Sashe 14
Sanadin Kenan Part 3 Complete Hausa Novel · about 3 min read
DANDANO DAGA
AUREN KWANGILA!
(Littafin Takori mai zuwa)
H
awaye masu dumi suka biyo idanun Ambassada Hamza, bai damu da ya kai hannu ya share ba, haka ya barsu suka yi ta malala akan kundukukinsa, abokan nasa suka ci gaba da ba shi baki, ba su san kuka biyu yake yi ba; kukan rashin mahaifiyarsa da kukan nadama...!!! Rayuwa kenan.
Hafsat bata san bidirin da Daddy ke yi da zuciya da kwakwalwar sa ba, ta sayo wa Mammah katin wayar da ta aike ta ta kamo hanyar dawowa. Tafiya take kanta a sunkuye don bazata iya daga ido ta dubi taron mazan nan dake zazzaune a kofar gida ba. Kamar ance da ita ‘dago kanki’ gab da zata shiga gida ta dan daga kai sabida jikinta ya bata ana kallonta sosai, ai kuwa karaf! Sai idanunta cikin na Daddy. Ta ganshi yana shatatar hawaye kamar karamin yaro, sukayi ido hudu dashi. Tuni ta gigice ta saki katin wayar da canjin kudin ta ci uban tuntube da wani katon dutse dake kofar shiga gidan an tare kofar dashi, ta fadi kiff! A kasa. Don tayi tsammanin a cikin mutanen nan balbaleta zaiyi da balbalin bala’in nasa.
Ji tayi ansa hannu biyu an dago ta, ta ji zafin faduwar sosai da sosai, gwiwoyinta duk sun kukkuje leben ta ya fashe jini ya wanke bakin. Ta cira ido a sannu cikin dauriya ta dubi wanda ya daga ta; Hamza Atiku Dakata ne.
“Wace irin tafiya kikeyi haka Addah? Ba kya kallon abinda ke gabanki, Addah in don ni kika rude haka don Allah kiyi hakuri, kar ki sake firgita in kin ganni, ba dodo bane ni, BABAN KI NE!!!
Hafsat-Suhaana, ta runtse idanunta, mafarki ne kawai ire-iren mafarkan da ta saba yi akan Daddyn, saboda yadda tasa damuwa da lamarin sa a ranta. Ta ki bude idon don bata so ta farka daga wannan daddadan mafarki. Daddy yasa hannu ya dauko hankicinsa daga aljihunsa fari tas dashi ya shiga goge jinin da ke zuba daga bakinta. Mutane wajen bakwai suka taso suka isko su.
Nan da nan labari ya isa ga Mammah, daga bakin dan Anty Mariya, wai Addah ta fadi a waje. Daddy ya sa an tafi da ita a mota a kaita asibiti. Sai taji maganar banbarakwai, ina ruwan Daddy da Suhaana har da zai ce a kaita wani waje a mota? Kar dai fa ya aika da ita GIDAN MARAYUN da yake ikirari? Tayi wata irin zabura ta mike, da gudunta tayi waje har zaninta na kwancewa ko mayafi babu a jikinta tayi hanyar soro, uban karo suka gabza da Daddyn yana kokarin shigowa saura kadan su fadi. Jikinta na bari, muryarta na karkarwa cikin son fashewa da kuka ta kama shi tana girgizawa.
“Ina Hafsat? Ina Addah ta? Ina ka tura a kaita? Ina ‘ya ta ina ‘yar amana ta???”.
AUREN KWANGILA!
Littafin
SUMAYYAH ABDULKADIR
(Goron Sabuwar Shekara)
Yana zuwa ba da jimawa ba insha Allahu.
AUREN KWANGILA!
(Littafin Takori mai zuwa)
H
awaye masu dumi suka biyo idanun Ambassada Hamza, bai damu da ya kai hannu ya share ba, haka ya barsu suka yi ta malala akan kundukukinsa, abokan nasa suka ci gaba da ba shi baki, ba su san kuka biyu yake yi ba; kukan rashin mahaifiyarsa da kukan nadama...!!! Rayuwa kenan.
Hafsat bata san bidirin da Daddy ke yi da zuciya da kwakwalwar sa ba, ta sayo wa Mammah katin wayar da ta aike ta ta kamo hanyar dawowa. Tafiya take kanta a sunkuye don bazata iya daga ido ta dubi taron mazan nan dake zazzaune a kofar gida ba. Kamar ance da ita ‘dago kanki’ gab da zata shiga gida ta dan daga kai sabida jikinta ya bata ana kallonta sosai, ai kuwa karaf! Sai idanunta cikin na Daddy. Ta ganshi yana shatatar hawaye kamar karamin yaro, sukayi ido hudu dashi. Tuni ta gigice ta saki katin wayar da canjin kudin ta ci uban tuntube da wani katon dutse dake kofar shiga gidan an tare kofar dashi, ta fadi kiff! A kasa. Don tayi tsammanin a cikin mutanen nan balbaleta zaiyi da balbalin bala’in nasa.
Ji tayi ansa hannu biyu an dago ta, ta ji zafin faduwar sosai da sosai, gwiwoyinta duk sun kukkuje leben ta ya fashe jini ya wanke bakin. Ta cira ido a sannu cikin dauriya ta dubi wanda ya daga ta; Hamza Atiku Dakata ne.
“Wace irin tafiya kikeyi haka Addah? Ba kya kallon abinda ke gabanki, Addah in don ni kika rude haka don Allah kiyi hakuri, kar ki sake firgita in kin ganni, ba dodo bane ni, BABAN KI NE!!!
Hafsat-Suhaana, ta runtse idanunta, mafarki ne kawai ire-iren mafarkan da ta saba yi akan Daddyn, saboda yadda tasa damuwa da lamarin sa a ranta. Ta ki bude idon don bata so ta farka daga wannan daddadan mafarki. Daddy yasa hannu ya dauko hankicinsa daga aljihunsa fari tas dashi ya shiga goge jinin da ke zuba daga bakinta. Mutane wajen bakwai suka taso suka isko su.
Nan da nan labari ya isa ga Mammah, daga bakin dan Anty Mariya, wai Addah ta fadi a waje. Daddy ya sa an tafi da ita a mota a kaita asibiti. Sai taji maganar banbarakwai, ina ruwan Daddy da Suhaana har da zai ce a kaita wani waje a mota? Kar dai fa ya aika da ita GIDAN MARAYUN da yake ikirari? Tayi wata irin zabura ta mike, da gudunta tayi waje har zaninta na kwancewa ko mayafi babu a jikinta tayi hanyar soro, uban karo suka gabza da Daddyn yana kokarin shigowa saura kadan su fadi. Jikinta na bari, muryarta na karkarwa cikin son fashewa da kuka ta kama shi tana girgizawa.
“Ina Hafsat? Ina Addah ta? Ina ka tura a kaita? Ina ‘ya ta ina ‘yar amana ta???”.
AUREN KWANGILA!
Littafin
SUMAYYAH ABDULKADIR
(Goron Sabuwar Shekara)
Yana zuwa ba da jimawa ba insha Allahu.