Chapter 1
Wani Sharrin Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Dubanin jama'a ne suka shaida ɗaurin auren Ajwa Usman da angonta Sa'idu Hashim.
Wani yaro ya shigo gidan yana shailar an ɗaura auren yanzu.
Inna Talatu da yara ke kiranta da Inna ta fito tsakar gida tana rangaɗa buɗa tana faɗin.
"Aure ya ɗauru ƴan baƙin ciki sai dai su mutu." Inna sai habaice habaice take yi amarya Ajwa tana yiwa mahaifiyarta kirari cike da alfahari.
Ganin abin ba mai ƙarewa bane dangin mahaifin Ajwa suka janye amarya domin hakan abin kunya ne a garesu.
Bayan sallar isha'i aka zo da motocin ɗaukar amarya, mahaifin Ajwa ya yi mata nasiha mai ratsa jiki sannan a ƙarshe ya ce.
"Dan Allah dan Annabi ki rufa mun asiri ki zauna lafiya a gidan mijinki, babu ruwanki da abin da bai shafeki ba kar inji kar in gani." Daga haka suka wuce da ita gurin motar da aka ware saboda ɗaukar amarya.
Gidan amarya part biyu ne ɗaya na mahaifiyar Sa'idu ne ɗaya kuma na Ajwa two bedroom ɗaya da toile ɗaya babu toilet, parlourn yasha kujeru saiti masu ruwan ƙasa da ratsin fari labulayen ɗakin ma irin kujerun ne.
Kitchen yana tsakar gida da toilet sai ɗan ƙaramin tsakar gida, yasha siminti gidan daidai zaman talaka ma sha Allah gidan ya yi kyau.
Ƴan kai amarya sun koma gida suna ta santin gidan Ajwa, Inna sai jin daɗi take yi tana yiwa amaryan ta habaici.
Washe garin biki kowa ya watse ƴan uwan mahaifin Ajwa na nesa basu koma ba, amaryar Inna mai suna Raliya amman yara suna kiranta da Mamy, tayi sallama ɗakin Inna suka gaisa da raguwan mutanen da basu koma gidajensu ba, daga nan ta zauna suka ɗan taɓa fira tayi sallama ta koma ɗakinta.
Bayan sati ɗaya da bikin Ajwa amarya tana zaune lafiya da mijinta da uwar mijinta, Sa'idu ya fahimci amaryansa bata san addini ba gaba ɗaya, tun a nan suka fara samun matsala da mijin.
Sa'idu ya fahimci Ajwa tana da taurin kai sai ya rabu da ita, bayan sallar magrib yake biya mata ƙawa'idi da ahalari.
Ajwa tana da kirki sosai sannan kuma tana son dangin mijinta, amman idan ka taɓa ta fitinanniya ce lamba ɗaya, sannan bata son zama guri ɗaya mace ne mai son yawo, bata da matsala da uwar mijinta domin tana ƙoƙarin kyautata mata, amman fa itama uwar mijin ba kanwar lasa bace idan ka ta ɓata.
Yau girkin Mamy ne Alhaji Usman wanda yara suke kira da Baba, ya yi sallama ya shigo room ɗin Mamy tana zaune tana chart a saman kujera.
Room ɗin yasha turaren wuta yana ta ƙamshi, parlourn na ɗauke da saitin kujeru black and white labulayen ɗakin ma haka.
"Talatu zata yi tafiya kuma tana san girki ya dawo hannunta, har zuwa lokacin tafiyar nata." Baba ya faɗa yana zama a ɗaya daga cikin kujerun parlour.
A zabure Mamy ta miƙa tana kallon Baba cike da mamakin furucin bakin shi.
"Bangane abin da kake nufi ba." Mamy ta faɗa murya na rawa.
"Talatu zata yi tafiya kuma tana son a rama mata kwanakin girkinta, idan ta tafi girkin sai ya dawo hannunki gaba ɗaya har zuwa lokacin da zata dawo." Baba ya faɗa yana danne danne a wayarshi.
"Amman dan Allah a ina a ka taɓa jin irin wannan, sai ka ce muna garin arna." Mamy ta faɗa tana jin jina rainin hankalin Talatu.
"Kina nufin nine arnen ko Talatu.?" Baba ya faɗa a fusace.
Mamy ta fashe da kuka tana cewa.
"Wallahi ban yarda ba sai dai ta fasa tafiyar."
"Shawara ya rage naki, domin na gama magana." Baba ya faɗa yana fita daga room ɗin.
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un, wannan wace irin masifa ce." Mamy ta faɗa hawaye masu zafi na zuba daga cikin idanunta.
Mamy tayi alwala ta ɗau Qur'ani yaranta Yusra da Aysar suka kewaye ta, Mamy tana karatu tana hawaye, sai da taji zuciyarta ya yi sanyi sannan ta ajiye Qur'anin tayi nafila, sai da ta tabbatar zuciyarta ya yi sanyi sannan ta miƙe ta shige bedroom, Yusra ƴar shekara goma tabi bayanta Aysar ɗan shekara bakwai ya fita zuwa gurin Baba.
Aysar yana fita suka haɗu da Zainab a tsakar gida.
"Zo nan dan uwarka."
Aysar ya zura da gudu ya koma ɗaki, Zainab tayi ƙwafa tana cewa.
"Zaka san na kiraka ka gudu."
Bayan sallar azahar Inna ta aiko Zainab amsar kwanon abinci, a bakin ƙofa ta tsaya tana tsaki, Aysar ya fito zai yi alwala Zainab ta riƙo shi ta zabga mishi mari guda biyu sannan ta ranƙwashe shi tana cewa.
"Shege mai baƙin hali irin na uwarsa."
Mamy na zaune a parlour tana kallon abin da ke faruwa, amman tayi kamar bata gani ba, domin idan ta ce zata yi magana ƙarshe abin ya koma kanta.
Aysar ya fashe da kuka Yusra zata fita Mamy ta hana.
"Kwanon abinci." Zainab ta faɗa tana hararan ƙofar ɗakin.
Yusra ta ɗau flas ɗin Mamy da kwanoni guda biyu ta fita, Aysar na duƙe yana kuka ta riƙo hannun shi tana share mishi hawaye, Zainab ta bigeta ta wuce da sauri Yusra ta dafe bango, Mamy ta share hawayen fuskarta sannan ta fito, hannun Aysar ta riƙo tana share mishi hawaye.
Mamy ta shiga da Aysar ɗaki Yusar kuma taje kai kayan abincin, Inna Zainab Khadijah A'isha dukkan su yaran Inna ne Ajwa ita ce babba a gidan.
Yusra jiki na rawa ta ajiye kayan hannunta zata koma, taji an daka mata tsawa an ce.
"Uban waye sa'an wasanki a gurin nan." Khadijah ce take wannan maganar.
Yusra ta dawo ta zauna fuskanta cike da hawaye.
"Shegiyya mai baƙin hali." A'isha ta faɗa tana ranƙwashinta a kai, Yusra ta dafe kai tana hawaye.
"Wallahi idan baki shanye wannan hawayen ba, yanzu zan saki mai dalili." Zainab ta faɗa tana hararan ta.
Mamy duk tana sauraron abin da ke faruwa, kuma ta fahimci zasu iya haɗuwa su zane mata yarinya kamar yanda suka saba, Mamy ta fita zuwa tsakar gidan ta kira Yusra.
Duk wannan abin dake faruwa Inna tana zaune tana raba abinci, kuma bata hana su ballantana ta tsawatar musu.
20 minutes da shigarsu ɗaki Zainab ta kira Yusra a kan tazo ta kwashi abincin su.
Kwanon Aysar ba a zuba komai ba Mama ta kalli Yusra, dake kallon kwanon abincin ƙaninta ta ce.
"Sai da nagama rabo na tuna dashi, dan haka kuyi maneji."
Yusra bata ce komai ba ta shiga ɗaki, ta ajiye abincin a gaban Mamy sannan ta faɗa mata yanda suka yi da Inna.
Mamy ta haɗa musu abincin duka harda nata, suka zauna suka ci amman basu ƙoshi ba, kasancewar abincin ba wani na kirki bane.
Mamy ta ɗauko ƙaramin murhu ta kunna gawayi bayan ya tashi ta ajiye a bakin ƙofa, taliya ta dafa da mai da yaji ta zuba wa yaran sannan ta zuba nata.
Bayan sun gama ci Yusra ta fita da kwanonin da suka ɓata, ta haɗa wanke wanken gaba ɗaya ta wanke Aysar na ɗaurayewa, ta kwashe kawonin zata shiga ɗaki Zainab data zo wucewa ta tureta, kwanonin da suka suka zube ta faɗa a kan su har da wuƙa.
Yusra jin zafi har cikin ƙwaƙwalwar kan ta yasa ta ƙwalla ihu, da sauri Zainab ta shige ɗaki.
Mamy ta fito da sauri ganin Yusra kwance a saman kayan wanke wanke tana kuka, yasa tayi saurin ƙarasawa gurin.
"Garin yaya kika faɗi, kamar bakya gani." Mamy ta faɗa tana riƙota.
Da sauri Yusra ta duƙa tana dafe gefen cikinta, Aysar dake ƙoƙarin kwashe kayan da ya zube ya kalli Mamy a furgice yana cewa.
"Lah Mamy jini a cikin Aunty."
Hankali tashe Mamy ta kai idununta gurin da Aysar yake nuna wa, tabbas jini ne yake ɗiga kaɗan kaɗan ajikin Yusra.
Daman da hijjab a jikin Mamy da sauri ta ɗauko Yusra tayi hanyar waje da ita Aysar ya bita da gudu.
Mamy chemis ta nufa hankali tashe tana tafe tana haɗa hanya, domin ko ganin gabanta bata yi saboda tashin hankali.
Ta Batulu ce..........✍️*WANI SHARRIN*
Mutum ke nemowa kansa
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
*(J.W.A)*
*TEAM JAJIRTATTUN MARUBUTA*
Written by ✍️
Jagabar Jajirtattu
Allahumma salli ala sayyadina Muhammad wassalim.
Wani yaro ya shigo gidan yana shailar an ɗaura auren yanzu.
Inna Talatu da yara ke kiranta da Inna ta fito tsakar gida tana rangaɗa buɗa tana faɗin.
"Aure ya ɗauru ƴan baƙin ciki sai dai su mutu." Inna sai habaice habaice take yi amarya Ajwa tana yiwa mahaifiyarta kirari cike da alfahari.
Ganin abin ba mai ƙarewa bane dangin mahaifin Ajwa suka janye amarya domin hakan abin kunya ne a garesu.
Bayan sallar isha'i aka zo da motocin ɗaukar amarya, mahaifin Ajwa ya yi mata nasiha mai ratsa jiki sannan a ƙarshe ya ce.
"Dan Allah dan Annabi ki rufa mun asiri ki zauna lafiya a gidan mijinki, babu ruwanki da abin da bai shafeki ba kar inji kar in gani." Daga haka suka wuce da ita gurin motar da aka ware saboda ɗaukar amarya.
Gidan amarya part biyu ne ɗaya na mahaifiyar Sa'idu ne ɗaya kuma na Ajwa two bedroom ɗaya da toile ɗaya babu toilet, parlourn yasha kujeru saiti masu ruwan ƙasa da ratsin fari labulayen ɗakin ma irin kujerun ne.
Kitchen yana tsakar gida da toilet sai ɗan ƙaramin tsakar gida, yasha siminti gidan daidai zaman talaka ma sha Allah gidan ya yi kyau.
Ƴan kai amarya sun koma gida suna ta santin gidan Ajwa, Inna sai jin daɗi take yi tana yiwa amaryan ta habaici.
Washe garin biki kowa ya watse ƴan uwan mahaifin Ajwa na nesa basu koma ba, amaryar Inna mai suna Raliya amman yara suna kiranta da Mamy, tayi sallama ɗakin Inna suka gaisa da raguwan mutanen da basu koma gidajensu ba, daga nan ta zauna suka ɗan taɓa fira tayi sallama ta koma ɗakinta.
Bayan sati ɗaya da bikin Ajwa amarya tana zaune lafiya da mijinta da uwar mijinta, Sa'idu ya fahimci amaryansa bata san addini ba gaba ɗaya, tun a nan suka fara samun matsala da mijin.
Sa'idu ya fahimci Ajwa tana da taurin kai sai ya rabu da ita, bayan sallar magrib yake biya mata ƙawa'idi da ahalari.
Ajwa tana da kirki sosai sannan kuma tana son dangin mijinta, amman idan ka taɓa ta fitinanniya ce lamba ɗaya, sannan bata son zama guri ɗaya mace ne mai son yawo, bata da matsala da uwar mijinta domin tana ƙoƙarin kyautata mata, amman fa itama uwar mijin ba kanwar lasa bace idan ka ta ɓata.
Yau girkin Mamy ne Alhaji Usman wanda yara suke kira da Baba, ya yi sallama ya shigo room ɗin Mamy tana zaune tana chart a saman kujera.
Room ɗin yasha turaren wuta yana ta ƙamshi, parlourn na ɗauke da saitin kujeru black and white labulayen ɗakin ma haka.
"Talatu zata yi tafiya kuma tana san girki ya dawo hannunta, har zuwa lokacin tafiyar nata." Baba ya faɗa yana zama a ɗaya daga cikin kujerun parlour.
A zabure Mamy ta miƙa tana kallon Baba cike da mamakin furucin bakin shi.
"Bangane abin da kake nufi ba." Mamy ta faɗa murya na rawa.
"Talatu zata yi tafiya kuma tana son a rama mata kwanakin girkinta, idan ta tafi girkin sai ya dawo hannunki gaba ɗaya har zuwa lokacin da zata dawo." Baba ya faɗa yana danne danne a wayarshi.
"Amman dan Allah a ina a ka taɓa jin irin wannan, sai ka ce muna garin arna." Mamy ta faɗa tana jin jina rainin hankalin Talatu.
"Kina nufin nine arnen ko Talatu.?" Baba ya faɗa a fusace.
Mamy ta fashe da kuka tana cewa.
"Wallahi ban yarda ba sai dai ta fasa tafiyar."
"Shawara ya rage naki, domin na gama magana." Baba ya faɗa yana fita daga room ɗin.
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un, wannan wace irin masifa ce." Mamy ta faɗa hawaye masu zafi na zuba daga cikin idanunta.
Mamy tayi alwala ta ɗau Qur'ani yaranta Yusra da Aysar suka kewaye ta, Mamy tana karatu tana hawaye, sai da taji zuciyarta ya yi sanyi sannan ta ajiye Qur'anin tayi nafila, sai da ta tabbatar zuciyarta ya yi sanyi sannan ta miƙe ta shige bedroom, Yusra ƴar shekara goma tabi bayanta Aysar ɗan shekara bakwai ya fita zuwa gurin Baba.
Aysar yana fita suka haɗu da Zainab a tsakar gida.
"Zo nan dan uwarka."
Aysar ya zura da gudu ya koma ɗaki, Zainab tayi ƙwafa tana cewa.
"Zaka san na kiraka ka gudu."
Bayan sallar azahar Inna ta aiko Zainab amsar kwanon abinci, a bakin ƙofa ta tsaya tana tsaki, Aysar ya fito zai yi alwala Zainab ta riƙo shi ta zabga mishi mari guda biyu sannan ta ranƙwashe shi tana cewa.
"Shege mai baƙin hali irin na uwarsa."
Mamy na zaune a parlour tana kallon abin da ke faruwa, amman tayi kamar bata gani ba, domin idan ta ce zata yi magana ƙarshe abin ya koma kanta.
Aysar ya fashe da kuka Yusra zata fita Mamy ta hana.
"Kwanon abinci." Zainab ta faɗa tana hararan ƙofar ɗakin.
Yusra ta ɗau flas ɗin Mamy da kwanoni guda biyu ta fita, Aysar na duƙe yana kuka ta riƙo hannun shi tana share mishi hawaye, Zainab ta bigeta ta wuce da sauri Yusra ta dafe bango, Mamy ta share hawayen fuskarta sannan ta fito, hannun Aysar ta riƙo tana share mishi hawaye.
Mamy ta shiga da Aysar ɗaki Yusar kuma taje kai kayan abincin, Inna Zainab Khadijah A'isha dukkan su yaran Inna ne Ajwa ita ce babba a gidan.
Yusra jiki na rawa ta ajiye kayan hannunta zata koma, taji an daka mata tsawa an ce.
"Uban waye sa'an wasanki a gurin nan." Khadijah ce take wannan maganar.
Yusra ta dawo ta zauna fuskanta cike da hawaye.
"Shegiyya mai baƙin hali." A'isha ta faɗa tana ranƙwashinta a kai, Yusra ta dafe kai tana hawaye.
"Wallahi idan baki shanye wannan hawayen ba, yanzu zan saki mai dalili." Zainab ta faɗa tana hararan ta.
Mamy duk tana sauraron abin da ke faruwa, kuma ta fahimci zasu iya haɗuwa su zane mata yarinya kamar yanda suka saba, Mamy ta fita zuwa tsakar gidan ta kira Yusra.
Duk wannan abin dake faruwa Inna tana zaune tana raba abinci, kuma bata hana su ballantana ta tsawatar musu.
20 minutes da shigarsu ɗaki Zainab ta kira Yusra a kan tazo ta kwashi abincin su.
Kwanon Aysar ba a zuba komai ba Mama ta kalli Yusra, dake kallon kwanon abincin ƙaninta ta ce.
"Sai da nagama rabo na tuna dashi, dan haka kuyi maneji."
Yusra bata ce komai ba ta shiga ɗaki, ta ajiye abincin a gaban Mamy sannan ta faɗa mata yanda suka yi da Inna.
Mamy ta haɗa musu abincin duka harda nata, suka zauna suka ci amman basu ƙoshi ba, kasancewar abincin ba wani na kirki bane.
Mamy ta ɗauko ƙaramin murhu ta kunna gawayi bayan ya tashi ta ajiye a bakin ƙofa, taliya ta dafa da mai da yaji ta zuba wa yaran sannan ta zuba nata.
Bayan sun gama ci Yusra ta fita da kwanonin da suka ɓata, ta haɗa wanke wanken gaba ɗaya ta wanke Aysar na ɗaurayewa, ta kwashe kawonin zata shiga ɗaki Zainab data zo wucewa ta tureta, kwanonin da suka suka zube ta faɗa a kan su har da wuƙa.
Yusra jin zafi har cikin ƙwaƙwalwar kan ta yasa ta ƙwalla ihu, da sauri Zainab ta shige ɗaki.
Mamy ta fito da sauri ganin Yusra kwance a saman kayan wanke wanke tana kuka, yasa tayi saurin ƙarasawa gurin.
"Garin yaya kika faɗi, kamar bakya gani." Mamy ta faɗa tana riƙota.
Da sauri Yusra ta duƙa tana dafe gefen cikinta, Aysar dake ƙoƙarin kwashe kayan da ya zube ya kalli Mamy a furgice yana cewa.
"Lah Mamy jini a cikin Aunty."
Hankali tashe Mamy ta kai idununta gurin da Aysar yake nuna wa, tabbas jini ne yake ɗiga kaɗan kaɗan ajikin Yusra.
Daman da hijjab a jikin Mamy da sauri ta ɗauko Yusra tayi hanyar waje da ita Aysar ya bita da gudu.
Mamy chemis ta nufa hankali tashe tana tafe tana haɗa hanya, domin ko ganin gabanta bata yi saboda tashin hankali.
Ta Batulu ce..........✍️*WANI SHARRIN*
Mutum ke nemowa kansa
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
*(J.W.A)*
*TEAM JAJIRTATTUN MARUBUTA*
Written by ✍️
Jagabar Jajirtattu
Allahumma salli ala sayyadina Muhammad wassalim.