Sashe 11
Sanadin Kenan Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Hawayen farin ciki suka zubo wa Amina, ta kai tafin hannunta ta share su.
"Na amince Baban Ameena, ko gobe ka kawo sadaki a daura mana aure".
Runtse idanunsa ya yi yana gode wa Allah cikin zuciyarsa. Bai yi zaton al’amarin zai zo masa haka da sauki ba, a yadda ya fahimta Amina bata san so ba, bata san komai da ya dangance shi ba,bata da hope akan shi, she’s naive,innocent, yayi zaton zai sha wahala kafin ya karkato da zuciyarta ya fahimtar da ita har kafin ta amince masa. A fili yace.
“lefe kuma fa? Ko shima an yafe mini? Kamar yadda aka ce da Turaki an yafe mini Tantabaru?”
Dariya ta subuce mata, ta kai tafin hannunta ta rufe fuskarta. Yana jiyo sautin dariyar data ke yin da ya jefa shi cikin wani matsanancin nishadi, zuciyarsa tayi kal itama tata zuciyar tayi fes! Duk damuwoyin dake cikin ranta sai ta nemesu ta rasa.
Wani irin yanayi take ji a kirjinta mai dadin da bazai misaltu ba.Ta tambayi to kanta, to ko wannan shine ‘Son’ data ki amincewa da gangan shine saida ta samu zuciyar Jikas din?
“Ke nake sauraro Amina, ko shima lefen baza’a karba ba sadaki kawai za’a karba?”.
Matsananciyar kunya tayi mata lullubi, amma jin ita yake sauraro kuma yana son jin ta bakinta akan abinda yace din sai ta daure ta magantu.
“If my humble consultant ya kawo ai bani da ikon mayarwa saboda karfin ikonsa a kaina. In yace bazan karba ba ma Dr. Turaki ya isa da ni”.
“Naga alama, shiyasa nima yake juya ni yadda ransa yake so don ya san ya isa da ‘yar tasa. Well, yanzu ki bani labari, hira nake so mu yi, irin wadda bamu taba yi ba”.
Murmushi tayi “Baban Ameena kenan. Akwai hirar da bamu taba yi bane tsayin shekara guda?”
Hirar ai kala-kala ce kuma kowacce da lokacin ta. We always talked on politics, bamu taba yin hira irin ta zuciya da zuciya ba, ban taba gaya miki wacece ke a zuciyar Ma’arouf ba. Girman matsayinki, da yadda kikayi overwhelming ruhi da zuciyar sa ba.
Ke ko dan ‘Ji-kas’ din da ake fada ma ba ki iya ba, you always call meBaban Ameena? This is not my name.It didn’t deserve you. Ki ba ni wani sunan ko ki kira ni da sunan da iyayena suka ba ni, zan fi son hakan, zan fi farin ciki da shi".
Ajiyar zuciya tayi, in wani ya gaya mata MA’AROUF JI-KAS yana magana haka, yanada baki har haka zata karyata, kalaman sa na kullum a kayyade suke koyaushe masu tarin ma’ana da hikima musamman a media, zababbu kuma dai-daiku kafin ya furta, yau gashi yanata zuba kamar ‘ya’yan kanya. Yau ta yarda ta amince soyayya gaskiya ce kuma ba wanda yake iya iko da kansa akanta, ta tabbata da Ma’arouf bai so ta har haka ba.
Murmushi tayi, wani irin tattausan murmushi da batasan daga ina ya fito ba tsakanin zuciya da ruhi. Ta san dai na tsananin jin dadin kalamansa ne. Duk da bata taba ko da gwada fadar sunan Ma’arouf Ji-kas ba, saboda nauyin da yake mata. A yau zuciyarta ta amince ta fada din,tunda ya ce fadar za ta sanya shi farin ciki. Ita kuma burinta kenan, ya kasance cikin farin ciki har karshen rayuwarsa.
"Good night MA'AROUF". Ta fada da dan sauri, ta yi hanzarin kashe wayarta, ta tura kasan filo, ta bi ta karkashin filon ta tusa fuskarta suka buya tare. Kunyar Dr. Amina yawa ne da ita.
Murmushi ya yi da ya fahimci ta kashe wayarta, zuciyarsa ta nutsu sosai, sai godiyar Allah ne fal a cikinta. Ya amince daga kwanaki casa’in masu zuwa zai fara wata irin rayuwar aure mai nagarta kamar kowanne dan Adam, irin tashi ta farko da wadda bazai taba mantawa ba koma fiyeda ita, ba irin wadda yake yi da Laila Ji-kas ba.
Burin da yake dashi akan rayuwar da zaiyi da Ameena mai yawa ne saboda soyayyar ta ma mai yawa ce, mai tsayi da fadi. Wadda ta cike filin zuciyar taf! Babu wani gurbi da wata ‘ya mace zata sake samu he believed.
****
Sati biyu da yin haka ya kara yin bad-da-kama ya zo don jin me Amina ta shirya wa aurensu?
A babban falon Goggo suke, Amina ta cika shi da ababen sha masu sanyi, wadanda ta sarrafa da hannunta daga 'fruits'. Yana kan kujera tana zaune a kan kilishi. Yanzu kunyarshi da ta ke ji ta ragu sosai, tana iya bude baki ta yi magana a gabansa babu jin nauyi. Sabida yadda yake jan ta da hira sosai a waya, ya maida kansa matashi dan ashirin da shidda kamarta. Tun daga ranar da suka yi wayar farko, duk dare sai ya kirata sun sha hira mai dadi da kara fahimtar juna da sanya dankon soyayya a zukatan su.
Amina ta muskuta ta gyara zamanta ta tattara hankalinta akan Ma’arouf din.
"Shirye-shirye nasu ne, bana son a sanar da daurin aurenmu a kowacce kafar sadarwa, a dauro a Shira, zan yi walima a nan gidanmu don 'yan uwa, iyaye, abokan karatu, na aiki da duk wasu abokan arziki. These are my programme of events your Excellency, please don't say no!".
Murmushi Ma'arouf Ji-kas ya yi, kwayar idanunsa a kanta da wani irin yanayi a cikinsu. Ita kuma sai ta sadda kanta cikin jin kunya. A tausashe ta tsinkayi furucinsa cikin kunnuwanta. Daga ji ba shi yake sarrafa kalaman bakinsa ba, suna sarrafa kansu ne tun daga karkashin zuciyarsa.
"A kan me zan ce NO? Bayan kowa da irin yadda yake tafiyar da tsarin rayuwarsa? Wanda ya tafiyar da rayuwarsa da sauki,ya kuma dauketa da saukin,shi ya huta. Ina da irin ra'ayinki a wasu bangarorin Aminahhh, ina sonki, ina yinki, ana mugun tare!!!".
Amina ta yi dariya, har fararen hakoranta suka bayyana, dariya sosai mai kyau da ban sha’awa, wadda ta nuna halin farin cikin da kalaman sa suka jefa zuciyarta.Shi ma ya taya ta. Sukayi abarsu mai isarsu. Goggo na daki tana jiyowa, da ma a kan sallayarta ta ke, ta idar da sallar lsha kenan, sai ta dungura ta yi wa Allah sujjadah, ta gode maSa da ya share mata hawayenta, Ya bai wa Aminanta irin mijin da kullum ta ke mata addu'ar samu, kafin Ya dau ranta. Tsarki ya tabbata ga Sarki Allah!!!
****
"Na amince Baban Ameena, ko gobe ka kawo sadaki a daura mana aure".
Runtse idanunsa ya yi yana gode wa Allah cikin zuciyarsa. Bai yi zaton al’amarin zai zo masa haka da sauki ba, a yadda ya fahimta Amina bata san so ba, bata san komai da ya dangance shi ba,bata da hope akan shi, she’s naive,innocent, yayi zaton zai sha wahala kafin ya karkato da zuciyarta ya fahimtar da ita har kafin ta amince masa. A fili yace.
“lefe kuma fa? Ko shima an yafe mini? Kamar yadda aka ce da Turaki an yafe mini Tantabaru?”
Dariya ta subuce mata, ta kai tafin hannunta ta rufe fuskarta. Yana jiyo sautin dariyar data ke yin da ya jefa shi cikin wani matsanancin nishadi, zuciyarsa tayi kal itama tata zuciyar tayi fes! Duk damuwoyin dake cikin ranta sai ta nemesu ta rasa.
Wani irin yanayi take ji a kirjinta mai dadin da bazai misaltu ba.Ta tambayi to kanta, to ko wannan shine ‘Son’ data ki amincewa da gangan shine saida ta samu zuciyar Jikas din?
“Ke nake sauraro Amina, ko shima lefen baza’a karba ba sadaki kawai za’a karba?”.
Matsananciyar kunya tayi mata lullubi, amma jin ita yake sauraro kuma yana son jin ta bakinta akan abinda yace din sai ta daure ta magantu.
“If my humble consultant ya kawo ai bani da ikon mayarwa saboda karfin ikonsa a kaina. In yace bazan karba ba ma Dr. Turaki ya isa da ni”.
“Naga alama, shiyasa nima yake juya ni yadda ransa yake so don ya san ya isa da ‘yar tasa. Well, yanzu ki bani labari, hira nake so mu yi, irin wadda bamu taba yi ba”.
Murmushi tayi “Baban Ameena kenan. Akwai hirar da bamu taba yi bane tsayin shekara guda?”
Hirar ai kala-kala ce kuma kowacce da lokacin ta. We always talked on politics, bamu taba yin hira irin ta zuciya da zuciya ba, ban taba gaya miki wacece ke a zuciyar Ma’arouf ba. Girman matsayinki, da yadda kikayi overwhelming ruhi da zuciyar sa ba.
Ke ko dan ‘Ji-kas’ din da ake fada ma ba ki iya ba, you always call meBaban Ameena? This is not my name.It didn’t deserve you. Ki ba ni wani sunan ko ki kira ni da sunan da iyayena suka ba ni, zan fi son hakan, zan fi farin ciki da shi".
Ajiyar zuciya tayi, in wani ya gaya mata MA’AROUF JI-KAS yana magana haka, yanada baki har haka zata karyata, kalaman sa na kullum a kayyade suke koyaushe masu tarin ma’ana da hikima musamman a media, zababbu kuma dai-daiku kafin ya furta, yau gashi yanata zuba kamar ‘ya’yan kanya. Yau ta yarda ta amince soyayya gaskiya ce kuma ba wanda yake iya iko da kansa akanta, ta tabbata da Ma’arouf bai so ta har haka ba.
Murmushi tayi, wani irin tattausan murmushi da batasan daga ina ya fito ba tsakanin zuciya da ruhi. Ta san dai na tsananin jin dadin kalamansa ne. Duk da bata taba ko da gwada fadar sunan Ma’arouf Ji-kas ba, saboda nauyin da yake mata. A yau zuciyarta ta amince ta fada din,tunda ya ce fadar za ta sanya shi farin ciki. Ita kuma burinta kenan, ya kasance cikin farin ciki har karshen rayuwarsa.
"Good night MA'AROUF". Ta fada da dan sauri, ta yi hanzarin kashe wayarta, ta tura kasan filo, ta bi ta karkashin filon ta tusa fuskarta suka buya tare. Kunyar Dr. Amina yawa ne da ita.
Murmushi ya yi da ya fahimci ta kashe wayarta, zuciyarsa ta nutsu sosai, sai godiyar Allah ne fal a cikinta. Ya amince daga kwanaki casa’in masu zuwa zai fara wata irin rayuwar aure mai nagarta kamar kowanne dan Adam, irin tashi ta farko da wadda bazai taba mantawa ba koma fiyeda ita, ba irin wadda yake yi da Laila Ji-kas ba.
Burin da yake dashi akan rayuwar da zaiyi da Ameena mai yawa ne saboda soyayyar ta ma mai yawa ce, mai tsayi da fadi. Wadda ta cike filin zuciyar taf! Babu wani gurbi da wata ‘ya mace zata sake samu he believed.
****
Sati biyu da yin haka ya kara yin bad-da-kama ya zo don jin me Amina ta shirya wa aurensu?
A babban falon Goggo suke, Amina ta cika shi da ababen sha masu sanyi, wadanda ta sarrafa da hannunta daga 'fruits'. Yana kan kujera tana zaune a kan kilishi. Yanzu kunyarshi da ta ke ji ta ragu sosai, tana iya bude baki ta yi magana a gabansa babu jin nauyi. Sabida yadda yake jan ta da hira sosai a waya, ya maida kansa matashi dan ashirin da shidda kamarta. Tun daga ranar da suka yi wayar farko, duk dare sai ya kirata sun sha hira mai dadi da kara fahimtar juna da sanya dankon soyayya a zukatan su.
Amina ta muskuta ta gyara zamanta ta tattara hankalinta akan Ma’arouf din.
"Shirye-shirye nasu ne, bana son a sanar da daurin aurenmu a kowacce kafar sadarwa, a dauro a Shira, zan yi walima a nan gidanmu don 'yan uwa, iyaye, abokan karatu, na aiki da duk wasu abokan arziki. These are my programme of events your Excellency, please don't say no!".
Murmushi Ma'arouf Ji-kas ya yi, kwayar idanunsa a kanta da wani irin yanayi a cikinsu. Ita kuma sai ta sadda kanta cikin jin kunya. A tausashe ta tsinkayi furucinsa cikin kunnuwanta. Daga ji ba shi yake sarrafa kalaman bakinsa ba, suna sarrafa kansu ne tun daga karkashin zuciyarsa.
"A kan me zan ce NO? Bayan kowa da irin yadda yake tafiyar da tsarin rayuwarsa? Wanda ya tafiyar da rayuwarsa da sauki,ya kuma dauketa da saukin,shi ya huta. Ina da irin ra'ayinki a wasu bangarorin Aminahhh, ina sonki, ina yinki, ana mugun tare!!!".
Amina ta yi dariya, har fararen hakoranta suka bayyana, dariya sosai mai kyau da ban sha’awa, wadda ta nuna halin farin cikin da kalaman sa suka jefa zuciyarta.Shi ma ya taya ta. Sukayi abarsu mai isarsu. Goggo na daki tana jiyowa, da ma a kan sallayarta ta ke, ta idar da sallar lsha kenan, sai ta dungura ta yi wa Allah sujjadah, ta gode maSa da ya share mata hawayenta, Ya bai wa Aminanta irin mijin da kullum ta ke mata addu'ar samu, kafin Ya dau ranta. Tsarki ya tabbata ga Sarki Allah!!!
****