← Book details Shimfidar Mijina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 12

Sashe 10

Shimfidar Mijina Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Tafiya me tsayi sukayi kafin suka isa garin Meduguri, isar dare sukayi duk sun gaji musamman su Baba me yalo da ba'a saba tafiya me nisa ba, duk da darene haka masu aiki suka shiga aikin kawo musu abinci, wani part aka kaisu me ɗauke da ɗakuna biyu, sai kitchen da toilet a gefe, wankan gajiya Fateema tayi, ta cika cikin ta da abinci sannan ta hau Sallah, tana idar wa, ta ɗauko jakarta zata ɗauki wayar ta, waya yace ɗaukeni inda kika ajiyeni, ba irin neman da batayi ba amma babu, haka ta hak'ura ta kwanta tabari akan yana wajen su Baba me Yalo.

Ƴ

.

.

Washe gari da safe Ummi ta aika aka k'ira mishi Baba me Yalo, yauma matashiyar nanne ajikin ta, sai zuba mata surutu takeyi, Ummi bata mishi magana ba har saida ta lura ta gama surutun, rabin surutun ma k'anzon kuregene.
"kamar yadda muka rabaku da garin ku, ina fata zaka mana aiki cikin aminci, nidai banida wasu yara a gidannan, yaro na guda ɗaya ne kuma bashi da futuna, zaka rik'a yimana gadi muna biyanka 50k a wata, tunda ka taho da iyalan ka, zasu iya shigowa suna mana wankau sai ana biyan su, ko yaya ka gani".
russunawa yayi yamata godiya.

🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
*SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏

.

Page 18

.

.

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_We dont just entertain and educate we touch the hears of readers_
*PML*

.

.

.

Writen By *Princess Eshat Aysm*

.

.

_K'irk'irarren labarine banyi don cin zarafin wani ko wata ba_

.

.

.

Maman Fateema sosai tayi murna, ita dai Fateema taɓe baki tayi ta ce "nidai wallahi babu aikin da zanyi".
"sai kiyi ta zama ai".
Inji maman ta, Baba me yalo kuwa cewa yayi "kiyi zamanki, dama ba nufina kiyi wani abuba, su suka buk'ata, tunda bakiso babu dole, amma da zaifi miki zaman kaɗaicinnan".
"Baba ni yanzu waya ta zaku bani"

Ya kama baki, "ni kuma me zanyi da waya Fatee, kidai duba cikin kayan naki".
Shiru Fateema tayi, don tasan babu irin duban da batayi ba, shikenan wayata ta ɓata kenan, ta faɗa a ranta.

.

.

Zaman gidan babu yabo babu fallasa, mahaifiyar ta tana shiga ta musu share2 harda wanki, da yake Mama akwai tsafta ga raha yasa har suka fara sabawa da Ummi, abu ɗayane yake damun ta, ta rasa wannan me cikin 'yarta ce ko kuma, kome tace tana so a gidan shi akeyi, ga wani girma da Ahmad yake bata duk k'ank'an tarta, shagwaɓa da iya shege babu wacce batayi, kuma taji Ummi ta ce ɗanta guda ɗayane, itadai bata tambaya ba

Satin su biyu a gidan Maman Fateema ta tashi bata jin daɗi, don haka da asuba tacewa Fateema taje tayi aikin kamar yadda ta saba, zunɓura baki tayi kafin tace "Nifa bansan kan gidan ba Mama, kuma ai bansan aikin da kikeyi ba".
Mama ta taɓe baki ta ce "gidan zaki share musu, sai ɗakunan su, sannan ki haɗa kayan da suka cire ki wanke su".
Fateema tayi tsaye tana kallon Mama.
"yanzu wai duk wannan aikin ke kaɗai kike yi, bansani ba da ina zuwa ina tayaki".
Dungure mata kai tayi ta ce "Ina nan akace kije kika k'i".
Tafiya tayi tana k'unkuni.
Dak'yar ta gane kan gidan sannan tahau gyarawa, saida yayi k'al sannan ta nufi ɗakin da taga Ummi ta nufa ranarda suka iso Garin, akan Sallaya ta samesu itada me cikinnan, Ummi ta ɗaga hanu tana addu'a "Allah ka gafarta wa mijina, Allah ka shiryi mijina, Allah kasa mijina ya shiga Aljannah, Allah kabaiwa mijina arziki na duniya da lahira me anfani.....
Duk abunda tace me cikinnan tana cewa Ameen, har suka shafa sannan Fateema ta russuna ta gaishe su, da fara'a suka amsa, Ummi tace "badai ciwon kan ya hanata zuwa ba"?
"Da sauk'i dai yanzu".
Fateema ta faɗa tana murmushi, Ummi ta dubi me cikinnan tace "Farida je ki haɗo mata wankin ɗakin ki".
Saida ta shagwaɓe fuska ta ce "wallahi ban iya tashi yanzu".
Ummi tayi murmushi ta ce "bari naje na dubo dakaina".
Itadai Fateema sake baki tayi ta kallon su, mik'ewa tayi ta gyara ɗakin sannan suka nuna mata ɗakin Ahmad akan idan 8:30 tayi kafin taje ta gyara saboda ba'a shiga sai ya futa.

"to".
Kawai tace taci gaba da aikin ta, k'arfe 8:30 tanayi ta nufi ɗakin Ahmad, ba damuwar komai tunda lokacin akace taje, ɗakin ta gyara duk da taga agyare yake kawai ɗan gyara wani wajen tayi, tana gamawa ta kwashe kayan da tabbatar su ya cire ta nufi toilet kai tsaye, wani mahaukacin k'ara ta saka ta fito a guje, bata gama maida numfashi ba taji an fizgo ta, ko ɗauraye jikin shi baiyi ba ya fito, sake wani k'aran tayi ganin mutum tsirara a gaban ta, ya wanke ta da mari, "ke mahaukaciyar inane, k'aramar 'yar iskace ke, tunda kin iya lek'a mutum yana wanka baki iya kallon shi ba, waye ya faɗa miki ana shigomun ɗaki".

Kuka ta rushe dashi da iya k'arfin ta, ya ware ido yana kallon ta yana mamakin to me yasa tashiga tasan yana wanka, cikata yayi ya koma wankan sa, aikuwa da gudu tabar ɗakin tana haki, ko wajen su Ummi bata nufa ba, ɗaki ta wuce ta kwanta, duk haushin Ahmad ya cikata, harda cemata k'aramar 'yar iska alhalin ahine ɗan iska da iya biyota haka, aikuwa ba inda zan sake zuwa.

.

.

Ruɗewar da tayi yayi masifar bashi dariya, tun yana wanka yake ta dariya har yafito ya gama shiri ya nufi wajen Ummi, har k'asa ya tsuguna ya gaishe ta, sannan ya juya wajen Farida, "Aunty ina kwana".
Ta ɗan shafo kanshi ta ce "bazan amsa ba sai nasan dalilin da yasa naga fara'a kwance a fuskar ka".
Murmushi yayi yace "Naga wata jerry taje gyaramun ɗaki, yau ina Maman tata"?
Farida tayi dariya ta ce "jerry fa kace, Fateema sunan ta, yau naga ka makara meyasa"?
Kafin ya bada amsa Ummi ta ce "kefa idan ba Ahmad kika gani ba sam baki warewa, yanzu ai sai kin makarar dashi zakiji daɗi"

.
.
.
.
.
.
.
.
.

Hajiya Jamila fa hankalin ta ya fara tashi, duk bayan kwana uku sai tasa Anwar ya tafi Jos amma har yau Fateema basu dawo ba, kullum Alhaji daɗa mata rashin mutunci yakeyi.

Anwar duk abun duniya ya isheshi ko yak'ira ta awaya har tagama ringn ba'a pickn, yanzu hankalin shi ya fara tashi, dama baka sanin kana son mutun sai ya maka nisa.

🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
*SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏

.

Page 19

.

.

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
_We dont just entertain and educate we touch the hears of readers_
*PML*

.

.

.

Writen By *Princess Eshat Aysm*

.

.

_K'irk'irarren labarine banyi don cin zarafin wani ko wata ba_

.

.

.

*Wayyyyyyo cikina*
*Ban taɓa dariya a novel irin wannan ba, SWEET SADNAF kina cin mutuncin Abdl ycn, hhhhhhhhhhhhhhhhhhh wallahi inason ku 'yan Pure moment, ta ko ina Novels ɗinsu dabanne*
🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣

.

.

.

.

.

Tana zaune a bakin gado a ɗakin da aka bata, tana baiwa Baby Aisha nono, ta zuba mata ido tanajin wani sanyi a ranta, Anwar yayi sallama ya shigo, idon shi yana kanta yana murmushi, itama murmushin tayi ta ce "Abban Aisha sai yanzu, nidai kwana biyunnan nakasa gane meke damun ka".
D'an murmusawa yayi lokacin da yake zama kusa da ita, yasa hanu ya shafa kan Baby Aisha, yace "Yaushe zaki dawo".
Binshi tayi da kallo ta ce "ko sati uku fa bamuyi ba".
Bakinshi yakai saman nonon, sauk'an numfashin bakinshi taji akai tayi saurin ɗago dakan shi, "me kakeyi haka Anwar"?
Susa kai yayi yana dariya ya wayince da cewa "inaso nafaɗa miki wata magana Maryam, naje garin su Fateema yafi a k'irga bana samun ta, kullum gidansu a rufe, wallahi hankalina ya fara tashi".
Da mamaki take kallon shi, ta ce "me kake zuwa yi mata, bacin ka saketa kuma kake wani hankalin ka ya fara tashi, to Allah yasa Aure tayi ma".
Ta karashe tana zunɓura baki.
Karɓan Baby Aisha yayi ganin tayi bacci, yakai ta wajen kwanciyar ta yana cewa "menene kike ɓata rai to, kuma adduan ki ba ameen ba".
Shima yafaɗa yana ɓata rai.
Chapter 10 · 0% Book details