← Book details Shimfidar Mijina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 12

Sashe 7

Shimfidar Mijina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dayake Anwar yana d'akin Fateema ne baima sani ba, a daddafe ta samu tayi Sallah saboda wani jirin da yake kwasar ta, akan Sallayar bacci ya kwashe ta, sau biyu Fateema tana lek'owa taga tana bacci sai ta koma, don haka tayi aikin ta ita kada'i.
sai kusan k'arfe 10 Anwar yafito, cikin shirin shi da alama futa yakeson yi, d'akin Maryam ya nufa yana tunanin wani irin bacci takeyi har yanzu.
har lokacin bata tashiba, kwanciyar kad'ai ya gani yagani ya fahimci ba kwanciyar jin dad'i bane, kusa da ita ya matsa yad'an rank'wafa kansa zai sumbace ta, da sauri yad'ago jin wani irin hucin zafin daya bugi fuskar shi, hijabin yayi sauri ya warware shi, yana k'ok'arin cirewa ta bud'e idanuwan ta da sukayi ja, ta lumshe su hawaye ya biyo baya saboda wani irin azaban da take ji akan ta, yana wani irin sarawa kamar zai fad'o, a rud'e yafara tambayar ta me yasame ta, ba abunda takeyi sai hawaye, da sauri ya mik'e ya Deb'o ruwa a cup, ya zauna ya mik'e k'afafuwan sa ya jawota yad'aura ta akai, kayan jikinnata ya cire yafara
matsa mata jiki da ruwan, sai da yaji jikin yad'an yi sanyi ya rungumo ta sosai, "me yake damun ki maryam, don Allah kiyi mun magana".

kai kawai ta kad'a mishi, ya dad'a mannata ajikin sa, kafin yayi magana Fateema ta turo d'akin ta shigo, ganinsu a haka sai da k'irjin ta ya buga, da sauri tayi baya zata juya, taji muryan shi yana cewa

"ina zakije"?

bata juyo ba ta k'wak'ulo murmushi ta ce "nazo duba Aunty ne".
ya ce "shine zaki koma"?
bata tsaya bashi amsa ba tasa kai ta futa.
ita kanta maryam kunya taji, daga ita sai pant ajikin ta, gashi ya wani matseta a jikin sa.

Ahankali ya d'agata ya d'auko mata kaya ya sanya mata harda hijabi, sannan yanufi d'akin Fateema, tana jinshi tayi toilet da gudu ta wanke fuskar ta tafito, binta yayi da kallo kafin ya ce "me ya sami idonki"?

murmushi tayi tace k'waro ne yashiga har yanzu ina jinshi, ka huremun, ta isa gaban shi tana ware idanuwan, kama kan yayi, yafara hure wa, yayi sau uku ta ce yafita, sannu yayi mata sannan yace, "zan kai Maryam Asibiti ashe batada lafiya".

tausayi k'arara a fuskanta ta ce "me yake damun ta, shiyasa bata tashiba, sai muje tare".

ya ce "a'a ki zauna yanzu zamu dawo, inaga zazzab'i ne kawai".

Har bakin mota ta rakasu, tanayi wa maryam sannu.
Gwajin farko aka shaida musu cikine ajikin ta, kuka Anwar ya farayi na tsananin murna, a take yayi sujjada yana godiya ga Allah, d'aga Maryam sama yayi yafara juyi da ita, shi kanshi likitan tayashi murna yakeyi, dak'yar ya iya tsayawa aka rubuta musu maganin da zai sa jikin yad'an rage zafi, tsam ya d'auke ta kamar wata jaririya, haka yayi ta ratsawa cikin mutane anata kallon su, bai damu ba don gani yake kamar idan tayi tafiya cikin zai zube.

koda suka isa gida ma d'aukar ta yayi, ta ce "ka sauke ni zan iya tafiya fa".

bai ko saurare ta ba ya tafi abunshi.
Fateema ta k'urawa tv ido taji shigowar su, da hanzari ta mik'e ganin Maryam nad'e a hannun shi, tayi tsammanin ciwon yayi tsanani ne, kawai sai gani tayi Anwar yana danse rawa harda 'yar wak'a

*Soyayya tayi k'arko masoyiy a kula da ita, kada ayi mata ɓatanci sahiba akiyaye ta, Wayyo ni Allah daɗi ya cikani....*

sororo Fateema tayi tana tunanin me zaisa Anwar farinciki haka, haihuwa, tabaiwa kanta amsa, kenan Maryam tasamu ciki, ai batasan lokacin da murna ta kamata ba, itama rik'o maryam tayi tana taya Anwar rawa tana amshi, Maryam daɗi kamar ya kashe ta ganin soyayyar da Fateema take nuna mata, ranar wuni sukayi suna abu ɗaya, duk ciwon da Maryam takeji haka ta daure kada ta ɗaga musu hankali.

Dare ya tsala amma Anwar ya kasa bacci, zuciyar shi sai kitsa mishi takeyi yaje ya dubo maryam, baiyi dogon tunani ba ya mik'e ya nufi k'ofa, Fateema ta ce "ina zakaje".
ya ce "zan dubo baby na".
Dariya tayi ta mik'e tace "muje tare nima inaso mu gana".

ya nok'e kafaɗa ya ce "nak'i wayon".
ta ce "wlh tare zamuje nima nak'i wayon".
da dariyar su suka nufi ɗakin Maryam.

Maryam ta daɗe da bacci saboda maganin da tasha, har rige rigen taɓata sukeyi, a hankali ta buɗe ido, ganin mutane akanta yasa tayi saurin tashi ta zauna tana mutssuka ido, waro ido tayi tace "lafiya"?
Fateema ta ce "yi hak'uri Aunty mun tasheki, rigimane dashi wai zai duba babyn shi".
Maryam ta ce "kodai rigima ne daku, tunda kum tashe ni sai kuzauna muyi ta kallon juna".
Dukkan su suka fashe da dariya, Anwar kamar jira yakeyi yaja hanun Fateema suka zauna a kusa da Maryam, Fateema ta ce "ga shawara, kada mubari Hajiya taga cikinnan, mubata mamaki".
Duk sukay na'am da maganar.

Rayuwa me daɗi sukeyi, Fateema bata gajiyawa ko kaɗan da halin da Anwar yake mata, ranar girkin ta aɗakin Maryam yake kusa kwana wai kada wani abu ya sameta, Maryam tayi2 ya daina yak'i, Fateema tace tabarshi kawai wataran itama zata rama.

🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏
*SHIMFID'AR MIJINA*
🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏🛏

.

.

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
PML
_We dont just entertain and educated we also teach the hearts of the readers_

.

.

Writen By *Princess Eshat Aysm*
.

.

Page 14
.

.

_Ina matuk'ar godiya da tarin adduoin da kuke sambaɗo mun Princess har kullum tana alfahari da masoyan ta_

.

.

_Duk wani cmmnt ɗin ku ina gani koda bani nayi postn ba_

.

.

_Ina ganin novel ɗinnan a groups sunfi 30 a fcbk ina godiya sosai_

.
.

.

*MASU CEWA NOVEL D'INNAN YASA SUNJI SUNA SO A MUSU KISHIYA, KUYITA ADDUA ALLAH YA KAWO TA GARI ZAI KAWO*

.

.

*MASOYANA ILYSM💋*

.

.

.

.

Adaidai lokacin Fateema ta cika shekara guda agidan, Maryam kuma tanada shekaru uku, cikin ta wata biyar harya fara fitowa, har lokacin Hajiya batasan Maryam tanada ciki ba, ita bata zuwa gidan ko kaɗan, acewar ta zasu rainata ita kuma akwai son girma, shiyasa batasan abunda yake faruwa ba.

yau tun safe Fateema ta shirya zataje gaishe da Hajiya kamar yadda ta saba takanje mata wuni wani lokaci, a hanya Anwar ya mata siyayya wanda zata kai mata.

Tun shigarsu Fateema taga canji, fuskar Hajiya a murtuk'e, dak'yar ta amsa gaisuwar da suke mata, Fateema ta ce "na shiga uku, kaddai shekara ɗaya har zata dawo kaina....
Maganar Hajiya ne ya katse mata tunani
"Anwar nifa nagaji da irin matar da kake kwasowa, ace har yanzu ba wani labari, to wallahi aure zan maka wacce zata cikamun gida da jikoki, kullum zuwa babu hayaniya babu komai".
Anwar daya zuba mata ido ya ce "Hajiya shifa haihuwa na Allah ne".
Ta taɓe baki ta ce "kullum maganar kenan, Allah yace rashi in taimake ka ai".

Zufa duk yagama wanke Fateema, "nafaɗa mata Maryam nada ciki kawai a huta, kai a'a banyi shawara da Aunty ba".

Ita kaɗai take saka da warwara a zuciyar ta.
Anwar yace "kinga irin wannan rashin hak'urin ne yasa kika so tafka kuskure".

Hajiya ta masa wani kallo kafin tace "yanzu don inaso naga ɗanka shine kake faɗa mun magana, ita waccan saboda taurin kunne kak'i sakin ta, bayan har k'wayoyi takesha, menene kuskure na anan".

Ta k'arashe kamar zatayi kuka, Anwar ya ruɗe ya ce "Ina nufin kuskuren da kikayi na bada magani asawa Maryam, gashi yanzu ta samu rabon ta, Allah ya bata cikinnan".

Zunɓur Hajiya ta mik'e, wani gefen zuciyarta tana nanata Maryam nada ciki, mummunan kallo ta watsa wa Fateema ta ce "Ashe ke algunguma ce? Zuwa kikayi kika faɗa masa? To wallahi bazan zauna dake ki rainani ba".

iya ruɗewa Fateema ta ruɗe, ta kalli Anwar ta fara girgiza mishi kai, shima girgiza mata kai yayi,
"Hajiya me kike tunani ne, ranarda kika bata maganinnan ina tsaye ina gani...
da sauri ta katse shi, "k'arya kakeyi Anwar, yanzu zaka saki yarinyar nan kafin mahaifin ka yadawo k'asar "Hajiya menene laifin Fateema a ciki, don Allah kimun rai kada ki rabani da farinciki na, idan har kika yi haka bakiyi adalci wa kanki...
tsawar data masa shi yasa shi yin shiru, lokaci guda tayi d'aki, da gudu Fateema ta fad'a jikin sa ta saki wani kuka, "kada kabari ta rabamu, ina sonku kaida Aunty Maryam, idan natafi wazai kula...
cikin tsananin tausayi ya had'e bakin shi da nata, biye mishi tayi har suka zauna basu sani ba.

"eyeeeh

*LALATA*

zaku nuna mun? wlh kaji na rantse saika sake ta".

muryar Hajiya suka jiyo, ta futo d'auke da bairo da takadda a hannun ta, a duburbure suka saki juna, Fateema tana kuka ta ce "HAJIYA nayi miki al'kawari bazan rainaki ba...".
ko kallo bata ishe ta ba, cike da masifa ta mik'a masa takaddar, runtse ido yayi ya ce "sai dai kiyi hak'uri, bazan iya saketa babu abunda tamun ba, idan laifine kece me laifi hajiya...".

Kafin ya gama ta tsinke shi da mari har sau biyu, "wlh matuk'ar baka sake ta ba zan tsine maka".

"zan sake ta".

a rud'e Fateema take kallon shi, bai ko kalle ta
ba ya mik'a hanu ya amshi takaddar wajen Hajiya, rubutu yayi ajiki ya nad'e ya baiwa Fateema, Kukan da ta b'oyene ya fito tayi waje da gudu, tana ji yana k'iran ta bata tsaya ba.

wani murmushi yayi ya ce "sai me kike buk'a ta? uwata me ran k'arfe".

Ita kanta jikin ta yayi sanyi, ta shige d'aki ta barshi.

Taxi Fateema ta nema ta nufi gida, sai da ta isa ta d'auko mishi kud'in, taji dad'i ganin Maryam bata falon, idon ta harya kumbura don kuka, bata b'ata lokaci ba ta had'a kayan sawar ta, ta jefa takaddan da Anwar ya bata ajaka, ta sid'ad'a taja kayanta tabar gidan.
Chapter 7 · 0% Book details