← Book details Sai Na Auri Marubuci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 18

Sashe 8

Sai Na Auri Marubuci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Nafseen kuwa ta bude data tare da zumudin ganin Erin amsan da samu wajen Nafeesa amma me sai yaji shiru Kawai ji yayi ransa ya baci ma ko group din be shiga ba ya rupe datan sai kuma ya fara tunani shi kadai "to meye ma bashi na damuwa har haka yayi kokarin cire tunanin ta aransa amma hakan be samu ba Sabida Nfeesa Yarinya ce shagwababbiya Edan yana tuna Erin yadda take masa shagwaba sai yayi murmushi kuma sai yakara cewa meke damu na ne Haka to mema zaisa na damu haka, Abu daya yake tunawa salon yarinya yana matukar birgesa gata yarinya Amman in tai wani abun babbama ba zai ba, duk abunnan bai taba ganin hotonta ba kuma bai taba tambaya ba Amman yana sawa aransa cewa kyakkyawace ajin farko kamar yadda halinta da kalamanta suke.

Maryam bayan tadawo addu,a ta karama ma Nafeesa ta kwanta aiko can cikin dare wajen 2:00 taji nafeesa na "Abhhi Dan Allah kayi hakuri kabani wayana na san Nafseeen ya min reply." Nan take ta fashe da kuka , Maryam ta riketa.

"Abhi ka taimaka min kaji Dan Allah Wallahi rabani da wayannan kaman Ana min baraxana da rayuwats ne Abhi plxxx ."

Maryam ta ce, "haba Nafeesa ki dawo hankalinki mana Wai yau ke ce Kika tashi ba addu',ah a bakinki keda Kike yima wasu fada akan addu'ah amma ace yau kene kika tashi ba ita?"

nan Nafeesa ta Fara share hawaye ta ce, " Astagfiirullah addu'a ta fara jerowa tana hawaye tana tuna abin da ya Faru Wai da gaske Abhi ya amshi wayana gaskiya bazan iya jure hakan ba.

tana wannan tunanin Maryam tace , "Mata babe oya a tashi a yi sallah ko nan ta Mike tayi alwala ta rama dukkan sallanta ta dear tana edarwa tasa kuka tace, " Maryam meya hanani tafiya kuma Wai da gaske ne Abhi ya kwace min wayana Maryam Idan ya baki ki bani ne Dan Allah kar kimin wasa kinsan yadda nakejikuwa?"
Maryam da hawaye suka cika mata Edo ta ce, ' nafeesa ki kwanta ki huta zamuyi maganagobe kinji."

kuka Nafeesa takara sautinsa "plss Maryam kibani amsa Dan Allah." Maryam ta ce ,"promise zan fada Miki gobe amma yanzu ki samu ki huta da kyar Maryam ta lallaba nafeesa ta hakura akan sae gobe.

Wa she gari

Ana kiran asuba Nafesa ta Fara tashin Maryam Sabida ita bacci ko na second daya be dauke ta ba hasalima hangowa take Erin amsan da Nafseen ya tura Mata gobe Maryam na bata wayan shi zata fara dubawa nan suka yi alwala sukayi sallah Nafeesa ta ce , "to ban wayan Habibbty."

Maryam ta ce, "baby girl ki saurari abin da zan fada Miki ."

Nafeesa ta ce , ,"to ban wayan sai muyi maganar."

Nafeesa Maryam ta fada cikin raunanniyar murya Mai dauke da damuwa nan da nan Nafeesa ta ba da attention dinta wa Maryam Sabida tasan abind a zata pada Mata yanada mahimmanci.

"inajinki baby girl da farin cikin ki Dana su Abhi wanne kika fi so ?"

Cewar Maryam.

Nafeesa ta ce, " Na su Sabida suma koda yaushe suna hana Kansu farin ciki domin suga nasamu."

Maryam ta ce to, " yanzu suma suna bukatan taemakonki da kuma kulawanki ."

Nafeesa ta ce , "akan me kenan ?"

Maryam ta matso kusa da Nafeesa tana , "Babe dole zaki yi hakuri da amsan wayan ki wajen Abhi Sabida farin cikin sa domin yana kallon kaman wayan na hanaki samun Hutu dole ki yadda da abin da yayi kiyi hakura ki danne damuwanki a gabansu dukda nas an da ciwo kan amma kiyi hakan Saboda su nasan edan kinyi haka Abhi zaiji dadi kin bi magna din sa yadda Kike nuna so a wayan ki nuna hakan tamkar be dameki ba Edan har Anga hakurinki wayan zai dawo wajenki soon."

Tunda Maryam ke mgnan nafesa kafeta tayi da ido ko kiftasu batayi ga farin cikin ta gaban iyayenta wanne zata bi?

Nafeesa ta...

😍😍MASOYA ASANI CIKIN ADDU'AH IN ANYI SALLAH PLEASE❤️TANAN NABI BUKATAR SOYAYYARKU GARENI,ALLAH BIYA MANA BUKATUNMU NA ALKAIRI👏

Urs Xayyeesherth❤https://www.facebook.com/106494781436168/

_*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_
_(Nafseen)_

*NOBLE WRITERS ASSOCIATION*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
_Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
NA
XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH

✨6STARS INDEED

_*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_

PAGE 17

BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM

*WANNAN FEJIN NAKINE DOTE HAUWA SULAIMAN😍😍BARKA DA KARA SHEKARA,INA MIKI FATAN NASARA ARAYUWARKI,MIJI NA GARI,ILIMI MAI ALBARKA INA YINKI IRIN SOSAI DINNANDINNAN*❤️

*TUKWICE GAREKI ANTYNA FARIDA MUSA (SWEERY)😍IDAN BABU KE KUSA DANI DOLE NAYI KUKA MATUKAR GASKE,BA ZAN IYA MIKI SO KADAN BA SON SO SABIDA ALLAH❤️ALLAH KARA BASIRA DA HAZAKA*

******

Nafeesa Ta Fara Kuka, "Habibbty Ban san ya zanyi da raina ba wallahi,kin fi kowa sanin muradin raina, Amman ba yadda zanyi farincikin Abhi da Mammah ya zarce nawa koda kuwa karshen rayuwatane zan ba su farinciki,na hakura da wayar in sha Allah na hakura."

Ta rike hannun Maryam gam tana, "Zasuyi Farinciki ko Habibbty? Indai za suyi ya fi nawa mahimmanci na hakura kinji."

Tsabar Tausayin Nafeesa ya gama mamaye zuciyar Maryam bata San lokacin da itama ta bige da kukan ba, sautin kukansu kadai ke tashi adakin, Nafeesa ta fara sharewa Maryam Hawayen tana, "Habibbty ki daina kuka kinji,bana so ina saku damuwa, In sha Allah zan jure dukkan radadin da zanji Dan ganin na faranta maku ki daina kukan kinji Nima na daina, Amman fa.....

Kawai sai ta kara fashewa da kuka ta kasa karasa maganar da za ta yi.

Maryam ta ja dogon numfashi kan ta ce, " Yawwa Habibbty Kinga mu yi shiru kar Mammah ta gane ko."

Nafeesa ta kakalo wani murmushi Wanda da ka gani zaka fahimci cewa na karfin haline.

Maryam ta ce, "Yawwa wai meya farune Ranar Kinje Skul Amman ban ganki ba."

Nafeesa ta tsaya Chan kuma sai ta ce, "Ranar! Hmm Mutansir ne." Sai kuma tayi shiru.

Maryam ta zaro ido tare da fadin, "Mutansir me? Me ya miki? Fadamin Habibbty."

Abubuwan ne suka fara dawo mata cikin wani yanayi kamar mafarki,kan ta ne ya fara juyawa ta fara kallon Dakin Uku Uku.

Tallefa kanta tayi da hannunta na dama tana, "Maryam ba zan Iya ba ki bar maganar nan kai na zai fice ni ban san meya faru ba."

Tana gama fadin hakan ta kwanta awajen kamar yadda ta saba ba barci tayi ba kuma ba suma tai ba.

"Innalillahi-wa'inna-ilaihir-raji'un." Abun da Maryam ke Iya furtawa kenan yayinda hawaye ke saukowa daga idanunta.

Riketa Kawai tai tamkar wata jaririya tana kallonta gabadaya ta ma rasa me za ta yi,ba abun ta kira Mammah ba hankalinsu ya tashi.

Kuka take bilhakki da gaskiya tausayin Nafeesa ya gama mamaye zuciyar Maryam ,ji take inda tanada dama da ta dawo da radadin da Maryam ke ji cikin jikinta.

Chan kuma ta tuna da maganar Nafeesa, "Habibbty ba abun da ya gagari ubangiji aduk lokacin da wani Abu ya samemu addu'ah ce Kawai mafita koda ace da maganin abun ta addu'ah na kan gaba domin itace babban magani ga dukkan mumini."

Tana gama tunano maganar Nafeesa ta share hawayen da ke fuskarta kan ta fara jerowa Nafeesa addu'o'i daga bisani ta dauko gorar ruwa ta fara tofa addu'o'in ciki.

Bayan ta kammala Addu'o'in dago Fuskar Nafeesa tai tare da shafa mata ruwan afuska,Sanan ta bude mata Baki kadan ruwan ya samu damar shiga.

Bayan ta gama shafa mata tagumi tai kawai tare da zubawa Aminiyarta ta ido,acikin zuciyarta tana rokon Allah da ya tada Nafeesa ayanzu batare da kowa ya fahimci halin da suke ciki ba.

Kamar wasa Nafeesa ta kusa yin Rabin awa kwance ba motsi ba alamar motsi sai numfashi.

Maryam ta rasa abun yi gabadaya zuciyarta ta jagule kwatsam ta hango inda littafan Nafeesa yake,da hanzarinta ta karasa wajen aiko ta ci Karo da Al-Qur'ani kamar yadda ta aiyya na aranta.

Dauka tayi yayinda tashinta kwatsam ta bige wani littafi takarda mai dauke da zanece ta Fada kasa, batare da ta waiwaba da ta lura takardane ne kawai sai ta nufi inda Nafeesa take.

Dai,dai lokacin da wannan takarda ta fada kasa,Nafeesa ji tai tamkar allura akayo mata, a hankali take fadin, "Kin Yar min da shi,ki daga min shi,nace ki daga shi."

Tsayawa Maryam tayi cak kasancewar tana jin magana Amman ta rasa ta inda maganar ke fitowa.

Nafeesa ta kara da"Habibbty nace ki daga min shi,ki daga min shi."

Cikin dimuwa Maryam ta kalli Nafeesa tare da waigawa kallon inda Nafeesa ke nuni da hannu,wannan takardarce dai data bige batare da saninta ba.

Da sauri ta karasa tare da dagawa zanene ta gani irin Wanda Nafeesa ta sabayi akullum tana fadin cewa Nafseen dinta ne.

Mik'o mata hannu Nafeesa ke yi alamar ta bata zanen.

Karasawa gareta tayi tare da mika mata, kamar wasa Nafeesa na karban zanen ta dawo normal tashi tayi ta zauna tare da jero addu'o'i.

Bayan ta kammala ta shafa hamma ta fara" Habibbty wallahi yunwa nakeji muyi wanka na San Mammah ta kammala Abinci yanzu."

Maryam da ke cikin tsananin mamaki ta ma rasa bakin magana murmushi tayi tare da girgizawa Nafeesa kai kawai.

Ta shi tayi tayi wankanta tsaf Kai kace ba ita ba,Abu dayane kawai da ya tsaya mata rashin waya ga shi ta tsinci kanta da tsananin son ganin sakon da Nafseen zai yo mata,amman in ta tuna da maganar Maryam sai tai kokarin kawar da damuwarta.

Bayan ta fito daga wankan zama tai bakin gado dauke da zanen sahibin nata ahannu sai kallo kawai take tana ta sakin murmushi,Allah ne kadai ya San me take aiyyanawa cikin ranta.

Fitowar Maryam daga wankane ya katse mata tunani, "Habibbty abani kaya in Sa,kin San dai ba zan maida na jikina ba." Cewar Maryam.

Dagowa tai ta karewa Maryam kallo cikeda shagwaba take maganar, "Haba Habibbty wannan ai wulakancine kayanma sai na baki? Yaushe ki ka zama haka,ni fa bana so Allah na Fada miki ban so."

Murmushi Maryam ta yi, "To al-shagwabatu bara in dau abuna."

"Eh din naji." Ta kare maganar cikin murguda baki.

Maryam ko ba abun da take ban da dariya.
Chapter 8 · 0% Book details