allahumma salli ala sayyadina Muhammad wassalim.
Mamy tayi sallama ta shigo hannunta ɗauke da babban plate mai ɗauke da plas ɗin abinci da jug ɗin ruwa ta aje.
"Khadijah ta lafiya.?" Baba ya faɗa yana tsare ta da ido.
"Yau ba a bamu abinci ba." Khadijah ta faɗa tana share hawaye.
Baba ya tsare Mamy dake zuba mishi abinci a plate, ya ce.
"Mai ya faru, kika hana su abinci.?"
"Nayi ta magana su zo su ɗau abinci, amman su kai banza dani." Mamy ta faɗa tana zama a kusa dashi.
"Ba muji kiran da tai mana ba." Khadijah ta faɗa tana share hawaye.
"Mai yasa da kika ji shiru baki ɗauki abincin kin kai musu ba.?" Baba ya faɗa yana ɗaure fuska.
"Saboda zaman su nake yi, dole in bisu da abinci ɗaki." Mamy ta faɗa cike da jin haushi.
"Wai dan Allah mai yasa bakya ƙaunar zaman lafiya ne.?" Baba ya faɗa yana tsareta da idanu Mamy tayi shiru, Baba ya kalli Khadijah dake zaune kamar munafuka.
"Jeki ɗauki abincin naku." Baba ya faɗa yana ɗaukar plate ɗin da aka zuba abinci, Khadijah ta fita tana tura baki.
Baba sai da ya gama cin abinci yasha ruwa sannan ya kalli Mamy.
"Wai dan Allah mai yasa bakya ƙaunar yaran nan.?" Baba ya faɗa cike da tausasawa.
"Yanzu kana nufin bana ƙaunar yaranka.?" Mamy ta faɗa cike da mamaki.
"Ƙwarai kuwa domin da kina ƙaunarsu baza ki barsu da yunwa ba." Baba ya faɗa yana fita a ɗakin.
"Allah ya kyauta." Mamy ta faɗa tana gyara gurin da Baba yaci abinci.
Haka zaman ya ka san ce tsakanin Mamy da su Khadijah, kullum da salon iskancin da zasu fito dashi, Mamy ko kallo basu isheta ba, idan Yusra ta fito su kama ta su daka Aysar tun da yaga hakan ya daina fitowa shi kaɗai, idan Baba ya yi magana su ce rashin kunya suke yi musu, Mamy data fahimci abin zalunci ne sai ta koma duk in da za suje zata rakasu, har toilet idan zasu shiga Mamy ke rakasu Mamy tana kawar da kai amman tana cutuwa, kuma Baba har kullum ganin laifinta yake yi akan bata ƙaunar ƴaƴanshi.
Mamy na zaune a parlour tana yan kewa Yusra ƙumba taji an yi sallama, A'isha dake zaune a tsakar gidan tana wanki ta amsa sallamar suka gaisa, sannan baƙuwar ta ce.
"Dan Allah umman Yusra tana nan.?"
"A'a bata nan." Khadijah dake fitowa daga ɗaki ta faɗa.
"Dan Allah ko tayi nisa ne.?" Baƙuwar ta faɗa tana shirin fita.
"Mu ma bamu san inda taje ba." A'ishah ta faɗa tana hararan ta.
Baƙuwar ta juya zata fita taji muryan Mamy a bayan ta tana faɗin.
"Maman Abdul." Cak baƙuwar ta tsaya ta juyo cike da mamaki, Mamy tayi murmushi ta riƙo hannun ta suka shige ɗaki.
Mamy da baƙuwar suka zauna a two seater Yusra ta ɗibo ruwa a jug ta ajiye mata, ta duƙa har ƙasa ta gaisheta sannan ta shige bedroom.
"Amman gaskiya yaran can basu da mutunci wallahi." Maman Abdul ta faɗa tana shan ruwan da Yusra ta ajiye.
"Uhm Allah ya kyauta." Mamy ta faɗa tana kawar da maganar.
Maman Abdul ƙanwar Mamy ne uwa ɗaya uba ɗaya.
Sai dare Maman Abdul ta tafi gida bayan anyi sallahr isha'i, Baba ya dawo gida kamar yanda ya saba Mamy ta tafi room ɗin Baba.
Yana zaune yana kaɗa ƙafa cike da rashin mutunci, tayi sallama ta shiga tayi mishi barka da zuwa, Baba ko kallon gurin da take bai yi ba, domin ƙiris yake jira daman.
Mamy ta shiga toilet tayi alwala tazo ta kwanta, Baba abin yaji ya ƙara ɓata mishi rai.
"Wai dan Allah mai ke damunki ne.?" Baba ya faɗa yana hararanta.
"Abban Yusra dan Allah maine ne lafina a gidan nan.?" Mamy ta faɗa hawaye na zubowa daga cikin idanunta.
"Saboda bakya sona, domin duk wanda baya son naka ai kai ne baya so a fakaice." Baba ya faɗa still yana hararanta.
"Yanzu kuma laifin mai na yi.?" Mamy ta faɗa tana jin zuciyarta na zafi.
"Ɗazun keda ƴar uwarki kun haɗu kun zage mun yara kunci musu mutunci, wannan abin kunya ne wallahi kema fa kina da yaran, sannan har kina hana su abinci bayan kuma ubansu ya nemo abincin." Baba ya faɗa a hassale.
"Zan jure duk wani cin mutunci da cin fuska daga gareka, amman wallahi ba zan lamunci hakan daga yaranka ba, abubuwa da yawa kayi mun wanda ya dace inyi zuciya in rabu dakai, amman ban yi hakan ba a cikin ƴan uwana babu wanda ya san halin da nake ciki, ka ƙwace girkina ka bata yaranka su zageni mahaifiyarsu tayi mun kaima kazo ka ɗaura daga inda suka tsaya, to wallahi ba zan ɗauka ba yanzu shirun da nayi ba tsoro nake ji ba." Mamy ta faɗa tana shirin barin ɗakin, daman da hijjab a jikin ta.
Baba ya riƙo ta yana faɗin.
"Haka kika ce koh.?"
Mamy cike da ɓacin rai ta ce.
"Eh haka na faɗa."
"Aiko zaki tafi gidan ubanki, domin wallahi ba a haifi matar da zata hora mun yara ba." Baba ya faɗa yana shigewa toilet.
Cike da furgicin furucin daya furta Mamy tabi shi da ido har ya shige.
Mamy ta share hawayen fuskan ta sannan ta ce.
"Aiko zan bar maka gidanka kamar yanda ka faɗa."
"Idan kin tashi tafiya karki tafi mun da yarana, domin ba a kawo ki dasu ba." Baba ya faɗa daga cikin toilet.
"Daman babu inda zanje maka da yara, dole su zauna a gidan ubansu." Daga hakan ta fita, ɗakinta ta koma ta ƙwanƙwasa Yusra ta buɗe mata ƙofa ta shiga, kai tsaye bedroom ta nufa ta sauko da akwati ta shirya kayanta, sannan ta zaunar da Yusra Aysar yana ta bacci abin shi.
"Duk rintsi duk wuya ki kula da ɗan uwanki, ki zame mishi innuwa a duk inda yake." Mamy ta faɗa hawaye masu zafi na zubowa daga idonta.
"Mamy ina za kije da daddaren nan.?" Yusra ta faɗa tana hawaye.
"Yusra zama na da mahaifinki ya ƙare, zan tafi namu gidan." Mamy ta faɗa tana tusayin rayuwar da zata bar ƴaƴanta.
"Mamy dan Allah ki tafi damu." Yusra ta ce tana fashewa da kuka.
Mamy ta rarrashi Yusra har sai dai ta yi bacci, sannan ta kwantar da ita ta kwashe akwatin ta fita, ta tsaya a bakin ƙofa ta kalli yaran.
"Allah ka tsare mun yarana a duk inda suke."
Mamy ta furta tana barin ɗakin, Khadijah da A'ishah na tsaye a window suna leƙen tsakar gidan, suna hango Mamy suka ce.
"Allah ya kiyaye hanya."
Mamy tayi murmushi ta ja akwatin tana faɗin.
"Ƴaƴa mata kuke masu rayuwa a ƙarƙashin wani."
Daga haka Mamy ta fita napep ta samu ta faɗa mishi inda zai kai ta.
Sun yi tafiya mai tsawo kafin ya tsaya a bakin wani babban gida, get ɗin gidan coffee ne.
Mamy ta fito mai napep ya ciro mata akwatin, ya ajiye mata kuɗi ta ɗauko masu yawa ta miƙa mishi, mai napep yana ta zabga godiya Mamy hankalinta baya jikinta, gaba ɗaya tunaninta na gurin yaranta.
Mai gadi ya buɗe kofar ta shiga ciki ya biyota da akwatin kayanta, babban gida ne part biyu ɗaya babba ɗaya ƙarami, sai rumfar ajiye motoci.*WANI SHARRIN*
(Mutum ke nemowa kansa)
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
*(J.W.A)*
*TEAM JAJIRTATTUN MARUBUTA✊*
Written by ✍️
Jagabar Jajirtattu
Allahumma salli ala sayyadina Muhammad wassalim.