← Book details Sanadin Kenan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 17

Sashe 10

Sanadin Kenan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

daya ko na biyu. Ba ta so katse mata baccin ba don da alama tana jin dadinsa. Ta dade tsaye a kanta tana kallonta tana yi mata addu in nasarar rayuwa cikin zuciyarta, miji na gari, wanda shi ne abin da ya fi tsaya wa Goggon a zuciya tun sanda ta lura ta fara al ada (jinin haila). Daga bisani ta tashe ta, ta yi wata irin doguwar mika da doguwar hamma, sannan ta mike don dauro alwala. Ko sallar isha ba a idar ba Hafiz ya yi sallama, dukkansu suna tsakar gida kowa kan abin sallarsa daban suna bin jam in masallacin da ke kusa da su daga nan inda suke. Sai ya karasa gindin famfo ya daura alwala, shi ma ya fita ya nufi masallacin. Kafin ya dawo Amina ta cika ta yi fam! Tana neman wajen gudu a zuciyarta, Goggo Zulai ta je kauye kamar yadda Goggo ta fada mata, ga ta ita ba gwanar shige-shigen gidan makwabta ba. Ba ta gama tunaninta ba ta ji sallamar Hafiz, ya dawo. Ya ja kujera ya zauna yana fuskantarta tana zaune a kan sallaya ko kunyar Goggo bai ji ba. Fuskar nan ta Amina ta kirne kamar wadda aka fasa wa danyen kwai a kanta. Goggo ta ce, An gama tuwo Hafizu Bar tuwon nan yau Goggo, murnar ganin Amina ba za ta barni in ci ba Ta shige daki ta rabu da su. Amina ta mike tana kokarin bin bayan Goggo, Hafiz ya ce, Don Allah, don Annabi Amina ki zauna, na yi miki alkawarin yau zan saurare ki in ji uzurinki da kalaman bakinki, in na gamsu da su, wallahi zan kyale ki, zan fita daga rayuwarki kamar yadda ki ke so Jikinta ya yi sanyi sakamakon yadda yake maganar (with a gesture), ya kuma nuna zai aikata abin da ya ce zai aikata din in har ta saurare shi. Ta sake shimfida sallayar ta koma ta zauna, amma ba ta kallonshi, wani gefen daban ta ke kallo. Ya dau mintuna biyu bai yi magana ba, ita ma ba ta nuna ta kosa ya yi maganar ba. Daga bisani ya ce, Tun ranar da Allah ya sa na fara ganinki duk da na sanki tun kina karama, ranar da na ganki a girmanki, Ubangiji ya jarrabe ni da ciwon sonki, kauna wadda nake fatan ta kai mu ga aure. Ban boye ba na nuna wa iyayena da Goggonki tun a lokacin. Amma minti guda ba ki taba ba ni don mu fahimci juna ba, duk da an ce labarin zuciya a tambayi fuska na fuskanci ba ki sona, kin tsane ni, ko me ya sa Amina? Amina ta hadiyi miyau, yau kam ta yanke shawarar ta bude baki ta magantu ko Hafiz ya shafa mata lafiya. Ni wallahi ban tsane ka ba Kamar daga sama Hafiz ya ji ta fada. Kamin ya farfado daga dadin da kalaman suka yi masa Amina ta ci gaba. Duk kusancina da mutum, duk kaunar da nake masa, in ya ce yana sona sai in ji duk duniya babu wanda na tsana irinsa. Kai dan uwana ne na jini, dole akwai kauna ta yan uwantaka, da za ka janye kalaman soyayya ko aure a tsakaninmu, lafiya za mu zauna Abin ya kusa bai wa Hafiz dariya, wato wannan so na aure da yake furtawa shi ne ba ta so ba shi ba. To ban da abin Amina me ye amfanin zumuncin mace da namiji in ba soyayya ce a ciki ba? Ya tattara kalamansa ya dunkule su cikin hikima, Amina, me ya sa ba kya so a ce ana sonki? Kai tsaye ta amsa, Saboda in Goggo ta samu tsayayye kwakkwara, aure za ta yi min, ba za ta bar ni in gama karatun da nake so in yi ba Hafiz ya girgiza kai, ya kuma fahimce ta, To ke kuwa Amina wane irin karatu ne wannan da zai hana ki aure? Amina ba ta ce komai ba, don a ganinta wannan ba huruminsa ba ne. Da bai samu waccan amsar ba, sai ya karo wata, In na jiraki ki ka gama karatun da ki ke so ki yi din, a kalla nan da shekaru goma, in kin kare za ki yarda ki aure ni ko da a mata ta biyu ne? Amina ta mirgina kai, Ban yi alkawari ba, saboda Allah shi Ya san gobe. Za dai ka shiga cikin manema in akwai su Hafiz ya rasa ta inda zai billo mata, yarinya na magana da cikakkiyar kwakwalwa kamar ta girme shi. Gara ya sanya wa ransa salama a kan Amina. *** *** *** Tun daga wannan ranar Goggo ta lura Hafiz ya dauke sawunsa daga gidanta. Ta sa Amina a gaba da fada kamar ta ari baki, ta tambaye ta ta gaya mata abin da ta yi masa, Amina ta ce, ita kawai ce masa ta yi ba yanzu za ta yi aure ba. Sai Goggo ta koma lallashi da nasiha, tana nuna mata ta daina wulakanta masu kaunarta, ta bi rayuwa a hankali, ta cire dogon buri. Duk da Hafiz ya hakura da Amina bai fasa zuwa jefi-jefi ya gaida Goggo ba, lokacin Amina ta koma makaranta. A gefe mahaifiyarsa na ta yin nata kokarin wajen malamanta don a yi masa firraqu da Amina. Sanda Hafiz ya gaya mata ya hakura da Amina ta samo masa mata, don shi ba shi da idon kallon kowacce mace a duniya ba Amina ba, ta wani bangaren kuma ya matsu da ya yi auren ne a wannan dan tsukin ko ya samu nutsuwa ya fidda Amina a ransa. Atika sai ta yarda kokarinta ne ya raba su, ta kara yarda da malamanta, ta kuma kara musu ihsani. Ta soma yi masa fafutukar auren yar kawarta mai suna Siyama, wadda ta fito daga gidan da ya gamsar da ita, ba wadanda za su zame musu (liability) ba. Lokaci ba ya jiran dan Adam, haka yake ta mirginawa cikin kudura da iradar Ubangiji. A yau Amina ta gama dukkan jarrabawoyinta na fita sakandire. Amina da Goggonta Hauwa sun yi godiya ga Allah da Ya nuna musu wannan ranar. Sun rabu ita da Hafsa kowa na sharar hawaye da alkawarin ziyartar juna in Mai duka ya yarda. Amina ta yi wa Hafsa alkawarin zuwa bikinta har Abuja idan Goggo ta amince, domin ba zai dauki lokaci ba, ita ake jira ta kare karatun nata, ga shi kuma an gama cikin yardar Ubangiji. Amina sai zaman gida don jiran fitowar sakamako. Ta yi kace-kace cikin taimaka wa sana ar Goggonta, duk karfin ayyukan ita ce don Allah bai halicce ta da kuiya ba. Sun je ita da Ilya sun bude asusu da sunan Amina da bankin (firstbank), aka ci gaba da zuba ribar kasuwancin Goggo a ciki. **** AMINA A JAMI Sakamakon bai dauki watanni uku ba kamar yadda ake yi a wancan lokacin, ya fito. Amina sai sam-barka ta lashe komai. Goggo ba ta yi wahalar banza ba. Babu jimawa ta samu gurbin da ta nema a kuma fannin data nema a ATBU a kananun shekarunta goma sha shidda, sakamakon (double promotion) da aka yi mata a karamar sakandire da firamare. Tun daga shige da fice na (registration) da ta fara ta lura ta kuma amince tafiyar ba mai sauki ba ce, don haka ta kara ba da himma. Manema kuma suka ce mata salamu alaikum, kamar da ma jira suke ta kare sakandiren ta fara jami a. ba ta sauraron kowa, kuma ba ta barin Goggo ta gane tana korarsu ne tun kafin su biyo ta gida. Lokacin da Amina ta shiga shekara ta karshe a jami ar Tafawa Balewa inda ta ke hada B.Sc dinta a Physiotherapy , wanda ta kwashe shekaru biyar tana yi, Goggo Hauwa ta soma shiga damuwa a kan rashin kwakkwaran manemi ga Aminar, a lokacin ta cika shekaru ashirin da daya a duniya. Abin ya soma damunta sosai. An tura su Amina internship na shekara daya a asibitin koyarwa (Abubakar Tafawa Balewa Teaching Hospital), bayan kammala B.Sc dinta, jininsu ya hadu da (consultant) dinsu Dr. Usman Turaki saboda kokarinta. Dr. Turaki na yabawa Amina sosai, yana kiranta Young Doctor , don duk cikin team dinsu da ke karkashin Dr. Turaki ita ce karama. Amina na girmama Dr. Usman Turaki don ta lura mutumin kirki ne mai tsanteni da mutuncinsa, ba shi da wasa ko kadan ga rikon addini. Duk sanda yake koyar da su da zarar an kira sallah, to fa zai katse ya yi umarni ga musulman cikinsu su je su yi sallah, sannan bai taba yi mata maganar banza ba, don haka tasu ta zo daya suke ganin mutuncin juna, duk abin da ya shige mata duhu shi ta ke samu, shi ya shige mata gaba ta ke samun (scholarship) daga gwamnatin jiha, ko da ba ta gaya masa komai da ya danganci (personal life) zahirin rayuwarta ba, ya lura iyayenta masu karamin karfi ne, an kuma taba gaya masa Babanta ya rasu, wannan scholarship da ta ke samu duk shekara ba karamin taimakawa yake yi ba. *** *** *** Goggo Hauwa da aminiyarta Zulai Babar Ilya, a dakin Goggon suke tattaunawa a kan damuwar Goggon. Na rasa daga ina matsalar ta ke? Aminatu sam ba ta da niyyar aure a rayuwarta Zulai, boko dai, boko dai? Ina ki ka fito? Asibiti, ina za ki? Asibiti! Babu mashinshini ko daya, lamarin nan yana tayar min da hankali, mu shekarunmu goma sha hudu aka yi mana aure, yau Amina in watan nan ya mutu shekarunta ashirin da uku. Yaushe ne ta ke tunanin ajiye iyali na kanta? In na tambaya babu manemi ta ce babu, ga Hafizu da ta kora yanzu yaransa biyu, jiya suka zo shi da maidakinsa da yaransa ba ki gani ba abin sha awa, ta san ta yi ta yin nan-nan da yaran wasu, amma ko miskala zarratin ba ta damu da itama ta yi ba, sai hidima da na mutane Goggo Zulai ta gyara zama, Kina nema wa yarinyar nan taimako kuwa? Yanzu ba wuya aljanu sun auri bil adama su cire musu son aure a ransu, ga jifa irin na marasa imani dole ki mike tsaye Goggo ta girgiza kai, In dai irin wannan mikewa tsayen ne ba zan taba mikewa
Chapter 10 · 0% Book details