← Book details Shaawar Ta Nikeyi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 15

Sashe 7

Shaawar Ta Nikeyi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

ta k'arasa maganar tana wani kashe mai idanu, Marwa kuwa tasan room d'inta a haukace yake sai cewa tayi bara naje na fara had'a ruwan wankan zan kiraka." Tana gama fad'ar haka ta haura sama kyanta ta fara kwashewa ta saka masu datti cikin ijinmin wanki ta saka marasa datti cikin wadroup, sabon bedsheet ta saka ta gyara komai ta aje sa inda ya dace,

Anam ce tayi sallama a k'ofar room d'in karb'awa tayi, tare fad'in shigo, Anam ta shiga, tacee "Aunty Marwa Aiki akeyi.?" D'an murmushi tayi kana tace "Bara na kama miki." Batayi musu suka cigaba da gyaran d'akin, har zuwa parloun ta kana ta shiga bathroom ta wanke sa tas da yake babu abinda babu na wankin bathroom,

turaree Anam ta kawo mata ta saka a bonar take ko ina ya game da k'amshi mai dad'i ga sanyin Ac daya ratsa ko ina, kana Anam tace "Aunty Marwa yunwa nike ji bara naje na ci abinci bey." Marwa tace "Na gode sosai saina fito." farin ciki ne ya kamata sai kallon bedroom d'inta takeyi da parlou, gwanin burgewa, a fili ta furta tsafta mai dad'i."

Bathroom ta shiga ta had'awa Alhaji ruwan wanka hadda turare kana ta sauka parlou tace "My love muje na had'a." Okey kawai ya fad'a ya bi bayanta, Ayma kuwa murmushi ta saki na samun nasara data farayi, Alhaji kuwa abinda be tab'a tsammanin ba ya gani parlon Marwa tsaf sai k'amshi yakeyi bedroom d'inta ma haka, be ida shan mamaki ba sai da ya shiga bathroom ya yi wanka,

bayan ya fito ya shirya kana suka sauka parlon k'asa suka ci abinci gaba d'ayan su,

Haka rayuwa ta cigaba da tafiya kullum ana samun sauyi a wurin Marwa, saboda gaba d'aya Yanzu bata zama da k'azanta tasfata takeyi ta gida data jiikinta, ga abubuwan gyaran jiki da Ayma ke koya mata su Ummie kuwa mayar su uku a gidan Gett Man yana hanasu shiga idan sun kira wayar Marwa bata d'auka,

saboda zuwan da sukayi a gidan na K'arshe, Marwa ta fito kitchen suna parlon sama sai zaginta sukeyi suna hirar maganin da suka karb'o wurin Boka suka bata da zimmar yin wufff da Alhaji a korata waje Ayma na jinsu tayi musu Record bayan sun tafi ta kunnawa Marwa taji duk abinda suke fad'a, taso kiransu ta zagesu Ayma ta hana mata, tace ta rabuda su kawai,

ta cigaba da K'awance da Sa'ida saboda itace karawata dake sonta tsakani da Allah yau Ayma ta ciga kwana goma a gidan ta tattara kayanta gaba d'aya ita da Anam zasu koma, gida Alhaji Abubakar ya kira Marwa suka zauna parlou ya sanar da ita komai Ayma ba Matarsa bace saboda ta gyara halinta ne ya aikata mata haka, saboda haka Ayma zata tafiyarta sai Allah ya sake sadasu da Alkhairy,

hadda kuka tayi da zasu tafi saboda ta saba da su sosai sukayi musayar number saboda zumunci, kana Alhaji ya mayarda Ayma Unguwar sabon layi, akan gobe zai dawo suyi magana,

suna shiga gidan ita da Anam ta tarar da Barau yana b'alla k'ofar d'akinta ai kuwa tayo kansa ta kifesa da wawan mari, tace "Kai uban waye ya baka damar b'alla min k'ofar d'aki.?" Hanan tace "Ai wallahi tin tafiyarki abinda yake k'ok'arin yi kenan, wai sai yaga abinda kika aje a ciki shine fa kika tarar da shi." Barau yace "To munafuka na gaji da zaman hayar ku saboda haka ki kwahse kayanku a bar min gidana haka kawai a dinka cutar dani."

Kwalar rigarsa Ayma taci kana tace Wallahi babu inda zamuje sai kud'in hayarmu ya k'are idan na koma ganin k'arfarka a k'ofar dakina saina karyaka sakaren banza." Anam tace"Ai wallahi dukan tsiya ya kamata ayiwa jaki." Barau yace "ai saiki zo ki dakeni muguwar banza." Ayma kuwa shigewa tayi d'akinta, ta barsu nan tsakiyar gida,

wayarta ce ta soma ringing dubawa tayi bak'owar number ce d'agawa tayi batare da tayi magana ba sallama akayi mata ta karb'a kana akace "sunana Alhaji Manir na samu number ki ne a gurin Anam idan ba damuwa zan iya zuwa mu haɗu ko ke zaki sameni.?" Ajiyar zuciya ta sauke kana tace"Kaga Alhaji kai ke nemana saboda haka kai zaka zo." Yace ba damuwa gashi nan zuwa, da yake yasan unguwar,

b'angaren Ayman kuwa washegari tinda ya shirya ya fita Company be dawo ba sai da yamma ya had'a jakar kayansa, suka wace filin jirgi, zuwa k'asar Dubai, Saudat kuwa tun tafiyarta bata kirasa a waya ba ko sau d'aya shima haka , kamar ba Mata da Miji ba, Safra na kwance, a room d'in hotel, ita da Wata Hajiya Billy, sai chachakar juna sukeyi wayarta ta soma ringing, da kyar ta iya d'agawa,

Akace "Saf kina ina ne wallahi naga Yarinyar da kike nema a unguwar GRA na bibiyeta har zuwa Unguwar sabon layi na tabbatar a nan take da zama gidan y'an Bariki ne." Zabura Safra tayi tana fad'in "Kai Rona da gaske kakeyi.?" Yace "Yo ina miki wasa ne wallahi itace na gani idan baki yarda ba zamuyi iya zuwa domin ki tabbatar."

Tace "shikenan kazo Hotel d'in da muke had'uwa." Ta kashe wayar saboda wata zuk'a da Billy tayi mata saida jiikinta ya d'auke rawa, bayan sun gamsar da juna tayi wanka ta shirya tace "Hajiya Billy zanje na dawo a nan zaki zauna ko tafiya zakiyi.?" Hajiya Billy tace "zan jiraki don ban k'oshi ba." Safra tace"Okey bey." Ta d'auke key d'in motarta ta fita,

a bakin Get suka had'u da Rona ta daukesa suka tafi, basu zame ko ina ba sai Sabon layi har cikin gidan ko sallama babu, Anam ta fito zata je shago, siyen lemo ta gansu Safra tace "Ke inane d'akin Ayma.?" Anam tace "Yana wurin koyan sallama." Safra tace "Kega wallahi zan saka ayimiki dukan tsiya inane d'akin Ayma.?"

Anam ta bud'e baki zatayi magana sai jin Muryar Ayma tayi a bayanta tace "Ba iya d'akin Ayma har Aymar Gani a nan don Kutumar ubanki Safra......

Writer Bey Pinky Darling Mrs Jay ✍🏼 more comment More typing please share
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*SHA'AWARTA NIKEYI*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀

(Romance and sxy)

🔞❌
Writer Bey
Pinky Darling Mrs Jay ✍️
✨✨✨✨✨✨✨✨

💪*JAJIRTATTU WRITER'S
ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)

Bismillahi Rahamanin Raheem 💫

Following this link to join my WhatsApp channel domin samun zafafan liltafaina sabbi da tsofaffi tare abubuwan k'aruwa

https://whatsapp.com/channel/0029ValAwoOInlqYMwE1dK00

BOOK ONE

PAGE 1️⃣5️⃣⏩1️⃣6️⃣

Safra tace"Kan uba Ayma ni zaki zaga saboda idanunki sun fara bud'ewa a Bariki to wallahi saikeyi dana sanin abinda kika aikata Rona chafko min shegiya naci ubanta naga wanda zai tsaya mata,"Ni ne nan zan tsaya mata sai akayi ya.?" muryar data ji a bayanta tayi masifar firgitata,

Juyawa tayi don tabbatar da abinda kunnenta yaji tabbas ba k'arya taji ba Ayman ne tsaye a bayanta ya hard'e hannuwansa a k'irji ga bodyguard d'insa d'auke da manyan bindigogi, shigarsu ka d'ai ta isa firgita mutum har ya saki fitsari a wando, mamaki ne ya kamata ta saki baki da hanci tana kallonsa, shi kuwa Ayma yake kallo, dake tsaye

ta rik'e k'ugu saboda masifa, bud'e bakinsa ya yi da kyar kamar wanda akayiwa dole yace "Ke d'auko kayanki mu tafi." Kallon baka da hankali tayi mai ganin yadda ya zuba mata lulu eyes d'insa masu tafiyar da zuciyar mai kallonsa ga wani kwarjini da ya yi mata, dole ta saukar da kanta ga masifar dake cinta amma ta kasa magana,

d'aya daga cikin bodyguard d'insa ne yace "Ke Madam ko baki ji abinda Ogah ya fad'a bane.?" Anam tace "Taji bara na fito da kayanta." Haka ta shiga ta had'o kayan Ayma gaba d'aya suka loda a Mota, kanan Ayman yace gaba d'aya su wuce su tafi har Anam haka ta d'auko jakar kayanta, suka bar Safra nan tsaye ita da Rona ba damar magana,

yanzu bodyguard d'insa suyi musu dukan mutuwa, har sun kai bakin k'ofar fita Ayma ta dawo gun Sarfa tace "Zamu had'u ne don Wallahi saina d'auke fansar abinda kikayi min keda wannan kwarton naki." Sarfa tace "Ai kuwa zanso wannan rana kuma bara kiji in dai Ayman ne abin alfaharinki wallahi saina raba ki da shi don ba sa'arki bane." Wata dariyar rainin hankali Ayma tayi kana tace"Losara kawai muje zuwa Wallahi iskancina ya fi karfinki."

Tana gama fad'ar haka ta fita, Sarfa kuwa mamakin Ayman ne fal a ranta saida taji d'agawar motocinsu kana suka fita wayarta ta d'auka ta shiga dannawa Saudat kira, amma har ta katse bata d'auka ba sake danna kiran tayi saida ta kusa katsewa kana Saudat ta d'auka, Safra tace"Besty wallahi ki gaggauta dawowa Najerya don Wallahi Ayma tayi wuff Ayman."

kwance Saudat take Raha na chachakar gindinta da yatsa sai data zabura tace "Saf kesan abinda kike fad'a kuwa.?" Safra tace "Wallahi da gaskiya nike fad'a miki idan k'arya ne kika dawo zaki gani saboda ke ganni nan mamaki ya cika ni kamar a mafarki fa." Nan gayamata duk yadda abinda ke faruwa ai kuwa Saudat ta dira kan bed ta shige bathroom wanka tayi ta fito ta soma had'a kayanta,

Raha na tambayarta meke faruwa ne nan take sanar da ita, wani murmushin mugunta tayi kana tace "kai amma wannan yarinyar anyi tsinanniya muje muci uban shegiya." Ta diro kan bed ta soma had'a kayanta suka fita sai filin jirgi, b'angaren Ayman kuwa basu zame ko ina ba sai gidansa babban parlou ya zauna saiga Anam da Ayma sun shigo yace

"A yanzu ni kike yiwa aiki ba Saudat ba girki kawai zaki dinga yimin da gyara min part d'ina, iya wannan ne nike buk'ata saiki fad'i ko nairya miliyan nawa kike buk'ata zan biyaki dollar ko kud'in najeriya yiro.?" Ayma tace "Shikenan dollar nike buk'ata duk wata dollar dubu d'aya sanan zan cigaba da fita sha'ani na." Ayman yace "Wannan matsalarki ce." yana gama fad'ar haka ya kira Samira kaisu part d'aya dake cikin parlon,
Chapter 7 · 0% Book details