Sashe 6
Sai Na Auri Marubuci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ta gama jibgarsu kowa ya tsere illa Mutansir da ke kwance ta dawo hayyacinta kallon jikinta ta farayi awani irin yanayi daga ita sai kananun kayan ciki, ta bi dakin ko ina da kallo sai shegen duhu da kyar ta kura ido sannan ta fara hango kayanta gefe guda,cikin sauri ta karasa wajen tare da dauka tana sawa,har yanzu bata fahimci meya faru ba bare abun da ya kawota dakin hakan ya Sa taketa kara hanzari wajen ganin ta bar dakin, kicib da mutum akasanta kallon da zatayi ta ga Mutansir,nan take hawaye ya fara zubo mata, jakarta ta kara hangowa gefe guda ta dauka ficewa daga dakin tayi cikin kuka, abun mamaki duk abun nan da ya faru glass dinta bai bar idonta ba koda na second daya.
*****Tana fita ba inda ta nufa sai bakin titi, tsare mai Nafe tayi kawai ba inda ta nufa sai gida, Mommah bata nan Sabeer ma na Skul duk ba su dawo ba, dakinta ta huce ban da kuka ba abun da takeyi azuciyarta tana fadin, "Kaddarar rayuwata ke nan Wanda ke so na baya sona Dan Allah gangar jikina yake so,ni kuma Wanda na ke so bai San inayi ba,ban San ma ko zai soni ba, da yanzu Mutansir ya Lalata min rayuwata shi ke nan." Fashewa ta karayi da kuka can kuma ta tuna da yanayin da ta tsinci kan ta, atsorace ta tashi ta zauna tana mamakin shin to ma wai "meyasami Mutansir ne? Kar dai mutuwa ya yi? Waya hanasa ketamun haddi ina sauran Abokan nasa
Shin wai me ke faruwa dani ne? Kokarin fara tuna abun da ya faru a islamiya tayi nan take kanta yafara juyawa duhu ta fara gani bata gane komai nan take wani irin gawartaccen barci ya yi awon gaba da ita.
Sai karfe biyu Mammah da Sabeer suka dawo tare ba karamin Mamaki Mammah taji ba ganin Gidan abude suna Shiga kuwa ta nufi dakin Nafeesa kamar ta sani gata nan kwance "ga duk kan alamu tana wannan barcin ne data saba aduk lokacin da aka bata mata rai." Abun da Mammah ta Fada aranta ke nan tana kallon diyartata cike da tausayi.
Kamar wasa har dare Nafeesa ba alamar motsi atattare da ita, Mammah ta zo har ta gaji da dubata lamarin ya sha bambam da Wanda tasaba yi.
Addu'ah kawai Mammah ta shafa mata tare da janyo kofar ta fita.
*****Wa she Gari da Asuba Mammah na tashi ta nufi dakin Nafeesa,tana nan dai yadda aka barta, ba Dan tana numfashi ba kai kace mutuwa tayi,Abun har ya fara damun Mammah gashi Abhi yau zai dawo hakan ne ma ya Dan sanyaya mata zuciya tafi minti biyar tana kallon diyartata kan daga karshe ta fita.
Karfe uku na yamma dai,dai Abhi ya isa.
Da Murmushinsa Ya shigo gidan,da gudu Sabeer ya rungumesa, Mammah na fadin, "Barka da dawowa Oga." Maganar take cike da fara'ah.
Abhi ya dubi ko ina ba alamar gilmawa Nafeesa.
"Niko wai Ina Ammynane?naga kowa Amman ba ita." Cewar Abhi ya na kara waige-waige.
Mammah tai murmushi, "Ammynka ba Lafiya barci take,."
Abhi ya ce, "Ayyah shiyasa gidan ba dadi Sam gaskiya sai na tada gimbiyata muje."
Mammah batace komai ba kawai suka bi bayan Abhi ita da Sabeer, suna shiga Mammah ta fara kwalla.
"Tun Jiya take barcinnan bata farka ba." Cewar Mammah cikin yanayin damuwa.
Abhi ya ce, "Subhannallah, Shine baki fadamin ba? Kuma baki kai ta asibiti ba?"
Mammah ta ce, "Na dubata Amman ba abun da asibiti za su Iya mata addu'a dai itace asibitin da maganin, tanayin hakan mun sani Amman wannan yanayinsa dabanne sai dai muta addu'an kawai."
Sam Abhi bai ji dadin lamarin ya ma kasa magana kawai ficewa ya yi, azuciyarsa yana matukar tausayin diyarnan tasa domin tunda tazo duniya take fuskantar kalubali kala daban daban iri iri.
Addu'o'i da saukan Al'qur'ani kawai suka Sa agaba.
Kwannan Nafeesa shida kwance ba motsi.
****wani bangaren kuwa na Mediya cikin Group din Marubuta anata hira da ban dariya,Mussaman Nafseen da ya Sa yan Matannan d ya Sa su agaba da tsokana, kamar wasa yana kokarin tagging din gaurayen yan matan gidan, sunantane NAFEESA ya fara fitowa awayarsa batare da Sa komai aransa ba kuwa ya danna kan sunan.
A dai dai lokacin Nafeesa..........
Urs Xayyeesherth
https://www.facebook.com/106494781436168/
_*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_
_(Nafseen)_
*NOBLE WRITERS ASSOCIATION*
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
_Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
NA
XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH
✨6STARS INDEED
_*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_
PAGE 14
BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM
*UMMU AFFAN* *MARUBUCIYAR YAFI DARE DUHU*
*INA GODIYA MATUKAR GASKE,ALLAH KARA BASIRA DA HAZAKA*❤️❤️
*SADAUKARWA GA MASOYAN ASALI BASA FUSHI DUK KWANAKIN DA ZAN DAUKA BNYI TYPING BA ZARAN SUN GANI ZASU SAMBADOMIN SHARHI INA YINKU WALLE*😘😘
Mrs Mubarak
Belar maxare(Maman tima)
Asma'u aji Ibrahim
Fatima Zahra
Fiddausi
Mrs Auwal Forever.
***
Ta farka , Hamdallah Mammaah ta fara. Cikin farinciki ta fita.
Maryam ta rike Nafeesa, "Sannu Habibbty kin tashi?"
Kan gadon ta fara bincikawa ta nemo glass dinta tare da kafawa a idonta ta gyara zaman.
Da Murmushi Nafeesa ta kalleta , "Na tashi Habibbty yaushe kikazo?"
Maryam ta ce, "Tun Safe kinata barcinki abunki."
Waige,waige ta fara, "Umm Habibbty ina wayata naji ana kirana,ki dubamin ita."
Maryam ta tashi tana, "Oh keda kike barci ina zakiji wani kiri ni kaina banji Ba bara na duba jakar nan taki."
Cikin sa'a kuwa ta Ciro wayar tare da mik'a mata, "To Madam ga shi wayar ma da akashe take, ko ta ina ki ka ji kiran mu ba mu ji ba oho."
Murmushi kawai tayi tare da kunna wayar kamar yadda taji aranta cewa Jameel na nemanta hakan ya sa ba inda ta fara lekawa sai Group din Marubuta, Message ko na farko d ya fara zuwa mata shine wan da sahibinta ya yi tagging dinta.
Tsayawa kallon message din tayi kawai tana sakar murmushi ba tare da ta Ankara ba.
Shigowar Mammah da Abhi ne ya katse ta daga duniyar ta shige acikin kankanin lokaci.
Abhi ya karaso gareta tare da dafa mata kai, "Ammienah ya jikin dai, barcin nan na lafiyane kuwa?"
Kallon agogon wayarta ta fara yi sannan ta dago ta kallesa, "Lah Abhi Yaushe ka dawo yau date 30 fa."
Cikin fara'a yake fadin, "Eh mana nazo kinata sharban barcinki nace ko takwararaki ce tazo kuke hira taki karewa kun manta damu."
"Abhina ke nan, ai da naga Kaka ko ba zan dawo ba yasin sai dai inyo maku byebye." Cewar Nafeesa tana kokarin latsa wayarta
Abhi Yayi Murmushi, "Wato dai ba za a ajiye wayar nan ba ko? To maza a ajiye ayi wanka ai sallah sannan aci abinci."
Shagabewa ta yi, "Umm Abhi nemana ake bara ince masu ina zuwa tam."
Shafa kanta yayi yana, "Yawwa Yar Albarka Ammiena,bara mu barki da Maryam ta tayaki kintsawa Muna falo in kin gama kya fito ki karbi tsarabarki."
Girgiza kai tare da murmushi kawai Nafeesa tai.
Mammah,Abhi tare da Sabeer suka fita, sai Nafeesa da Maryam.
Reply tayowa Jameel da , "Tab Yasin ni ba gauruwace ba,Dan dai bana da lafiyane Amman da yanzu nayi jajjagen miyar Kuka da kai."
Message din na Isa Yayo murmushi , "ni ko zan jira har ki samu sauki domin inga yadda ake jajjage da mutane."
Dariya Nafeesa tai wadda sai da ta fito fili ta ce, "Bara inyi wanka in dawo yau zanyi caskale da wani agidannan."
Da fadin hakan ta rufe data Amman har yanzu murmushi ya kasa gushewa daga fuskarta hakwarannan kamar mai tallan makilin.
Mamaki ya sa Maryam yin shiru tare da tafiya dogon tunani,domin tun da take bata taba ganin Nafeesa Cikin farinciki kamar na yau ba,duk da kasancewar kullum cikin murmushi take Amman bata cika washele baki da sunan tana dariya ba.
Nafeesa ce ta dakawa Maryam duka abaya, "Dilla ni kin tafi wani tunani rikeni in tashi jikina ba kwari."
Cikin Ranzana Maryam tayi tsaki, "To ai ke dince naga kinata wani kyalkyala dariya tamkar sabuwar kamu wai miye Sirrinne?"
Dafa Maryam Nafeesa tai tare da kokarin tashi, "Sirrin na da tsawo Dana baki labari."
Maryam ta riketa ta karasa tasowa tana, "Ina binki fa bashin wani sirrin ga wani ma na yau ni gaskiya na zaku inji sirrukannan Dan kwanakinnan salon ya chanja gabadaya."
A kofar toilet din ta tsaya, "In Lokacin ki San Sirrin yayi zan sanar da ke batare da kin ankaraba Amman ba yanzu ba." Ta sake mata murmushi akarshen maganar tare d shigewa cikin bandakin.
Wanka tayo tare da dauro alwala sannan ta fito tayi sallah, gabadaya yau yanayin Nafeesa ya chanja ba Magana illa murmushi da ke bayyana afuskarta.
Cikin Shigarta ta Farar doguwar Riga tare da mayafinta ta fito hannu rike Dana Habibbtynta.
"Oyoyo Ammien Dady,kullum kara girma da kyau Babyna ke yi." Cewar Abhi.
Rufe fuska da hannu Nafeesa tayi tare da shagwabewa , "Uhum Abhina ni ka daina."
Abhi ya ce, "To, to na dain a Ammien Abhi Zo in baki abinci da kaina nasan Mammah ba wani kulamin da ke take ba."karasa maganar yayi tare da bude hannunsa alamar tazo.
Sabeer ya sa kuka, "Mammah kin gama Abhi ni baya ban abinci abaki Amman zai baiwa Aunty ko?"
Mammah ta ce, "Rabu da su Sabeer dina Dadinta ma kowa ya san kai ne Auta ita kuwa gardiyace."
Dariya Sabeer yayi yana kallon Nafeesa tare da yi mata gwalo.
Nafeesa ta kalli Abhi , "Abhi ka gan su ko?"
"Sharesu ke kadai zan ba tsaraba da Maryam,Amman Sabeer kam da Mammahsa sai kallo." Fadin Abhi.
Gwalo ita ma tai wa Sabeer kamar yadda yayi mata.
Gabadaya dariya suka sa afalon.
Abhi ya fara bawa Nafeesa Abinci,kamar magani take karba cikin shagwaba harda guntun kuka, can ta tuna da tacewa Sahabinta tana zuwa.
Azabure ta mike batare da ta ce komai ba ta shige dakinta aguje.
Tsayawa kallonta kawai sukai sai gashi ta dawo hannu dauke da waya.
Abhi ya ce, "Oh wannan waya dai, to zo ki karasa abincin ko?"
Cikin shagwaba take fadin, "Um umm ni na koshi Abhi inna kara amai zan yi fa."
*****Tana fita ba inda ta nufa sai bakin titi, tsare mai Nafe tayi kawai ba inda ta nufa sai gida, Mommah bata nan Sabeer ma na Skul duk ba su dawo ba, dakinta ta huce ban da kuka ba abun da takeyi azuciyarta tana fadin, "Kaddarar rayuwata ke nan Wanda ke so na baya sona Dan Allah gangar jikina yake so,ni kuma Wanda na ke so bai San inayi ba,ban San ma ko zai soni ba, da yanzu Mutansir ya Lalata min rayuwata shi ke nan." Fashewa ta karayi da kuka can kuma ta tuna da yanayin da ta tsinci kan ta, atsorace ta tashi ta zauna tana mamakin shin to ma wai "meyasami Mutansir ne? Kar dai mutuwa ya yi? Waya hanasa ketamun haddi ina sauran Abokan nasa
Shin wai me ke faruwa dani ne? Kokarin fara tuna abun da ya faru a islamiya tayi nan take kanta yafara juyawa duhu ta fara gani bata gane komai nan take wani irin gawartaccen barci ya yi awon gaba da ita.
Sai karfe biyu Mammah da Sabeer suka dawo tare ba karamin Mamaki Mammah taji ba ganin Gidan abude suna Shiga kuwa ta nufi dakin Nafeesa kamar ta sani gata nan kwance "ga duk kan alamu tana wannan barcin ne data saba aduk lokacin da aka bata mata rai." Abun da Mammah ta Fada aranta ke nan tana kallon diyartata cike da tausayi.
Kamar wasa har dare Nafeesa ba alamar motsi atattare da ita, Mammah ta zo har ta gaji da dubata lamarin ya sha bambam da Wanda tasaba yi.
Addu'ah kawai Mammah ta shafa mata tare da janyo kofar ta fita.
*****Wa she Gari da Asuba Mammah na tashi ta nufi dakin Nafeesa,tana nan dai yadda aka barta, ba Dan tana numfashi ba kai kace mutuwa tayi,Abun har ya fara damun Mammah gashi Abhi yau zai dawo hakan ne ma ya Dan sanyaya mata zuciya tafi minti biyar tana kallon diyartata kan daga karshe ta fita.
Karfe uku na yamma dai,dai Abhi ya isa.
Da Murmushinsa Ya shigo gidan,da gudu Sabeer ya rungumesa, Mammah na fadin, "Barka da dawowa Oga." Maganar take cike da fara'ah.
Abhi ya dubi ko ina ba alamar gilmawa Nafeesa.
"Niko wai Ina Ammynane?naga kowa Amman ba ita." Cewar Abhi ya na kara waige-waige.
Mammah tai murmushi, "Ammynka ba Lafiya barci take,."
Abhi ya ce, "Ayyah shiyasa gidan ba dadi Sam gaskiya sai na tada gimbiyata muje."
Mammah batace komai ba kawai suka bi bayan Abhi ita da Sabeer, suna shiga Mammah ta fara kwalla.
"Tun Jiya take barcinnan bata farka ba." Cewar Mammah cikin yanayin damuwa.
Abhi ya ce, "Subhannallah, Shine baki fadamin ba? Kuma baki kai ta asibiti ba?"
Mammah ta ce, "Na dubata Amman ba abun da asibiti za su Iya mata addu'a dai itace asibitin da maganin, tanayin hakan mun sani Amman wannan yanayinsa dabanne sai dai muta addu'an kawai."
Sam Abhi bai ji dadin lamarin ya ma kasa magana kawai ficewa ya yi, azuciyarsa yana matukar tausayin diyarnan tasa domin tunda tazo duniya take fuskantar kalubali kala daban daban iri iri.
Addu'o'i da saukan Al'qur'ani kawai suka Sa agaba.
Kwannan Nafeesa shida kwance ba motsi.
****wani bangaren kuwa na Mediya cikin Group din Marubuta anata hira da ban dariya,Mussaman Nafseen da ya Sa yan Matannan d ya Sa su agaba da tsokana, kamar wasa yana kokarin tagging din gaurayen yan matan gidan, sunantane NAFEESA ya fara fitowa awayarsa batare da Sa komai aransa ba kuwa ya danna kan sunan.
A dai dai lokacin Nafeesa..........
Urs Xayyeesherth
https://www.facebook.com/106494781436168/
_*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_
_(Nafseen)_
*NOBLE WRITERS ASSOCIATION*
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
_Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
NA
XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH
✨6STARS INDEED
_*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_
PAGE 14
BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM
*UMMU AFFAN* *MARUBUCIYAR YAFI DARE DUHU*
*INA GODIYA MATUKAR GASKE,ALLAH KARA BASIRA DA HAZAKA*❤️❤️
*SADAUKARWA GA MASOYAN ASALI BASA FUSHI DUK KWANAKIN DA ZAN DAUKA BNYI TYPING BA ZARAN SUN GANI ZASU SAMBADOMIN SHARHI INA YINKU WALLE*😘😘
Mrs Mubarak
Belar maxare(Maman tima)
Asma'u aji Ibrahim
Fatima Zahra
Fiddausi
Mrs Auwal Forever.
***
Ta farka , Hamdallah Mammaah ta fara. Cikin farinciki ta fita.
Maryam ta rike Nafeesa, "Sannu Habibbty kin tashi?"
Kan gadon ta fara bincikawa ta nemo glass dinta tare da kafawa a idonta ta gyara zaman.
Da Murmushi Nafeesa ta kalleta , "Na tashi Habibbty yaushe kikazo?"
Maryam ta ce, "Tun Safe kinata barcinki abunki."
Waige,waige ta fara, "Umm Habibbty ina wayata naji ana kirana,ki dubamin ita."
Maryam ta tashi tana, "Oh keda kike barci ina zakiji wani kiri ni kaina banji Ba bara na duba jakar nan taki."
Cikin sa'a kuwa ta Ciro wayar tare da mik'a mata, "To Madam ga shi wayar ma da akashe take, ko ta ina ki ka ji kiran mu ba mu ji ba oho."
Murmushi kawai tayi tare da kunna wayar kamar yadda taji aranta cewa Jameel na nemanta hakan ya sa ba inda ta fara lekawa sai Group din Marubuta, Message ko na farko d ya fara zuwa mata shine wan da sahibinta ya yi tagging dinta.
Tsayawa kallon message din tayi kawai tana sakar murmushi ba tare da ta Ankara ba.
Shigowar Mammah da Abhi ne ya katse ta daga duniyar ta shige acikin kankanin lokaci.
Abhi ya karaso gareta tare da dafa mata kai, "Ammienah ya jikin dai, barcin nan na lafiyane kuwa?"
Kallon agogon wayarta ta fara yi sannan ta dago ta kallesa, "Lah Abhi Yaushe ka dawo yau date 30 fa."
Cikin fara'a yake fadin, "Eh mana nazo kinata sharban barcinki nace ko takwararaki ce tazo kuke hira taki karewa kun manta damu."
"Abhina ke nan, ai da naga Kaka ko ba zan dawo ba yasin sai dai inyo maku byebye." Cewar Nafeesa tana kokarin latsa wayarta
Abhi Yayi Murmushi, "Wato dai ba za a ajiye wayar nan ba ko? To maza a ajiye ayi wanka ai sallah sannan aci abinci."
Shagabewa ta yi, "Umm Abhi nemana ake bara ince masu ina zuwa tam."
Shafa kanta yayi yana, "Yawwa Yar Albarka Ammiena,bara mu barki da Maryam ta tayaki kintsawa Muna falo in kin gama kya fito ki karbi tsarabarki."
Girgiza kai tare da murmushi kawai Nafeesa tai.
Mammah,Abhi tare da Sabeer suka fita, sai Nafeesa da Maryam.
Reply tayowa Jameel da , "Tab Yasin ni ba gauruwace ba,Dan dai bana da lafiyane Amman da yanzu nayi jajjagen miyar Kuka da kai."
Message din na Isa Yayo murmushi , "ni ko zan jira har ki samu sauki domin inga yadda ake jajjage da mutane."
Dariya Nafeesa tai wadda sai da ta fito fili ta ce, "Bara inyi wanka in dawo yau zanyi caskale da wani agidannan."
Da fadin hakan ta rufe data Amman har yanzu murmushi ya kasa gushewa daga fuskarta hakwarannan kamar mai tallan makilin.
Mamaki ya sa Maryam yin shiru tare da tafiya dogon tunani,domin tun da take bata taba ganin Nafeesa Cikin farinciki kamar na yau ba,duk da kasancewar kullum cikin murmushi take Amman bata cika washele baki da sunan tana dariya ba.
Nafeesa ce ta dakawa Maryam duka abaya, "Dilla ni kin tafi wani tunani rikeni in tashi jikina ba kwari."
Cikin Ranzana Maryam tayi tsaki, "To ai ke dince naga kinata wani kyalkyala dariya tamkar sabuwar kamu wai miye Sirrinne?"
Dafa Maryam Nafeesa tai tare da kokarin tashi, "Sirrin na da tsawo Dana baki labari."
Maryam ta riketa ta karasa tasowa tana, "Ina binki fa bashin wani sirrin ga wani ma na yau ni gaskiya na zaku inji sirrukannan Dan kwanakinnan salon ya chanja gabadaya."
A kofar toilet din ta tsaya, "In Lokacin ki San Sirrin yayi zan sanar da ke batare da kin ankaraba Amman ba yanzu ba." Ta sake mata murmushi akarshen maganar tare d shigewa cikin bandakin.
Wanka tayo tare da dauro alwala sannan ta fito tayi sallah, gabadaya yau yanayin Nafeesa ya chanja ba Magana illa murmushi da ke bayyana afuskarta.
Cikin Shigarta ta Farar doguwar Riga tare da mayafinta ta fito hannu rike Dana Habibbtynta.
"Oyoyo Ammien Dady,kullum kara girma da kyau Babyna ke yi." Cewar Abhi.
Rufe fuska da hannu Nafeesa tayi tare da shagwabewa , "Uhum Abhina ni ka daina."
Abhi ya ce, "To, to na dain a Ammien Abhi Zo in baki abinci da kaina nasan Mammah ba wani kulamin da ke take ba."karasa maganar yayi tare da bude hannunsa alamar tazo.
Sabeer ya sa kuka, "Mammah kin gama Abhi ni baya ban abinci abaki Amman zai baiwa Aunty ko?"
Mammah ta ce, "Rabu da su Sabeer dina Dadinta ma kowa ya san kai ne Auta ita kuwa gardiyace."
Dariya Sabeer yayi yana kallon Nafeesa tare da yi mata gwalo.
Nafeesa ta kalli Abhi , "Abhi ka gan su ko?"
"Sharesu ke kadai zan ba tsaraba da Maryam,Amman Sabeer kam da Mammahsa sai kallo." Fadin Abhi.
Gwalo ita ma tai wa Sabeer kamar yadda yayi mata.
Gabadaya dariya suka sa afalon.
Abhi ya fara bawa Nafeesa Abinci,kamar magani take karba cikin shagwaba harda guntun kuka, can ta tuna da tacewa Sahabinta tana zuwa.
Azabure ta mike batare da ta ce komai ba ta shige dakinta aguje.
Tsayawa kallonta kawai sukai sai gashi ta dawo hannu dauke da waya.
Abhi ya ce, "Oh wannan waya dai, to zo ki karasa abincin ko?"
Cikin shagwaba take fadin, "Um umm ni na koshi Abhi inna kara amai zan yi fa."