← Book details Shimfidar Mijina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 12

Sashe 9

Shimfidar Mijina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

.

.

Anwar duk wata sai ya tura da kayan abinci nik'i2 gidan su Fateema, hatta tufafi, bai daina aika mata dashi ba, kuma yana haɗawa da kuɗi me tarin yawa, tun bata jure rashin shi har tafara jurewa, ta gama idda da wata ɗaya Maryam ta fara nak'uda, Hajiya Jamila tsaban tsaurin ido tafi kowa ɗoki akan cikin, har gida taje ta nemi yafiyar Maryam akan haɗa mata sharri da ta so yi..
Anwar kam sosai ya manta da kaɗaicin Fateema, yasan dai tana manne a k'asan zuciyar sa amma bawai na kaɗaici ba.

Lokacin da ta fara nak'uda cikin darene, Anwar duk ya ruɗe, tana kuka yana kuka, ganin abun nata yana gaba gabane yasa ya kinkime ta, du k'aton cikinnan baisa yaji wani nauyi ba, mota yasata suka tafi asibiti, duk ta jigata shima ya jikata, da sauri aka sgigar da ita saboda takai matakin k'arshe, minti 10 tsakani aka fito aka shaida masa ta haihu.

🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
*SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏

.

page 16

.
.

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_We dont just entertain and educate we also touch the hearts of readers_

.

.

Writen By *Princess Eshat Aysm*

.

.

.

.

.

Santaleliyar 'yarta mace ta haifa, kyakkyawa me kama da Anwar, murna wajen Anwar da dangin sa ba'a magana, Hajiya Jamila abun nema ya samu, Manya manyan mutane ta gayyata, kuma a lokacin Dadyn Anwar ya dawo, Ansha shagali kamar ba gobe, ansaka wa yarinya suna AISHA!
takwara akayi wa Eshat Aysm, Bichiki Fans ina gani suna taka rawa saboda anyi wa k'anwar su takwara, iyalan gulma saida sukaje wajen taron sunannan su Afeefah, cure Farida, Janan beauty, Ayusha Durln...
Sunada yawa iyalan gulman🙄

Maryam tasha kyautuka sosai, bayan suna k'anwar Momyn ta tace dole fa akai ta wankan gida, fushi sosai Anwar ya shiga yi amma ta ce fir sai Maryam ta tafi wankan gida, abu har yaje gaban mahaifin Anwar, hak'uri ya bashi ya lallaɓa shi ya ce kwana Arba'in ɗin nawane kamar yaune, Hajiya Jamila ta ce "nima shi nagani".
Dady ya ce "kuma ba kanada wata matar ba"?
Da sauri Hajiya ta kalle shi tana k'yafta mishi ido, yayi kamar bai ganta ba, ya ce "Dady ai bata nan, tayi wata 5 a gida yanzu".
Jaridar hanunsa ya ajiye, yamaida nutsuwar sa ga ɗan nasa, "me yafaru"?

Hajiya Jamila tayi caraf ta ce "yarinyar batada kunyane, shiyasa ya saketa".
Dady ya ɗaga mata hanu "Bafa ke na tambaya ba".
Ta tsuk'e bakin ta tayi shiru, Anwar ya ce "Ban saki matata ba, Dady, matsala aka samu....
Sai kuma yayi shiru yana kallon Hajiya, yana so ya rufa mata asiri amma idan ya biyeta Fateemar sa bazata dawo ba kenan, Dady yace "matsalar me zai janyo har ka kasa hak'uri kayi saki, kana yaro dakai kafara saki, idan ba sakiba me zaisa taɗau tsawon lokaci tana gida, bana son shashanci fa Anwar".
Anwar ya sunkuyar dakai yace "Hajiya ce tasan komai".
Harara ta watsa masa "Ni ina uwar taka zakamun sharri"?
Alhaji ya ce "banaso kisake magana Jamila, nasan halinki sarai ba tausayi kike dashi ba, Anwar faɗamun duk abunda yafaru kaji".
Anwar kuwa baiyi k'asa a gwiwa ba yasanar masa duk abunda ya faru, Hajiya har wani ɓari takeyi saboda kaɗuwa, Alhaji ranshi ya gama ɓaci ya ce "kana nufin ba takaddar saki ka bata ba"?

"wallahi ban saki Fateema ba Dady".

Wani kallo Alhaji ya watsa mata ya ce "ke har ɗannaki ma mugunta kike masa, to nima zanyi abu guda ɗaya, matuk'ar auren yaronnan bai gyaruba to wallahi zan sakeki".
Anwar ya ruɗe ya ce "Haba Dad yaya zaka faɗi haka kuma harka rantse, uwata ce fa, ni nayafe mata duk abunda tayi".
Hajiya Jamila kam tuni hawaye ya fara wanke mata fuska, Alhaji ya ce "kidawo masa da matar sa sai auren ki ya gyaru, kinma samu yanada hankali da yanzu yayi saki da kincuce shi kinkuma cuci kanki, maganar wankan gida kuma kayi hak'uri kabarta taje, kwanakin basuda yawa".
Russunawa Anwar yayi ya masa godiya sannan ya mik'e ya tafi.

.

.

Fateema tuni ta saki ranta, bata tunawa da komai saiɗmda jefi2, tunda taga ta gama iddah taci gaba da rayuwar ta kamar bata taɓa aure ba.

.

.

Mahaifin Fateema ne zaune a kasuwa wajenda yake sayar da yalo da mangoro, garin yau kwata2 babu ciniki, ya haɗa tagumi yaji tsayuwar mota a gefen rumfar shi, mata ne su biyu, kana ganin su kasan basuda wata matsala, sallama suka masa ya amsa da fara'arsa, 'yar matashiyar ta ce "ka zuba mana yalo".
ta mik'a mishi 1000, da ɓari ya karɓa yana washe baki, ya cika leda ɗaya ta viva matar ta ce "wannan ai yayi yawa, idan banda kwaɗayin masu ciki mezai kaiki cin yalo".
Zunɓura baki ɗayar tayi kamar zatayi kuka ta ce "Ummi zan iya cinyewa fa".
"to amsa mutafi kinsan akwai tafiya agabanmu".
Har sunfara tafiya matar ta ce "kinga wannan tsohon da zai amince da mun tafi dashi zai mana amfani".
"kaji Ummi da wani magana, wazai biki haka kawai baisan wacece ke ba, duniyar nan kowa bai yadda da kowa bane, amma kinga da ya huta da wannan shan ranar, sai dai kuma baza'a rasa yanada iyali ba".
matar da aka k'ira Ummi ta ce "dazai amince harda iyalin nasa sai mutafi mubasu gida ɗaya, shikuma yana mana gadi muna biyan shi, tsoron mutanen Meduguri nakeyi shiyasa nakasa nema acan".
"to nidai mutafi tunda tsayuwar bashi da amfani".
H
Duk abunda suke faɗa Mahaifin Fateema yana jinsu, Sosai yaji yanaso yabisu, ganin sun shige motane yasa ya kwasa da gudu ya tsinkaye su, Ummi ta lek'o ta ce "Baba wani abune"?
Yasusa kai ya ce "Naji kuna maganar aiki, shine nace na amince".
Suka kalli juna kafin matashiyar ta ce "ka amince damene? Mufa gadi zaka mana, idan kanada mata da yara zamu tafi da ku duka, tunda garin banan kusa bane".
"To Hajiya wazaik'i ci gaba a rayuwar sa, inada mata ɗaya sai yarinya ta ɗaya sauran sunyi aure".
Buɗe mishi sit ɗin baya tayi ta ce "shigo mutafi muje gidan naka".
Ba musu ya shiga suka tafi yana nuna musu hanya.

🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
*SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏

.

Page 17

.

.

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_We dont just entertain and educate we touch the hears of readers_
*PML*

.

.

.

Writen By *Princess Eshat Aysm*

.

.

_K'irk'irarren labarine banyi don cin zarafin wani ko wata ba_

.

*Ali Sufi*

"We don't just entertain and educate we also touch the heart of readers..... Gsky ni die hard fan dinkune PML writers. Long live Hausa novels,long live readers and long live PML".

*ALI SUFI*
PURE MOMENT
_tana matuk'ar godiya_

.

.

.

Fateema suna zaune da Sakeena Maman tana hura wuta sukaji tyayuwar mota, Sakeena ta ce "yau kuma Anwar ya tuna dake kenan yazo".
Fateema ta taɓe baki ta ce "idan yak'irani yana wani maganar kamar baisan ya sakeni ba, harda bani umurnin kada naje kasuwa, kada na tsaya da wani, kinji fa wani kulle kamar zanyi ta zama masa babu aure ne".
Sakina mamaki ya kamata ta ce "kinsan yana sonki, shima babu yanda ya iyane, ɗaukomun takaddarma naga saki nawa ne".
Fateema taja tsuka "Don Allah manta da takaddarnan ko saki nawane ai anriga da anyi, ni so nakema na canza layi yadaina k'irana, kullum famamun ciwon sonshi yakeyi".
Maman ta tanajin su, ajiyar zuciya tayi ta ce "kullum bakuda taɗi sai Anwar, zanga ranar da zaki cire shi aranki....
Bata k'arasa ba Baba me yalo ya shigo, sai washe baki yakeyi.
"yau akwai alamar nasara a kasuwa, sai farinciki kakeyi".
Ya ce "sosai ma, nan ya kwashe yanda sukayi da Matannan ya faɗa mata, itama washe baki tayi tana adduar Allah yasa k'arshen talauci ne yazo, Fateema kam kuka tasa tana cewa babu inda zataje, itama Sakeena kuka takeyi kada atafi mata da k'awa, masifa ya shiga surfa musu, yana ganin zai huta yara zasu masa buk'ulu, dole ma ta bishi su tafi ko kuma ya ɗaura mata aure yau yayi tafiyar sa.

Cikin k'ank'anin lokaci yayun ta suka zo, suma sunyi murna, su hakanma yafi musu tunda basuda 'yan uwa agarin sungaji da ganin mahaifin su yana saida yalo, su Ummi kam tunda suka ajiye Baba me yalo suka koma masauk'insu akan da asuba zasu zo ɗaukarsu kafinnan sun gama shiri, dak'yar aka shawo kan Fateema ta amince sai da taga da gaske duka zata sha.

.

.

Hajiya Jamila zaune ta rabka tagumi, nadama ne ya cika ta sosai, tunanin ta ɗaya bai wuce ta ina zata fara ba, gashi tunda Alhaji yaji maganar ya daina kula ta, dabara ne ya faɗo mata, ta ɗauko wayar ta tafara k'iran Anwar, yana kwance sai juyi yakeyi, kewar matan sa duk ya addabe shi, musamman Fateema dayake jin wani bugun zuciya idan ya tuna ta, ga tsananin sha'awar datake takura mishi, duk yayi wani zuro a kwana biyu.
Jin wayar shi ta fara ruri ya tashi a kasalan ce, ganin Hajiya yasa shi watssakewa yana tunanin ko lafiya.
"Hello Anwar kana ji na"?
"inajin ki Hajiya".
"kayi hanzari ka dawo da matar ka".
Anwar me zaiyi idan ba dariya ba "yaufa kwanan ta biyu da tafiya kuma sai tayi kwana arba'in zata....
Katse shi tayi da sauri "Ubanka na ce, ni zaka raina ko Anwar, kasan wacce nake nufi".
K'unshe dariyar yayi yace "Gobe insha Allah zanje, kina tsoron Dady....
D'uf ta kashe wayar tana zage2, yaronnan ya raina ni wallahi.
shikam dariya yayi ya ce uwata sai Dady, yayimun dabara.

.

.

Washe gari da safe bayan yaje yaga Baby Aisha ya nufi garin Jos, hankalin shi a kwance.

yana isa ya tarar da gidan gark'ame da kwaɗo, can ya hango yaro ya k'ira shi, tun kafin ya tambaye shi ya ce "mutanen gidan sunyi tafiya jiya, amma inaga bazasu juma ba naga basu ɗauki kayansu ba".
Anwar yayi jum sannan ya masa godiya yabashi 1k.

Zuciyar shi fal tunani ya koma gida, gidan Hajiya ya wuce kai tsaye, tana ganin shi ta hau tambayar shi ya ɗauko ta, girgiza mata kai kawai yayi yaje ya kwanta abunshi.

.

.
Chapter 9 · 0% Book details