Sashe 2
Sanadin Kenan Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
****
Haka Amina ta ci gaba da aiki a gidan Gwamnati har ga shi yau ta debi watanni goma tana kula da Ameena da iyakar iyawarta da iya zurfin ilmin da Allah ya hore mata, bata tsaya anan ba, tana cigaba da bincike akan wahalar ‘paralysis’, dare da rana yini da safiya tana kuma hadawa da addu’a, nafilfili, tsayuwar dare duk akan lafiyar Ameena Ma’arouf. Kullum kuma yarinya Ameena kara samun lafiya da kuzari ta ke.
Hannayenta hagu da dama duk suna motsi, kafar ce guda daya har yau Allah bai ba ta damar takawa ba, Amina ta soma yi mata amfani da karafuna biyu hagu da dama, tana taimaka mata tana koyon takawa da su.
A hankali sabo mai tsanani ya ci gaba da shiga tsakanin Gwamna Ji-kas da Amina, cikin dabara yake janta a jiki yana shiga al’amuran rayuwarta, hali shi ne babban abin da ke sanyawa a so mutum. Kuma Amina tanada hali, hali kuwa mai kyau abin yabo.
Kullum Ma'arouf Ji-kas cikin (observing) halayen Amina yake, na yau daban, na gobe daban masu yi masa kamanceceniya da na A’ISHA. A sannu soyayya mai girma ta cigaba da ginuwa a zuciyarsa ba tare da sanin shi kansa ba. Irin son nan mai shiga ahankali batareda sanin ma’acbocinsa ba.
Abinda ya nuna masa son Aminan ya dade da kama shishine; halin kewa da rashin sukunin da yake samun kansa a ciki a duk lokacin da ta je gida karshen mako, ga damuwa da al'amuranta. Ga son ganinta akai-akai, ga son jin sassanyar muryarta. Ya samu kansa da damuwa da Amina cikin duk abubuwan da yake gabatarwa, komai yake yi sai ta fado masa a rai da wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa.
Goggo da Ilya, wanda yanzu ya zama na hannun daman Ma’arouf kuma babban (officer) na (catering) a gidan gwamnati sun dade da gane His Excellency son Amina yake yi, amma ita wawiyar har gobe ta sanya Baban Ameena a matsayin wani mutum mai son ci gabanta, mai kula da al'amuranta, mai darajja iyayenta da ‘yan uwanta. Mai son kowa nata.
Hatta Talatu da Zulai Jikas ya san da zamansu. Don haka itama a gare ta Ma'arouf Habibu Ji-kas, mutum ne mai daraja da kimada bata ajiye matsayin sa nan kusa a zuciyar ta ba, irin matsayin nan da kake baiwa babban Yayanka da kuke ciki daya.
A gefe ga kaunar da Hajiya ke mata kamar ta hadiye ta, kusan kullum sai sun yi waya. Kaji su suna hira rai-rai-rai kamar ‘ya da uwa. Amma bata cika zuwa ba. Hajiya na da wannan dadadden burin a zuciyarta na Allah ya hada zuciyoyin Ma'arouf da Amina, amma idan ta tuna tsarin da a kullum yake fadin ya yi wa rayuwarsa sai jikinta ya yi sanyi. Duk da haka tana addu'a idan Allah ya tashi sauya zuciyar Ma'arouf daga kan tsarinsa na auren mata daya kacal, Ya sanya Amina ce.
Ita ba za ta tilasta masa ya kara aure ba, ko ta tallata masa Amina ya zo ya ce a'ah ta zubar mata da martaba a banza a idanunsa.
A daya gefen zamansa da Laila na kara tabarbarewa. Kullum ba ta gida, in kuma tana nan za ka tadda falonta cike da kawaye da women leaders. Idonta ya bude sosai da harkar siyasa ta yadda har ba ta da lokacinsa. Ko tafiya ce ta kama shi ya nemi rakiyarta ba ya samu yanzu, za ta ce tana da biki, ko gayyatar taro ya je abinsa.
Tafiya ta yi tafiya aka gangara watanni goma sha daya. Ma'arouf Ji-kas ya soma ganewa, wato bayan ilmin likitancin tada mataccen kashi da Allah ya baiwa Amina, ita din fasiha ce, tana da sani a fannonin rayuwa daban-daban. A hankali zuciyarsa ta cigaba da afuwaga soyayyar Amina mai girman gaske.
A karshen wata na goma sha daya ne Amina ta duba asusunta. Kudin ciki sun ba ta tsoro, sai ta ga lokacin da ya dace ta cika burinta a kan Goggonta ya yi.
A wani yammaci ta kira Ilya kafin ya wuce gida, bayan ya tashi daga aiki. Suka zuna a wani hadadden dankaramin falo, ta gyara zama ta fuskanceshi, tace,
"Ilya, na kira ka ne don ka taimaka mani, na samu abin da zai ishe ni cika burina. So nake Goggo ta ji dadi a wannan siradin na rayuwarta. Ta daina wannan wahalalliyar sana'ar, shekarunta sun ja. Tana bukatar hutu.
Inaso Goggo nata daina shiga motar haya, ta je ta sauke farali. A rushe gidanmu a yi mata na zamani. Ga abinda nake da shi, gaba daya na damka wannan hidimar a hannunka.
Ina kuma rokonka kada ka gaya mata sai ka kammala komai. Aikin hajji kuwa, sai an sa musu ranar tashi za ka gaya mata".
Ilya ya dubi Amina, sai ya ga tana share hawaye.
"To kukan na mene ne kuma? Allah ya yi miki albarka Amina, Allah ya ba ki miji na gari da zuri'a mai albarka masu jin kan mahaifa. Hakika ni ma na yi wannan tunanin, lokaci ya yi da Goggo za ta huta haka a rayuwarta tunda dukkanmu ni da ke yanzu mun tsaya da kafafunmu, mun kawo karfi.".
Amina ta yi sharbe,
"Ba komai ya sa ni kuka ba Ilya, illa tuna Baba da na yi. How I wish shi ma yana raye? Ya shigo cikin inuwar ilmin da suka dora ni a kai? Suka tsaya min nayi? Allah ya yi masa rahama!".
"Daina kukan haka, ya isa. Ki ba ni wata guda, komai zai kammala a gabanta insha Allah. Amma maganar gini, ki ba ni wata biyu, ba nata za a rushe ba, sabo za a yi. In aka ce sai an rushe dole sai ta fito daga gidan, kuma sai ta tambayi ba'asi.
Sabon fili za a saya ayi sabon gini, a gaba kadan damu akwai wasu sababbin filaye da ake sayarwa kwanannan. Aikin hajj kuwa an kusa gama biyan na wannan shekarar, don haka zan hanzarta. Mota kuwa har Kwatano zani da kaina na auno mai kyau, ta zamani. Allah ya yi miki albarka".
Amina ta ce, "Ameen.Sai abu na biyu. So nake Goggo ta daina wannan sana'ar wahalar kwata-kwata daga lokacin da za ta tare a sabon gidanta, zan dinga raba albashina biyu duk wata ina bata rabi".
Ilya ya dan girgiza kai,
"Da kyar za ta yarda da wannan. Zan dai dauki ma'aikata a dinga biyansu su ci gaba da komai, nata ya zamo umarni".
*****
Gadan-gadan Ilya ya shiga aiwatar da aikin amanar da Amina ta damka masa. Sai da ya kammala komai, madaidaicin lodge dinGoggo mai brown rufi ya kammala, mota kirar (E-Class) ta iso. Matsala daya Ilya ya samu, wato dole Goggo ta je a yi mata fasfot da daukan hoto.
Daga baya dabara ta zo masa, ya je ya samu Goggo ya ce ta yi shiri su je wani waje za a yi musu takardar zama 'yan kasa, kuma dole sai an dauki hoto.
Goggo ba ta yi musu ba ta shirya suka jeimmigrationofficeaka yi mata fasfot ba da saninta ba. Aka dauke ta hoto, ba ta sa wa ranta komai ba, Ilya ya je ya biya kudin kujerar hajjin Goggo, aka yi mata visada komai aka sanya musu ranar tashi, sannan ne ya zo ya gaya wa Goggo komai ya damka mata fasfot dinta.
Goggo don dadi sai hawaye. Wai ita ce za ta je dakin Allah mai alfarma karkashin inuwar Amina. Lokacin Amina na government house, Goggo ta kira ta a waya.
"Sai kuma na ji wannan abin alheri haka? Aminan Goggo,Allah ya yi miki albarka, Ya baki miji nagari wanda zai tallafi maraicinki, ya rike ki da amana da kauna ta gaskiya".
Dadi ya rufe Amina, dama abinda take so kenan, (albarkar Goggo),cewa ta ke, "Amin-Amin Goggo, Goggo Allah Ya bar min ke!!!".
Ranar juma'a su Goggo suka tashi zuwa kasa mai tsarki. Don haka wannan satin Amina ta yi zamanta ba ta zo gida ba, ta ci gaba da kula da Ameena.
Idan Hajiya Hauwa tana dawafi a Ka’abah, ba abinda ta ke rokosai miji nagari ga Amina. Idan sujjadah ta yi a Maqama Ibrahima, addu'ar da ke kan halshenta kenan. Idan Safah da Marwah ta ke, roqon Allah ta ke ya fiddo wa Amina miji nagari cikin gaggawa. Yasa jinkirinta ya zame mata alkhairi. Ta yaya Allah zai juyar da wannan addu’ar ta UWA? Wannan shi ne kadai sauran burinta a rayuwa, sai neman cikawa da imani.
Goggo na can Makkah, Amina na dakinta na gidan gwamnati tare da patientdinta, wadda ke kwance kan cinyoyinta tana mata messaging a gabobinta. Sai kawai Ameena ta yunkura ta tashi zaune.
Dr. Amina ta ce, "Mene ne Amina?"
"Fitsari zan yi".
Kafin ta yi wani motsi na taimaka mata don mikewa, Ameenar ta mike da kanta a kan kafafunta (all of a sudden). Ta yi hanyar bayan gida.
Haka Amina ta ci gaba da aiki a gidan Gwamnati har ga shi yau ta debi watanni goma tana kula da Ameena da iyakar iyawarta da iya zurfin ilmin da Allah ya hore mata, bata tsaya anan ba, tana cigaba da bincike akan wahalar ‘paralysis’, dare da rana yini da safiya tana kuma hadawa da addu’a, nafilfili, tsayuwar dare duk akan lafiyar Ameena Ma’arouf. Kullum kuma yarinya Ameena kara samun lafiya da kuzari ta ke.
Hannayenta hagu da dama duk suna motsi, kafar ce guda daya har yau Allah bai ba ta damar takawa ba, Amina ta soma yi mata amfani da karafuna biyu hagu da dama, tana taimaka mata tana koyon takawa da su.
A hankali sabo mai tsanani ya ci gaba da shiga tsakanin Gwamna Ji-kas da Amina, cikin dabara yake janta a jiki yana shiga al’amuran rayuwarta, hali shi ne babban abin da ke sanyawa a so mutum. Kuma Amina tanada hali, hali kuwa mai kyau abin yabo.
Kullum Ma'arouf Ji-kas cikin (observing) halayen Amina yake, na yau daban, na gobe daban masu yi masa kamanceceniya da na A’ISHA. A sannu soyayya mai girma ta cigaba da ginuwa a zuciyarsa ba tare da sanin shi kansa ba. Irin son nan mai shiga ahankali batareda sanin ma’acbocinsa ba.
Abinda ya nuna masa son Aminan ya dade da kama shishine; halin kewa da rashin sukunin da yake samun kansa a ciki a duk lokacin da ta je gida karshen mako, ga damuwa da al'amuranta. Ga son ganinta akai-akai, ga son jin sassanyar muryarta. Ya samu kansa da damuwa da Amina cikin duk abubuwan da yake gabatarwa, komai yake yi sai ta fado masa a rai da wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa.
Goggo da Ilya, wanda yanzu ya zama na hannun daman Ma’arouf kuma babban (officer) na (catering) a gidan gwamnati sun dade da gane His Excellency son Amina yake yi, amma ita wawiyar har gobe ta sanya Baban Ameena a matsayin wani mutum mai son ci gabanta, mai kula da al'amuranta, mai darajja iyayenta da ‘yan uwanta. Mai son kowa nata.
Hatta Talatu da Zulai Jikas ya san da zamansu. Don haka itama a gare ta Ma'arouf Habibu Ji-kas, mutum ne mai daraja da kimada bata ajiye matsayin sa nan kusa a zuciyar ta ba, irin matsayin nan da kake baiwa babban Yayanka da kuke ciki daya.
A gefe ga kaunar da Hajiya ke mata kamar ta hadiye ta, kusan kullum sai sun yi waya. Kaji su suna hira rai-rai-rai kamar ‘ya da uwa. Amma bata cika zuwa ba. Hajiya na da wannan dadadden burin a zuciyarta na Allah ya hada zuciyoyin Ma'arouf da Amina, amma idan ta tuna tsarin da a kullum yake fadin ya yi wa rayuwarsa sai jikinta ya yi sanyi. Duk da haka tana addu'a idan Allah ya tashi sauya zuciyar Ma'arouf daga kan tsarinsa na auren mata daya kacal, Ya sanya Amina ce.
Ita ba za ta tilasta masa ya kara aure ba, ko ta tallata masa Amina ya zo ya ce a'ah ta zubar mata da martaba a banza a idanunsa.
A daya gefen zamansa da Laila na kara tabarbarewa. Kullum ba ta gida, in kuma tana nan za ka tadda falonta cike da kawaye da women leaders. Idonta ya bude sosai da harkar siyasa ta yadda har ba ta da lokacinsa. Ko tafiya ce ta kama shi ya nemi rakiyarta ba ya samu yanzu, za ta ce tana da biki, ko gayyatar taro ya je abinsa.
Tafiya ta yi tafiya aka gangara watanni goma sha daya. Ma'arouf Ji-kas ya soma ganewa, wato bayan ilmin likitancin tada mataccen kashi da Allah ya baiwa Amina, ita din fasiha ce, tana da sani a fannonin rayuwa daban-daban. A hankali zuciyarsa ta cigaba da afuwaga soyayyar Amina mai girman gaske.
A karshen wata na goma sha daya ne Amina ta duba asusunta. Kudin ciki sun ba ta tsoro, sai ta ga lokacin da ya dace ta cika burinta a kan Goggonta ya yi.
A wani yammaci ta kira Ilya kafin ya wuce gida, bayan ya tashi daga aiki. Suka zuna a wani hadadden dankaramin falo, ta gyara zama ta fuskanceshi, tace,
"Ilya, na kira ka ne don ka taimaka mani, na samu abin da zai ishe ni cika burina. So nake Goggo ta ji dadi a wannan siradin na rayuwarta. Ta daina wannan wahalalliyar sana'ar, shekarunta sun ja. Tana bukatar hutu.
Inaso Goggo nata daina shiga motar haya, ta je ta sauke farali. A rushe gidanmu a yi mata na zamani. Ga abinda nake da shi, gaba daya na damka wannan hidimar a hannunka.
Ina kuma rokonka kada ka gaya mata sai ka kammala komai. Aikin hajji kuwa, sai an sa musu ranar tashi za ka gaya mata".
Ilya ya dubi Amina, sai ya ga tana share hawaye.
"To kukan na mene ne kuma? Allah ya yi miki albarka Amina, Allah ya ba ki miji na gari da zuri'a mai albarka masu jin kan mahaifa. Hakika ni ma na yi wannan tunanin, lokaci ya yi da Goggo za ta huta haka a rayuwarta tunda dukkanmu ni da ke yanzu mun tsaya da kafafunmu, mun kawo karfi.".
Amina ta yi sharbe,
"Ba komai ya sa ni kuka ba Ilya, illa tuna Baba da na yi. How I wish shi ma yana raye? Ya shigo cikin inuwar ilmin da suka dora ni a kai? Suka tsaya min nayi? Allah ya yi masa rahama!".
"Daina kukan haka, ya isa. Ki ba ni wata guda, komai zai kammala a gabanta insha Allah. Amma maganar gini, ki ba ni wata biyu, ba nata za a rushe ba, sabo za a yi. In aka ce sai an rushe dole sai ta fito daga gidan, kuma sai ta tambayi ba'asi.
Sabon fili za a saya ayi sabon gini, a gaba kadan damu akwai wasu sababbin filaye da ake sayarwa kwanannan. Aikin hajj kuwa an kusa gama biyan na wannan shekarar, don haka zan hanzarta. Mota kuwa har Kwatano zani da kaina na auno mai kyau, ta zamani. Allah ya yi miki albarka".
Amina ta ce, "Ameen.Sai abu na biyu. So nake Goggo ta daina wannan sana'ar wahalar kwata-kwata daga lokacin da za ta tare a sabon gidanta, zan dinga raba albashina biyu duk wata ina bata rabi".
Ilya ya dan girgiza kai,
"Da kyar za ta yarda da wannan. Zan dai dauki ma'aikata a dinga biyansu su ci gaba da komai, nata ya zamo umarni".
*****
Gadan-gadan Ilya ya shiga aiwatar da aikin amanar da Amina ta damka masa. Sai da ya kammala komai, madaidaicin lodge dinGoggo mai brown rufi ya kammala, mota kirar (E-Class) ta iso. Matsala daya Ilya ya samu, wato dole Goggo ta je a yi mata fasfot da daukan hoto.
Daga baya dabara ta zo masa, ya je ya samu Goggo ya ce ta yi shiri su je wani waje za a yi musu takardar zama 'yan kasa, kuma dole sai an dauki hoto.
Goggo ba ta yi musu ba ta shirya suka jeimmigrationofficeaka yi mata fasfot ba da saninta ba. Aka dauke ta hoto, ba ta sa wa ranta komai ba, Ilya ya je ya biya kudin kujerar hajjin Goggo, aka yi mata visada komai aka sanya musu ranar tashi, sannan ne ya zo ya gaya wa Goggo komai ya damka mata fasfot dinta.
Goggo don dadi sai hawaye. Wai ita ce za ta je dakin Allah mai alfarma karkashin inuwar Amina. Lokacin Amina na government house, Goggo ta kira ta a waya.
"Sai kuma na ji wannan abin alheri haka? Aminan Goggo,Allah ya yi miki albarka, Ya baki miji nagari wanda zai tallafi maraicinki, ya rike ki da amana da kauna ta gaskiya".
Dadi ya rufe Amina, dama abinda take so kenan, (albarkar Goggo),cewa ta ke, "Amin-Amin Goggo, Goggo Allah Ya bar min ke!!!".
Ranar juma'a su Goggo suka tashi zuwa kasa mai tsarki. Don haka wannan satin Amina ta yi zamanta ba ta zo gida ba, ta ci gaba da kula da Ameena.
Idan Hajiya Hauwa tana dawafi a Ka’abah, ba abinda ta ke rokosai miji nagari ga Amina. Idan sujjadah ta yi a Maqama Ibrahima, addu'ar da ke kan halshenta kenan. Idan Safah da Marwah ta ke, roqon Allah ta ke ya fiddo wa Amina miji nagari cikin gaggawa. Yasa jinkirinta ya zame mata alkhairi. Ta yaya Allah zai juyar da wannan addu’ar ta UWA? Wannan shi ne kadai sauran burinta a rayuwa, sai neman cikawa da imani.
Goggo na can Makkah, Amina na dakinta na gidan gwamnati tare da patientdinta, wadda ke kwance kan cinyoyinta tana mata messaging a gabobinta. Sai kawai Ameena ta yunkura ta tashi zaune.
Dr. Amina ta ce, "Mene ne Amina?"
"Fitsari zan yi".
Kafin ta yi wani motsi na taimaka mata don mikewa, Ameenar ta mike da kanta a kan kafafunta (all of a sudden). Ta yi hanyar bayan gida.