← Book details Sai Na Auri Marubuci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 18

Sashe 12

Sai Na Auri Marubuci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mutasir Dane ga Alhaji Abdallah Adam da hajiya balkis Ahmad tun bayan auren su suke son haihuwa Amma Allah bai basu ba sun jima a haka tun suna rai har suka cire Alhaji ba Irin abin da beyi ba amma shiru sai kawai ya fara tunanin aure Dan Kawai yasamu haihuwa Allah da ikonsa kuwa sai ga hajiya da ciki zokaga murna wajen Alhaji tun daga wannan lokacin ya daina fita ko Ina yana tayata zama Hajiya ta samu kulawa sosai har Allah yasa ta haihu aka samu namiji Wanda yaci suna Mutasir, Alhaji ya dauki so da kauna da duk wani burin sa na duniya akan dansa akan sa ba da Wanda ba zai iya Fada ba. koda ko hajiya ce, duk da bata son Abun da Dan nata yake Amman ba yadda ta Iya domin kuwa tsaf Alhaji ya shirya rabuwa da duk Wanda yaso taba masa farincikin Dansa.

haka Muta sir ya taso a sangarce besan fada ba duk abinda yayi shine daidai momy na iya kokarinta Amma Dady yafi karfinta kuma yaro duk Wanda yake nuna abin da yake yi shine daidai to yafi son shi idan an masa fada zai ga kaj ba masoyin shi bane .

Daddy yaso kaishi kasar waje karatu Amma shi yace yafi son a bashi yayi anan a haka ya Karasa secondary harya shiga tertiary institutions inda ya hadu da Nafeesa, wannan kenan.

Maryam ko Nafe na ajiye ta motan Kabir na parking a kopan gidan su sarai ta ganshi Amma ta basar dashi tana kokarin shiga gida yazo da sauri yasha gabanta, " haba Maryam mesa kike min haka ne kina wahalar min zuciya, narasa gane me zanyi miki ki gane irin son da nake miki kodai saj ranan da kikaji ance na kamu da ciwon zuciya ko ko na mutu zaki yadda da cewa ina kaunarki,
Maryam Dan Allah ki taimaka min ki Kara bani Dama kiyi hakuri."

Maryam ko kallo bai isheta ba ta ce, " Malam matsa zan wuce inaga kaman gidan mune ko?"

Ya ce, " Hakane Maryam Amma ki saurareni Dan Allah ."
kafin tayi wani abu Kabir ne ya Saka gwiwowinsa a kasa yana , "Maryam ki tausayi min please."

ta bi ta gepan sa ta shiga gida Kabir besan sanda hawaye ya fara zubawa daga idanunsa ba kaman ba namiji ba da kyar ya kai kansa mota yaja tare da barin unguwar jiki asanyaye.

Maryam na shiga gida Ummi ta dara mata fada danko duk taji abin da Maryam tayi ma Kabir

"Maryam ba kyau wulakanta mutum fa idan ma baki sonsa bata haka zaki masa ba ki bi shi a hankali,ni zai ban koya miki wulakanta kowa ba."

Maryam ko ban da hawaye ba abin da take Dan ita bata ga Me zatayi da soyayya ba bare tasa wani aranta harta bashi kulawa bazata iya ba gaskiya daki ta shiga ta zauna tana jin haushin Kabir har cikin Ranta, ko Nafeesa dake Soyayya ma tausayinta takeji hakan ya sa take kallon cewa soyayyarma bakidaya bata lokacine.

******

Nafeesa ko bata farka ba sak da aka fara kiran sallah magrib Mammah taji dadin hakn sosai Dan yau baccin beyi nisa ba sallah tayi duk tana jin jikinta ba dadi yana mata ciwo,ko abinci bataci ba ta dauko wayarta tare kunna data...

Urs Xayyeesherth
[3/16, 2:24 PM] Xayyeesherthul-humaerth: _*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_
_(Nafseen)_

*NOBLE WRITERS ASSOCIATION*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
_Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
https://www.facebook.com/106494781436168/

NA
XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH

✨6STARS INDEED

_*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_

PAGE-22

BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM

_*TABBAS ASON RAINA LITTAFIN NAN BA ZAI ZARCE FEJI GOMA BAMA KWATA-KWATA😁AMMAN KADDARA YA SAUYA MASA AKALA YA FITA DAGA SAHUN GAJERAN LABARI,KADA KU GAJI😓 AKARA HAKURI DA RASHIN TYPING DINA KAN LOKACI,NA SAN KUNAYI AMMAN AKARA🥰INA SON KU MASOYANA,SON SO❤️*_

_*SADAUKARWA GA YAN GROUP DINA SAI NA AURI MARUBUCI FANS KUYI YADDA KUKESO DA SHI TARE DA RUWAN SHARHI*_

Tsayawa kallon Wayar tai kawai yayinda messages ke shigowa,idonta ba inda yake illa kan Sunan Ruwan Ranta *NAFSEEN* Amman har messeges sun kusa gama shigowa har yanzu ba alamar nasa, Hawayene ya fara zubowa daga fuskarta,ta San cewa tana da bukatar ganin sakonsa "Amman to miye dalilin hawayen? Tamkar wadda akace ya mutu?, Ah'ah bai mutu ba,me zai Sa ya mutu wallahi bai mutu ba." Nan take ta fara share hawayen tare da shiga tana bin hirar rakinsu.

Murmushi ne ya fara bayyana afuskarta azuciyarta take fadin, "Lallai kai na mussaman ne kamar yadda rubutun ka yake na mussaman,maza da yawa a media da zaran an fara magana da su ta private burinsu daya suga hoton mutum,Amman ko kadan kai bakada wannan akidar azuciya rayuwarka kake mai cike da annushuwa, tabbas ina sonka kuma SAI NA AURI MARUBUCI (Nafseen), ta cigaba da fadin nikam dai ayanzu duk da ban taba ganinka ba Amman na sanka,kuma ina kara ji araina cewa yadda na siffantaka haka kake babu shakka."

Tana karasa maganar ta tashi tare da nufar inda ta saba ajiyar zanen Sahibinta, Kallonsa ta tsayayi na Dan lokaci daga karshe ta shafa fuskarsa tana mai fadin, "INA SONKA, INA SO KASAN DA HAKAN." Ji tai tamkar yana kallonta hakan yasata rufe fuska da hannayenta cikin sauri, tare da nunin jin kunya,a haka har ta bar dakin sannan ta bude fuska.

Dakin Mammah ta nufa saida tai alwala sukai sallah tare kan suka fito falo, dai,dai da shigowar Abhi da Sabeer daga masallaci kenan.

Da sauri Nafeesa taje gun Abhi ta rungumesa, tana ta sakin murmushi.

Dago da ita ya yi yana. "Ammeerna Ya naganki hakane yau sai murmushi ga dukkan alamu yau an faranta miki."

Rike mi shi hannu tai tare da janshi suka zauna sannan ta ce, "Ina Sonka Abhi na."

Cike da so ya kalli Yartasa, "Tabbas nima ina sonki Ammina farincikina,Allah kara rayamun ke mu sha biki,inga ranar aurenki."

Da sauri ta rufe fuska, "Umm Umm nidai bana so."

Mammah da Sabeer ko ban da dariya ba abunda suke domin ba yau Nafeesa da Abhi suka saba irin wannan dramar ba,sun shaku matukar gaske.

Cikin farinciki,nishadi da walwala sukaci abincin darensu,sai da Abhi ya raka Nafeesa har daki kan ya nufi dakin Mammah.

Wa she gari

Da sassafe Nafeesa ta shirya domin da safe sukeda lecture, hijabinta tasa har kasa tare da glass, sai jakar makarantarta,ban da kamshi ba abun da ke tashi, ba karamun kyau Nafeesa tai ba.

Sallama taiwa Abhi domin yau zai koma aiki,sannan ta nufi skul ita da Sabeer,Mammah kuwa ta tsaya sai taga tafiyan Abhi.

Nafeesa na isa dai-dai da lokacin da driven su Maryam ya tsaya.

Da gudu Nafeesa zata karasa gun Maryam tayi kicibis da wani duzu zata fadi, da sauri Mutansir ya karaso zai tareta, dagowa tai tare da galla masa wata hamshakiyar harara ta wuce.

Binta da kallo kawai yayi azuciyarsa yana kara jin tsantsar so da kaunar ta.

Rungume Maryam tai tana, "Oyoyo Habibbty Mie,nayi kewarki aradu."

Maryam tai Murmushi , "Umm Habibbty kenan yau fa tin daga nesa nake ganin hakoranki me muka samu ne?"

Nafeesa ta kyalkyale da dariya, "har yanzu nima bansan me aka samu ba ko za asamu,Amman ina ji araina cewa abun da Nagani ne jiya,duk da kasancewar ma ya tafi ya barni batare da ya min ko magana ba."

Maryam ta ce, "Habibbty kina bani Mamaki,soyayyarki abun karantace mai zaman kanta a makaranta,na saba da ke na jima da ke Amman har yanzu Mamaki kike bani yadda kika dauki so da matsayin da ba kowa zai Iya hakan ba, tabbas kina tare da boyayyen sirri da ya kasa bayyana agaremu Allah ne kadai inyaso zai bayyana mana,bama wannan ba nasan maganar bata wuce na Sahibinki ba to me kika gani?"

Nafeesa ta ce, "Yo to wa zan gani bayan shi?.ta karasa maganar tana dariya.

Maryam ta galla mata harara, " daman nasani ai, kuma fa ina binki bashin labaran Sirri."

Nafeesa ta saki murmushi, "With Time inji bature, muje saura 2minit afara lectures."

Rike hanun junansu sukai har sai da suka shiga tare da zama awajensu da suka saba.

Karatu ake Amman gabadaya hankalin Mutansir na kan Nafeesa, shi dama ba zaman lectures din yasaba ba,Amman yau Dan ita kawai ya shigo kowa Mamaki yake, in aka lura da yadda yanayinsa ke kan Nafeesa, zaka fahiimci ita kawai yake kallo.

Gajiya ya yi abunka da ba sabanba ya tashi zai fita, Lecturern ya ce, "Kai Mutansir Ina zaka yanzu kuma? I think saura 30minit mu kammala ma." Ya karasa maganar yana kallon agogon hanunsa.

Mutansir ya ce, "Wallahi Nafeesa.......

Sai ya kasa karasa maganar domin bai ma San yadda akayi abun da ke ransa ya fito filiba.

Kallon Nafeesan yayi suna hada ido yayi saurin kawar da kai.

Daga Lecturern har sauran yan class din dariya kawai suka fara

Kunyace ta kama Mutansir ya fita kawai.
Zama yayi acikin mota ban da kallon Inda Nafeesa zata fito ba abun da yake yi,ji yake tamkar ya kara komawa domin kuwa tunda ya fito ya rasa nutsuwarsa.

Karfe 2 dai,dai Suka fito,Idon Mutansir kuwa Kur akan Nafeesa, cire tsoro yayi tare da tunkararta azuciyarsa yana mai fadin koda marinsa zatayi t dakesa da kanta ba zai fasa bayyana sirrin ransa ba.

Haka kuwa akayi Karasa wa yayi yana yi mata magana kamar bazata tsaya ba ji tai ta tsinci kanta da tsayuwar.

Mutansir ya durkusa yana fadin, "Dan Allah ki yafemun Nafeesa Sharrin shedanne ki bani dama in nuna miki hakikanin soyayyar da nke miki Dan Allah,ina sonki Nafeesa."

Kalmar son da ya furta ya sauya Nafeesa nan take wani irin yana yi ta shiga batare da ko hanunta yayi motsiba Jefar da Mutansir gefe akayi,aka kara dagasa sama kan aka sauke,ban da ihu ba abun da yake.

Nafeesa ta........

Urs Xayyeesherth
[3/16, 2:24 PM] Xayyeesherthul-humaerth: https://chat.whatsapp.com/GeuRcMbmDGuHPBZu4928K8

_*SAI NA AURI MARUBUCI📝📝📝*_
_(Nafseen)_

*NOBLE WRITERS ASSOCIATION*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
_Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu._
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
NA
XAYYEESHERTHUL-HUMAERATH

https://www.facebook.com/106494781436168/

✨6STARS INDEED

_*SAI NA AURI MARUBUCI...Kirkiraren labarine, mai dauke da nishadi na mussaman, al'ajabi tare da ban tausayi,tsantsar soyayya da kauna mai ban mamaki*_

PAGE-23
Chapter 12 · 0% Book details