Sashe 6
Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Shukrah,Shukrah “ taji ana qwala mata kira,
Muryar sameer ne,da sauri tasa hannu ta goge idonta,ta dan saisaita kanta,shigowa yayi ya tarar da ita zaune a qasa da takaddu biyu a hannunta,zama yayi shima tare da duba abinda ke hannunta,kallon yanayin ta yayi,yace “kinzo nan babu mai kula da ke kika shigo nan kina aikin kukan ko? To ki shirya mu tafi yanzu” wata qwallar ce ta zubo mata ba tare da ta sani ba,kafin tace komai sameer ya qara cewa “A ina kika samo irin wannan zanen da kike dashi kuma?” Share hawayen tayi
“A nan wata court lady tazo aka yi mata irin shi” ta fada a taqaice,cikin murmushi yace mata “kin hadu da ita kenan? Itace wacce kike nema ko? Kin samu abinda kike buqata a wajenta?” Duk ya jero mata tambayoyin,kwabe fuska tayi tace “Ni ban ganta ba,mai aikin sassaqa katakon kuma ya tafi,manager ne ya fada min na wata court lady ne” sameer yai saurin cewa “meyasa shi managern baki tambaye shi wacece ba? “
Tace “ba zai san wacece ba tunda bashi yake yi ba,wanda yakeyi din kuma lokacin da na ga abin ya riga ya tashi kuma sai wani satin zai dawo aiki,kaga kuwa ba zan samu sanin wacece ba” gyada kai sameer yayi sannan yace mata “kiyi haquri yanzu ki tashi mu tafi ko?” Ba tare da tace masa komai ba ta miqe ta hada sauran kayanta ta qulle a abinda tazo dashi ta fito suka tafi.
A bangaren jalila kuwa tana komawa gida (tana zaune ne a wajen mariqin ta,minister na tribunal) ta tarar dasu suna magana a farfajiyar gidan minister da babban danshi mai suna jameel kamar cikin rashin nutsuwa,qarasawa tayi kusa dasu tare da cewa “lafiya kuwa na ganku haka? Ko wani abin ne ya faru a gidan?”
Juyowa sukai a tare gaba dayansu suka kalleta,jameel ne ya ce mata “mun fahimci kamar dowager queen tana da wani qulli da ta shirya ranar da zaki shiga cikin masarauta” cikin rashin fahimta tace “me kake nufi da haka?”
“Ta shiryawa young prince(qaramin qanin mai martaba ne) taron murnar zagayowar haihuwar sa,kasancewar shi dan consort din da tafi tsana ne yasa bata taba bashi muhimmanci irin wannan ba,shiyasa muke tunanin akwai wani abu da take shiryawa,kuma ko menene yana da alaqa da ma’aikatar kida(bureu of music)”
Jinjina kai tayi cikin zurfin tunani ba tare da tace komai ba,jameel ya qara cewa “ ko zaki canza ranar ki qara ko kwana biyu ne saboda mu kaucewa ko ma me suke qullawa” girgiza kai tayi tace “A’ah bana son na kaucewa ko me suke qullawa,domin idan na kauce dole zasu qara qulla wani,a zaman da nayi a baya a masarautar na san yadda komai yake gudana,idan baka iya siyasa ba,ba zaka iya rayuwa ba saboda haka daidai nake da ita”
Sai a lokacin hakimi ya ce “Wannan haka yake jalilah,shiyasa na san duk inda zaki shiga ba zaki bani kunya ba”.
Oum tasneem ✍️
❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤
ROYAL CONSORT
Korean inspired novel
©️ marriam mayshanu…. ✍️
Whattpad :Oum_tasneeem
Page 6
‘Yan surutai ne suka fara tashi qus qus daga Ɓangaren hakiman arewa,mai martaba ne yayi wa chief eunuch alama da hannu nan take ya juya shima ya bawa na bayansa umarni,shi kuma ya juya ya sauka daga kan inda suke zuwa inda shugaban masu kiɗa yake,magana yayi masa a kunne ya juyo ya dawo inda yake,yayinda shi kuma shugaban masu kida ya fara yiwa mutanen sa alamun su tashi da su da kayansu su bar wajen.
Mai martaba yayi hakan ne domin hana cece-kucen da zai tashi a dalilin matsalar da aka samu,sai ya kasance kowa jikinsa babu dadi hakan yasa aka tashi taro kowa ya watse.
A wajen jalila ma hakan ce ta kasance domin kiɗa yaqi daɗi,hakan yasa ta sallame su suka tafi.
Minister of state affairs ne a durqushe gaban queen dowager,dukkansu babu mai cewa komai,shi ne yayi qarfin halin cewa
“Yanzu shikenan mun shiga uku an kawo mana annoba cikin masarauta Your Majesty” ya fada muryarsa cike da takaici,murmushi queen dowager tayi tare da kallon shi tace
“Ai jalila da ni take zancen,da qafarta zata gudu daga cikin masarautar nan don sai nasa zaman gidan nan ya gagare ta” ta qarasa cike da mugun nufi a ranta,minister da yake cikin alhini yayi mata kallon rashin fahimta,yana qoqarin bude baki yayi mata tambaya ta dakatar dashi da hannunta sannan ta dora da cewa
“Da me kuke tunani? In zauna in nade hannu na jalila tazo ta haifar wa mai martaba da,inaaa ba zai yiwu ba ace jininta zai hau kujerar mulkin garin nan,sannan abu na gaba ina umartar ka da ka rufe bakinka gum,bana buqatar maganar nan taje kunnen kowa ko da kuwa sarauniya haneefa ce”
Gyada kai yayi alamar ya ji ba tare da yace komai ba,ya miqe tsaye ya rusunar da kanshi ta gefen da queen dowager take sannan ya fice yana ta saqe saqe a ranshi.
Cikin masarauta yau ta rikice,kowane lungu da saqo duk inda ka leqa bayin gidan na munafurcin ai jalila annoba ce,domin a camfin su babbar annoba ce ace sautin kida yaqi samuwa toh lallai akwai wani mugun abu da zai faru,haka aka cigaba da yadawa har yazo kunnen jalila.,hankali tashe take qwalawa chief maid dinta kira
“Halisa,halisa,halisa” da gudu ta fado dakin domin daga jin kiran da ake mata ba na lapia bane,tazo ta durqusa a gaban uwar dakinta tare da cewa
“Gani my lady,lapia kuwa?”
Cikin muryar tashin hankali jalila tace
“Ki fada min wace magana naji tana yawo a cikin gidan nan? Me hakan yake nufi?”
Halisa da bata tsammaci jin maganar jita-jitar dake ta yawo a gidan a kunnen uwar dakin tata ta dan sunkuyar da kai tare da cewa
“Rqnki ya dade…” shiru tayi ta kasa qarasawa
“Ki fada min nace “ jalila ta fada cikin tsawa,halisa da ta firgice da jin tsawar ta fara magana cikin rawar jiki
“Ki gafarceni my lady,kasancewar a yau an rasa melody 🎶 na kida,yaqi fita yadda akeso ne yasa….” Qin qina ta fara
“Yasa meee? “ jalila ta tambayeta cikin qaguwa da jin abinda halisa zata fada mata
“ shine ake alaqanta hakan da dawowarki cikin masarauta yau da annoba (bad omen)” ta qarasa tana mai qasqantar da kanta,dafe kai jalila tayi a cikin zuciyarta tana fadin
“Wannan shine shirin queen dowager kenan,don nasan ba aikin kowa bane face nata” a fili kuma ta kalli halisa tare da cewa
“Ayi min shirin zuwa GRAND PALACE sannan ku sanar musu da zuwana” tana gama fadin haka ta juya ta zauna a mazauninta da yake wajen tare da fadawa zurfin tunanin mafitar halin da zata iya shiga a dalilin wannan abin,domin indai har masarautar da ta sani ce,ta san ministers din arewa sai sunyi wa mai martaba petition (qara) game da ya qara duba hukuncin sa na shigo da ita masarautar kuma tasan matuqar dai suka fishi hujja to sai abinda suka ce domin zasu bada hujjar suna kare qasar su ne daga annoba.
Tana cikin wannan tunanin ne Taji shigowar halisa,rusunar da kanta tayi tare da cewa
“Shirye shirye sun kammala my lady,babbar fada suna shirin zuwanki”
Alkyabbar ta ta dauka wacce take plain ce babu adon komai a jiki ta yafa sannan suka fito,maids dinta da suke tsaye a bakin qofa ne suka bi bayansu har grand palace,a bakin grand palace suka tsaya yayinda aka yi mata iso zuwa ga mai martaba,qofa aka bude mata ta shige su kuma maids dinta suke jeru a gefen qofar da ta shiga suna jiran fitowar ta.
A can bureu of music kuwa sun duqufa wajen gani dalilin da yasa yau melody din kidan su yaqi fita,tare da damuwa a cikin ransu,domin su masu yadda ne da camfi qwarai da gaske hakan yasa suke ganin kamar wani mugun abu zai faru a cikin garin ne shiyasa aka samu matsala da melody din,shukra ce ta kalli manager tare da cewa
“Amma ranka ya dade,baka ganin ko matsala aka samu da wani abin daga cikin kayan kidan?” Kallon banza ya watsa mata tare da cewa “har yaushe wannan yarinyar ta fara aikin zama mai gano matsalolin kayan kida?”
Sameer ne ya qunshe bakin shi da dariya,yayin da ya kalli manager yace
“Yallabai ka qyale shukra da shirmen ta kawai” dan qasa yayi da murya kuma ya qara matsawa kusa da kunnen manager tare da cewa
“Ana ta cewa hakan yana da alaqa da dawowar lady jalila ne,haqiqa ita din annoba ce ga masarautar nan”
Manager da ya dauki maganar da muhimmanci amma yana tsoron wani ya jisu suna yi ya toshe bakin sameer tare da rada masa
“Idan ka bari wani ya jika kasani a bakin ranka ne”
Shiru sameer yayi tare dan yin murmushi,ya kalli shukra yace mata
“Tashi muje waje”
A hankali suke takowa har bakin qofar office din manager,shukra ce tace
“Nifa yallabai ina ji a raina kamar akwai wani abu da yake faruwa,don ni gaskiya ban yadda da camfin nan ba”
Sameer ne ya kalle ta tare da cewa
“Ke dai rigimar ki yawa ce da ita shukra,abinda kika ji ana fada gaskiya ne,lady jalila ce annobar da tasa hakan ya faru,don hakan alama ce qarara da take nuna faruwar wata annoba tun zamanin iyaye da kakanni”
Gyada kai shukra tayi tare da cewa
“Zan gwada dubawa na gani,ko zan samu wani abin da zan kafa hujja dashi,kuma kafin kace min komai ni bana buqatar taimakon kowa,amma zan qoqarta don har naji lady jalila tana bani tausayi duk da ban santa ba”
Kafin sameer yace wani abu shukra tayi gaba ta barshi a wajen,kallo ya bita dashi yace
“Shukra kenan,Ina fatan kada ki janyo mana abinda ba zamu iya ba”
Shukra kai tsaye dakin baccinta ta nufa tare da canja kayan jikinta,domin idan ta fita da kayan da take sawa duk wanda ya ganta zai gane cewar ita baiwar masarauta ce,hakan yasa ta canja domin tana son ta fita wajen masarautar ta dan sha iska.
Muryar sameer ne,da sauri tasa hannu ta goge idonta,ta dan saisaita kanta,shigowa yayi ya tarar da ita zaune a qasa da takaddu biyu a hannunta,zama yayi shima tare da duba abinda ke hannunta,kallon yanayin ta yayi,yace “kinzo nan babu mai kula da ke kika shigo nan kina aikin kukan ko? To ki shirya mu tafi yanzu” wata qwallar ce ta zubo mata ba tare da ta sani ba,kafin tace komai sameer ya qara cewa “A ina kika samo irin wannan zanen da kike dashi kuma?” Share hawayen tayi
“A nan wata court lady tazo aka yi mata irin shi” ta fada a taqaice,cikin murmushi yace mata “kin hadu da ita kenan? Itace wacce kike nema ko? Kin samu abinda kike buqata a wajenta?” Duk ya jero mata tambayoyin,kwabe fuska tayi tace “Ni ban ganta ba,mai aikin sassaqa katakon kuma ya tafi,manager ne ya fada min na wata court lady ne” sameer yai saurin cewa “meyasa shi managern baki tambaye shi wacece ba? “
Tace “ba zai san wacece ba tunda bashi yake yi ba,wanda yakeyi din kuma lokacin da na ga abin ya riga ya tashi kuma sai wani satin zai dawo aiki,kaga kuwa ba zan samu sanin wacece ba” gyada kai sameer yayi sannan yace mata “kiyi haquri yanzu ki tashi mu tafi ko?” Ba tare da tace masa komai ba ta miqe ta hada sauran kayanta ta qulle a abinda tazo dashi ta fito suka tafi.
A bangaren jalila kuwa tana komawa gida (tana zaune ne a wajen mariqin ta,minister na tribunal) ta tarar dasu suna magana a farfajiyar gidan minister da babban danshi mai suna jameel kamar cikin rashin nutsuwa,qarasawa tayi kusa dasu tare da cewa “lafiya kuwa na ganku haka? Ko wani abin ne ya faru a gidan?”
Juyowa sukai a tare gaba dayansu suka kalleta,jameel ne ya ce mata “mun fahimci kamar dowager queen tana da wani qulli da ta shirya ranar da zaki shiga cikin masarauta” cikin rashin fahimta tace “me kake nufi da haka?”
“Ta shiryawa young prince(qaramin qanin mai martaba ne) taron murnar zagayowar haihuwar sa,kasancewar shi dan consort din da tafi tsana ne yasa bata taba bashi muhimmanci irin wannan ba,shiyasa muke tunanin akwai wani abu da take shiryawa,kuma ko menene yana da alaqa da ma’aikatar kida(bureu of music)”
Jinjina kai tayi cikin zurfin tunani ba tare da tace komai ba,jameel ya qara cewa “ ko zaki canza ranar ki qara ko kwana biyu ne saboda mu kaucewa ko ma me suke qullawa” girgiza kai tayi tace “A’ah bana son na kaucewa ko me suke qullawa,domin idan na kauce dole zasu qara qulla wani,a zaman da nayi a baya a masarautar na san yadda komai yake gudana,idan baka iya siyasa ba,ba zaka iya rayuwa ba saboda haka daidai nake da ita”
Sai a lokacin hakimi ya ce “Wannan haka yake jalilah,shiyasa na san duk inda zaki shiga ba zaki bani kunya ba”.
Oum tasneem ✍️
❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤
ROYAL CONSORT
Korean inspired novel
©️ marriam mayshanu…. ✍️
Whattpad :Oum_tasneeem
Page 6
‘Yan surutai ne suka fara tashi qus qus daga Ɓangaren hakiman arewa,mai martaba ne yayi wa chief eunuch alama da hannu nan take ya juya shima ya bawa na bayansa umarni,shi kuma ya juya ya sauka daga kan inda suke zuwa inda shugaban masu kiɗa yake,magana yayi masa a kunne ya juyo ya dawo inda yake,yayinda shi kuma shugaban masu kida ya fara yiwa mutanen sa alamun su tashi da su da kayansu su bar wajen.
Mai martaba yayi hakan ne domin hana cece-kucen da zai tashi a dalilin matsalar da aka samu,sai ya kasance kowa jikinsa babu dadi hakan yasa aka tashi taro kowa ya watse.
A wajen jalila ma hakan ce ta kasance domin kiɗa yaqi daɗi,hakan yasa ta sallame su suka tafi.
Minister of state affairs ne a durqushe gaban queen dowager,dukkansu babu mai cewa komai,shi ne yayi qarfin halin cewa
“Yanzu shikenan mun shiga uku an kawo mana annoba cikin masarauta Your Majesty” ya fada muryarsa cike da takaici,murmushi queen dowager tayi tare da kallon shi tace
“Ai jalila da ni take zancen,da qafarta zata gudu daga cikin masarautar nan don sai nasa zaman gidan nan ya gagare ta” ta qarasa cike da mugun nufi a ranta,minister da yake cikin alhini yayi mata kallon rashin fahimta,yana qoqarin bude baki yayi mata tambaya ta dakatar dashi da hannunta sannan ta dora da cewa
“Da me kuke tunani? In zauna in nade hannu na jalila tazo ta haifar wa mai martaba da,inaaa ba zai yiwu ba ace jininta zai hau kujerar mulkin garin nan,sannan abu na gaba ina umartar ka da ka rufe bakinka gum,bana buqatar maganar nan taje kunnen kowa ko da kuwa sarauniya haneefa ce”
Gyada kai yayi alamar ya ji ba tare da yace komai ba,ya miqe tsaye ya rusunar da kanshi ta gefen da queen dowager take sannan ya fice yana ta saqe saqe a ranshi.
Cikin masarauta yau ta rikice,kowane lungu da saqo duk inda ka leqa bayin gidan na munafurcin ai jalila annoba ce,domin a camfin su babbar annoba ce ace sautin kida yaqi samuwa toh lallai akwai wani mugun abu da zai faru,haka aka cigaba da yadawa har yazo kunnen jalila.,hankali tashe take qwalawa chief maid dinta kira
“Halisa,halisa,halisa” da gudu ta fado dakin domin daga jin kiran da ake mata ba na lapia bane,tazo ta durqusa a gaban uwar dakinta tare da cewa
“Gani my lady,lapia kuwa?”
Cikin muryar tashin hankali jalila tace
“Ki fada min wace magana naji tana yawo a cikin gidan nan? Me hakan yake nufi?”
Halisa da bata tsammaci jin maganar jita-jitar dake ta yawo a gidan a kunnen uwar dakin tata ta dan sunkuyar da kai tare da cewa
“Rqnki ya dade…” shiru tayi ta kasa qarasawa
“Ki fada min nace “ jalila ta fada cikin tsawa,halisa da ta firgice da jin tsawar ta fara magana cikin rawar jiki
“Ki gafarceni my lady,kasancewar a yau an rasa melody 🎶 na kida,yaqi fita yadda akeso ne yasa….” Qin qina ta fara
“Yasa meee? “ jalila ta tambayeta cikin qaguwa da jin abinda halisa zata fada mata
“ shine ake alaqanta hakan da dawowarki cikin masarauta yau da annoba (bad omen)” ta qarasa tana mai qasqantar da kanta,dafe kai jalila tayi a cikin zuciyarta tana fadin
“Wannan shine shirin queen dowager kenan,don nasan ba aikin kowa bane face nata” a fili kuma ta kalli halisa tare da cewa
“Ayi min shirin zuwa GRAND PALACE sannan ku sanar musu da zuwana” tana gama fadin haka ta juya ta zauna a mazauninta da yake wajen tare da fadawa zurfin tunanin mafitar halin da zata iya shiga a dalilin wannan abin,domin indai har masarautar da ta sani ce,ta san ministers din arewa sai sunyi wa mai martaba petition (qara) game da ya qara duba hukuncin sa na shigo da ita masarautar kuma tasan matuqar dai suka fishi hujja to sai abinda suka ce domin zasu bada hujjar suna kare qasar su ne daga annoba.
Tana cikin wannan tunanin ne Taji shigowar halisa,rusunar da kanta tayi tare da cewa
“Shirye shirye sun kammala my lady,babbar fada suna shirin zuwanki”
Alkyabbar ta ta dauka wacce take plain ce babu adon komai a jiki ta yafa sannan suka fito,maids dinta da suke tsaye a bakin qofa ne suka bi bayansu har grand palace,a bakin grand palace suka tsaya yayinda aka yi mata iso zuwa ga mai martaba,qofa aka bude mata ta shige su kuma maids dinta suke jeru a gefen qofar da ta shiga suna jiran fitowar ta.
A can bureu of music kuwa sun duqufa wajen gani dalilin da yasa yau melody din kidan su yaqi fita,tare da damuwa a cikin ransu,domin su masu yadda ne da camfi qwarai da gaske hakan yasa suke ganin kamar wani mugun abu zai faru a cikin garin ne shiyasa aka samu matsala da melody din,shukra ce ta kalli manager tare da cewa
“Amma ranka ya dade,baka ganin ko matsala aka samu da wani abin daga cikin kayan kidan?” Kallon banza ya watsa mata tare da cewa “har yaushe wannan yarinyar ta fara aikin zama mai gano matsalolin kayan kida?”
Sameer ne ya qunshe bakin shi da dariya,yayin da ya kalli manager yace
“Yallabai ka qyale shukra da shirmen ta kawai” dan qasa yayi da murya kuma ya qara matsawa kusa da kunnen manager tare da cewa
“Ana ta cewa hakan yana da alaqa da dawowar lady jalila ne,haqiqa ita din annoba ce ga masarautar nan”
Manager da ya dauki maganar da muhimmanci amma yana tsoron wani ya jisu suna yi ya toshe bakin sameer tare da rada masa
“Idan ka bari wani ya jika kasani a bakin ranka ne”
Shiru sameer yayi tare dan yin murmushi,ya kalli shukra yace mata
“Tashi muje waje”
A hankali suke takowa har bakin qofar office din manager,shukra ce tace
“Nifa yallabai ina ji a raina kamar akwai wani abu da yake faruwa,don ni gaskiya ban yadda da camfin nan ba”
Sameer ne ya kalle ta tare da cewa
“Ke dai rigimar ki yawa ce da ita shukra,abinda kika ji ana fada gaskiya ne,lady jalila ce annobar da tasa hakan ya faru,don hakan alama ce qarara da take nuna faruwar wata annoba tun zamanin iyaye da kakanni”
Gyada kai shukra tayi tare da cewa
“Zan gwada dubawa na gani,ko zan samu wani abin da zan kafa hujja dashi,kuma kafin kace min komai ni bana buqatar taimakon kowa,amma zan qoqarta don har naji lady jalila tana bani tausayi duk da ban santa ba”
Kafin sameer yace wani abu shukra tayi gaba ta barshi a wajen,kallo ya bita dashi yace
“Shukra kenan,Ina fatan kada ki janyo mana abinda ba zamu iya ba”
Shukra kai tsaye dakin baccinta ta nufa tare da canja kayan jikinta,domin idan ta fita da kayan da take sawa duk wanda ya ganta zai gane cewar ita baiwar masarauta ce,hakan yasa ta canja domin tana son ta fita wajen masarautar ta dan sha iska.