Sashe 33
Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A grand palace cikin mamaki mai martaba yake kallon wakilin china
“Kace ya kashe kanshi?”
“Qwarai kuwa,ya kashe kanshi a cikin qasar ka” wakilin china ya fada,tare da miqawa mai martaba wata takadda
“Ya bar wannan takaddar ne da ya rubuta cewa ya kashe kansa ne domin duniya ta yadda bashi da laifi,sharri kawai ake nemanshi dashi” karbar takaddar mai martaba yayi nan take yanayin fuskar shi ta canja zuwa bacin rai,yana gama karanta takaddar ya nannadeta ya ajiye akan tebur din dake tsakiyar su,wakilin china yace
“Nayi shiru lokacin da kuka tura mana ladies investigators ban ce komai ba,na qara yin shiru lokacin da yarinya daya a cikinsu ta shigo mana a boye,amma wannan karon da aka dorawa dan rakiya ta sharri tabbas zan dauki mataki tunda har hakan ya kai ga rasa ransa domin ya kare kansa ya kuma tabbatar bashi da laifi” mai martaba cikin bacin rai yace
“Aka yi masa sharri kuma? Bayan hujja da muka samu akan shi?”
“Hujja? Kana nufin wannan saqon takaddar sirrin da palace maid dinku ta samo? Ta yaya zan yadda dama can ba ku kuka tsara hakan ba? Tunda dama kuna zargin Kim Young Dal?” Wakili ya fada,
“Wakili!!! Kana daukar abin nan da nisa,ta yaya zamu shirya haka kawai domin muna son mu kama shi?” Mai martaba ya fada masa cikin bacin rai,amsa wakili ya bashi da
“Tabbas hakan zai iya zama shirin ku ne,kuma matuqar labari ya kai wa sarkin china,to matsalar sai tafi haka girma,domin Kim dan asalin qasar nan ne,amma yanzu ya zama dan qasar china,kuma yazo ya kashe kanshi a qasarku” mai martaba ne ya dan sassauta murya
“Toh yanzu me kuke son ayi muku?” Ajiyar zuciya wakili yayi tare da cewa
“Ina son ka bani yarinyar nan your majesty,ina da damar da zan bincika na gani ko shiri ne kuka yi domin ganin kun kama Kim da laifi,zan tafi da lady investigator dinnan china domin na yi mata tambayoyi da azaba har sai ta fadi gaskiya your majesty” Ran mai martaba idan yayi dubu to duk sun baci,fuskar nan babu annuri ko kadan ya kalli wakili cikin daga murya yace
“Kalle ni nan Wakili! Me kake fada haka? Na dauki yarinya na baku ku tafi da ita qasar ku? Bayan bata da laifin komai?” Ganin yadda ran mai martaba ya baci Wakili ya miqe tare da cewa
“Ka dai qara tunani,domin idan ba hakan akayi ba,tabbas qasar JOSHUN zata samu babbar matsala da sarkin china.
Washegari a office of investigation,suna tsatstsaye kowa da abokin hirar sa shukra ta shigo,magana ta fara yi musu tana gaishe su kowa yayi mata banza,cikin mamakin hakan ta qaraso inda Aliya,sameera da ruqayya suke tsaye tace
“Sannunku,kun tashi lapia?” Juyar da kansu sukayi ba tare da sunce mata,gaba tayi ta wuce su tare da tsayawa tana tunanin dalilin hakan,sai ga Afrah nan,da sauri ta qaraso inda shukra take suka gaisa sannan tace wa shukra
“Kiyi sauri kije office ki samu Lady nadeeyah”
Shukra da ta dan tsorata tace
“Lady nadeeyah kuma? Lafia?” Murmushi Afrah tayi wanda daga ganinshi na yaqe ne,sannan tace
“Idan kinje wajenta zakiji ko menene” da sauri shukra ta wuce,Afrah ta bita da kallon tausayi.
Da shigarta office din,nadeeya da basma ne a zaune a kan kujera,bayani sukayi mata akan buqatar Wakilin sarkin china na tafiya da ita qasar su,cikin razana tace
“Suna son su tafi dani china! Na shiga uku!” Babu wanda ya qara ce mata komai domin suma su biyun suna cikin tashin hankali sosai,don haka kawai yarinyar ta kwanta musu a rai musamman nadeeyah,tana qaunar shukra sosai har cikin ranta.
A majalisar sarki an zauna zama na musamman akan wannan matsalar,dukkan hakimai suna zaune a qasa a jere kamar yadda suka saba zama,tribunal minister ne yake cewa
“Mai martaba,dole ne mu nemi hanyar da zamu gusar da bacin ran su,domin dorewar zaman lapia tsakanin qasashen namu guda biyu” mai martaba da har yanzu ran shi a bace yake yace
“Kana nufin mu miqa musu yarinyar su tafi da ita kenan?”
Minister of state affairs yace
“Your majesty,daya daga cikin ‘yan rakiyar Wakili ya kashe kansa fah!kuma hakan zai bamu matsala sosai da sarkin china,ka taimaka ka miqa musu ita kawai sannan…..”
“Bana buqatar ji!!!” Mai martaba ya fada cikin gigitacciyar tsawa
“Ya isheku haka! Yarinyar nan da ake magana a kanta ba ita tayi laifi ba,aikin ta kawai takeyi,ta yaya zaku bude baki kuce na miqata zuwa wajensu?” Shiru dukkansu sukayi,tribunal minister yace
“Amma mai martaba idan ba’a yi hakan ba,ta yaya za’a yi maganin wannan matsalar? Wakili ba zai bar garin nan ba tare da ita ba,idan kuma ya zauna mana,zasu turo sojojin su daga can qasarsu domin suyi gadin shi da mutanensa,hakan kuma zai iya zama yaqi tsakanin mu dasu,ta yaya zamu iya hana hakan faruwa? ka qara duba lamarin nan your majesty” dukka wajen suka hada baki tare da saukar da kansu qasa a yadda suke a zaune,suka ce
“Ka qara duba lamarin nan your majesty! Ka qara duba lamarin nan your majesty!! Ka qara duba lamarin nan your majesty!!!” Huci kawai mai martaba yakeyi yana kallonsu daya bayan daya.
A quaters din queen dowager,chief maid dinta ce tazo tana bata labarin dalla-dallah tun daga farkon farawar lamarin har zuwa yanzu da mai martaba yace ba zai bada shukra a tafi da ita ba,tabe baki tayi
“Yanzu ya gwammace ya jawo wa qasar nan rikici da tashin hankali akan wata palace maid wacce ba kowan kowa ba?” Queen haneefah da take gefe tace
“His majesty ya yanke hukuncin da ya dace Mamaa,wannan palace maid din itama ai ‘yar qasar sa ce,kuma haqqine a kansa ya kareta “
Harara queen dowager ta miqa mata,amma ba tare da kallon idonta fuska da fuska ba,tace
“Ta yaya zaki fadi haka a cikin wannan halin da ake ciki? Yarinya ita kadai ta addabi dukkan garin nan,kowa hankalinsa a tashe?”
Basma ce ta shigo office da gudu,inda nadeeya da Afrah suke tsaye suna jimamin abinda yake shirin faruwa,kallonta sukayi domin yanayin da ta shigo kawai ya nuna musu ba lapia ba,kafin suyi magana tace
“Hakimai gaba daya sunayiwa mai martaba zanga-zanga akan ya miqa shukra” Afrah da sauri cikin bacin rai tace
“Ta yaya zasuyi zanga-zanga don a miqa wacce take yiwa qasa aiki?” Basma ce ta bata amsa
“Ai su hakiman basa bawa palace maid wata daraja,su kawai damuwar su bacin ran sarkin china” nadeeyah da jikinta gaba daya yayi sanyi tace
“Ta yaya zasuyi haka? Ina ganin ana son a hukunta shukra ne saboda qwazo da qoqarin ta,zan je na samu IG saboda naji ainihin abinda yake faruwa” basma tace
“Zan biki muje”Afrah ma tace
“Muje”
Hajiya jameela ce ta shirya tsaf domin zuwa cikin masarauta don ganin lady jalila,ita da maid dinta suka fito daga daki a tsakar gida suka tarar da jaleel,kallon yanayin shigar da tayi ne yasa yace
“Maama,ina zuwa haka?” Ba tare da ta tsaya ba ta bashi amsa
“Zanje wajen jalila,na san wannan halin da ake ciki na yaqi ko yau ko gobe kuma gashi akan yarinyar da ta shigo da ita Office of investigation,nasan hankalinta ba a kwance yake ba,tana buqatar wani a kusa da ita” tsayar da ita jaleel yayi da murmushi a fuskar shi tare da cewa
“Haba maama,in dai don wannan ne ai ba sai kinje ba,duk wannan abin da kike gani nine nan na shirya shi” da mamaki hajiya jameela take kallonshi
“Kai !!! Me ka aikata haka?” Murmushi ne har yanzu akan fuskar shi
“Tun ina yaro nake sawa kowa yake min kallon shashasha,sai na basu mamaki,amma fa lady jalila bata sani ba don ban sanar da ita ba,kuma ina yin wannan ne saboda ita don bata san hatsarin wanann yarinyar shukra a kusa da ita ba” tsabar mamaki kasa cewa komai tayi,kawai ta tsaya tana kallonshi.
A gida sameer yake bawa Abdullahi labarin abinda yake faruwa,domin duk abinda akeyi bai sani ba,da sauri ya tashi domin neman shukra,a bakin qofar quaters din baqin china ya ganta cikin kayanta irin dai wanda talakawan gari suke sawa,yadda aka jera sojojin china,ga kuma sojojin JOSHUN suma a jere suna fuskantar su kamar dai masu shirin yaqi,ta bayanta ya tsaya tare da cewa
“Shukra” juyowa tayi cikin tsoro,ganin Abdullahi ne yasa ta sauke ajiyar zuciya,hannun ta ya jawo har zuwa gidan sameer,suka shigo daki ya fara tattara kayan duk da ya san nashi ne,ganin haka shukra ta jefa masa tamabaya
“Me kenan kake yi?” Ba tare da ya kalleta ba,kuma bai daina abinda yake yi ba ya bata amsa
“Ya kamata ki bar qasar nan,saboda a halin yanzu kina cikin hatsari” Da sauri cikin daga murya tace
“Orabeuni !” (Yaya!)
Juyowa yayi a wannan lokacin ya kalleta
“Naji abinda yake faruwa shukra,Wakilin china ba zai haqura ba har sai ya sameki”
“Amma ni palace maid ce,kuma palace maid basa guduwa,hakan babban laifi ne” shukra ta fada masa
“Kina nufin ki zauna,a basu ke su tafi dake china ko? Idan suka tafi ke kashe ki zasu yi” ya fada mata qwalla tana cika a idonsa,jikinta ne yayi sanyi ganin qwallar da take idonshi,ganin bata ce komai ba ya cigaba da magana
“Kawai kiyi yadda nace,yau da daddare zamu bar garin nan,saboda haka ki shirya kawai” yana gama fada mata haka ya cigaba da hada kayansa,tana masa magana amma bai qara kallon inda take ba balle ya amsa mata tunda ya gama magana.
“Kace ya kashe kanshi?”
“Qwarai kuwa,ya kashe kanshi a cikin qasar ka” wakilin china ya fada,tare da miqawa mai martaba wata takadda
“Ya bar wannan takaddar ne da ya rubuta cewa ya kashe kansa ne domin duniya ta yadda bashi da laifi,sharri kawai ake nemanshi dashi” karbar takaddar mai martaba yayi nan take yanayin fuskar shi ta canja zuwa bacin rai,yana gama karanta takaddar ya nannadeta ya ajiye akan tebur din dake tsakiyar su,wakilin china yace
“Nayi shiru lokacin da kuka tura mana ladies investigators ban ce komai ba,na qara yin shiru lokacin da yarinya daya a cikinsu ta shigo mana a boye,amma wannan karon da aka dorawa dan rakiya ta sharri tabbas zan dauki mataki tunda har hakan ya kai ga rasa ransa domin ya kare kansa ya kuma tabbatar bashi da laifi” mai martaba cikin bacin rai yace
“Aka yi masa sharri kuma? Bayan hujja da muka samu akan shi?”
“Hujja? Kana nufin wannan saqon takaddar sirrin da palace maid dinku ta samo? Ta yaya zan yadda dama can ba ku kuka tsara hakan ba? Tunda dama kuna zargin Kim Young Dal?” Wakili ya fada,
“Wakili!!! Kana daukar abin nan da nisa,ta yaya zamu shirya haka kawai domin muna son mu kama shi?” Mai martaba ya fada masa cikin bacin rai,amsa wakili ya bashi da
“Tabbas hakan zai iya zama shirin ku ne,kuma matuqar labari ya kai wa sarkin china,to matsalar sai tafi haka girma,domin Kim dan asalin qasar nan ne,amma yanzu ya zama dan qasar china,kuma yazo ya kashe kanshi a qasarku” mai martaba ne ya dan sassauta murya
“Toh yanzu me kuke son ayi muku?” Ajiyar zuciya wakili yayi tare da cewa
“Ina son ka bani yarinyar nan your majesty,ina da damar da zan bincika na gani ko shiri ne kuka yi domin ganin kun kama Kim da laifi,zan tafi da lady investigator dinnan china domin na yi mata tambayoyi da azaba har sai ta fadi gaskiya your majesty” Ran mai martaba idan yayi dubu to duk sun baci,fuskar nan babu annuri ko kadan ya kalli wakili cikin daga murya yace
“Kalle ni nan Wakili! Me kake fada haka? Na dauki yarinya na baku ku tafi da ita qasar ku? Bayan bata da laifin komai?” Ganin yadda ran mai martaba ya baci Wakili ya miqe tare da cewa
“Ka dai qara tunani,domin idan ba hakan akayi ba,tabbas qasar JOSHUN zata samu babbar matsala da sarkin china.
Washegari a office of investigation,suna tsatstsaye kowa da abokin hirar sa shukra ta shigo,magana ta fara yi musu tana gaishe su kowa yayi mata banza,cikin mamakin hakan ta qaraso inda Aliya,sameera da ruqayya suke tsaye tace
“Sannunku,kun tashi lapia?” Juyar da kansu sukayi ba tare da sunce mata,gaba tayi ta wuce su tare da tsayawa tana tunanin dalilin hakan,sai ga Afrah nan,da sauri ta qaraso inda shukra take suka gaisa sannan tace wa shukra
“Kiyi sauri kije office ki samu Lady nadeeyah”
Shukra da ta dan tsorata tace
“Lady nadeeyah kuma? Lafia?” Murmushi Afrah tayi wanda daga ganinshi na yaqe ne,sannan tace
“Idan kinje wajenta zakiji ko menene” da sauri shukra ta wuce,Afrah ta bita da kallon tausayi.
Da shigarta office din,nadeeya da basma ne a zaune a kan kujera,bayani sukayi mata akan buqatar Wakilin sarkin china na tafiya da ita qasar su,cikin razana tace
“Suna son su tafi dani china! Na shiga uku!” Babu wanda ya qara ce mata komai domin suma su biyun suna cikin tashin hankali sosai,don haka kawai yarinyar ta kwanta musu a rai musamman nadeeyah,tana qaunar shukra sosai har cikin ranta.
A majalisar sarki an zauna zama na musamman akan wannan matsalar,dukkan hakimai suna zaune a qasa a jere kamar yadda suka saba zama,tribunal minister ne yake cewa
“Mai martaba,dole ne mu nemi hanyar da zamu gusar da bacin ran su,domin dorewar zaman lapia tsakanin qasashen namu guda biyu” mai martaba da har yanzu ran shi a bace yake yace
“Kana nufin mu miqa musu yarinyar su tafi da ita kenan?”
Minister of state affairs yace
“Your majesty,daya daga cikin ‘yan rakiyar Wakili ya kashe kansa fah!kuma hakan zai bamu matsala sosai da sarkin china,ka taimaka ka miqa musu ita kawai sannan…..”
“Bana buqatar ji!!!” Mai martaba ya fada cikin gigitacciyar tsawa
“Ya isheku haka! Yarinyar nan da ake magana a kanta ba ita tayi laifi ba,aikin ta kawai takeyi,ta yaya zaku bude baki kuce na miqata zuwa wajensu?” Shiru dukkansu sukayi,tribunal minister yace
“Amma mai martaba idan ba’a yi hakan ba,ta yaya za’a yi maganin wannan matsalar? Wakili ba zai bar garin nan ba tare da ita ba,idan kuma ya zauna mana,zasu turo sojojin su daga can qasarsu domin suyi gadin shi da mutanensa,hakan kuma zai iya zama yaqi tsakanin mu dasu,ta yaya zamu iya hana hakan faruwa? ka qara duba lamarin nan your majesty” dukka wajen suka hada baki tare da saukar da kansu qasa a yadda suke a zaune,suka ce
“Ka qara duba lamarin nan your majesty! Ka qara duba lamarin nan your majesty!! Ka qara duba lamarin nan your majesty!!!” Huci kawai mai martaba yakeyi yana kallonsu daya bayan daya.
A quaters din queen dowager,chief maid dinta ce tazo tana bata labarin dalla-dallah tun daga farkon farawar lamarin har zuwa yanzu da mai martaba yace ba zai bada shukra a tafi da ita ba,tabe baki tayi
“Yanzu ya gwammace ya jawo wa qasar nan rikici da tashin hankali akan wata palace maid wacce ba kowan kowa ba?” Queen haneefah da take gefe tace
“His majesty ya yanke hukuncin da ya dace Mamaa,wannan palace maid din itama ai ‘yar qasar sa ce,kuma haqqine a kansa ya kareta “
Harara queen dowager ta miqa mata,amma ba tare da kallon idonta fuska da fuska ba,tace
“Ta yaya zaki fadi haka a cikin wannan halin da ake ciki? Yarinya ita kadai ta addabi dukkan garin nan,kowa hankalinsa a tashe?”
Basma ce ta shigo office da gudu,inda nadeeya da Afrah suke tsaye suna jimamin abinda yake shirin faruwa,kallonta sukayi domin yanayin da ta shigo kawai ya nuna musu ba lapia ba,kafin suyi magana tace
“Hakimai gaba daya sunayiwa mai martaba zanga-zanga akan ya miqa shukra” Afrah da sauri cikin bacin rai tace
“Ta yaya zasuyi zanga-zanga don a miqa wacce take yiwa qasa aiki?” Basma ce ta bata amsa
“Ai su hakiman basa bawa palace maid wata daraja,su kawai damuwar su bacin ran sarkin china” nadeeyah da jikinta gaba daya yayi sanyi tace
“Ta yaya zasuyi haka? Ina ganin ana son a hukunta shukra ne saboda qwazo da qoqarin ta,zan je na samu IG saboda naji ainihin abinda yake faruwa” basma tace
“Zan biki muje”Afrah ma tace
“Muje”
Hajiya jameela ce ta shirya tsaf domin zuwa cikin masarauta don ganin lady jalila,ita da maid dinta suka fito daga daki a tsakar gida suka tarar da jaleel,kallon yanayin shigar da tayi ne yasa yace
“Maama,ina zuwa haka?” Ba tare da ta tsaya ba ta bashi amsa
“Zanje wajen jalila,na san wannan halin da ake ciki na yaqi ko yau ko gobe kuma gashi akan yarinyar da ta shigo da ita Office of investigation,nasan hankalinta ba a kwance yake ba,tana buqatar wani a kusa da ita” tsayar da ita jaleel yayi da murmushi a fuskar shi tare da cewa
“Haba maama,in dai don wannan ne ai ba sai kinje ba,duk wannan abin da kike gani nine nan na shirya shi” da mamaki hajiya jameela take kallonshi
“Kai !!! Me ka aikata haka?” Murmushi ne har yanzu akan fuskar shi
“Tun ina yaro nake sawa kowa yake min kallon shashasha,sai na basu mamaki,amma fa lady jalila bata sani ba don ban sanar da ita ba,kuma ina yin wannan ne saboda ita don bata san hatsarin wanann yarinyar shukra a kusa da ita ba” tsabar mamaki kasa cewa komai tayi,kawai ta tsaya tana kallonshi.
A gida sameer yake bawa Abdullahi labarin abinda yake faruwa,domin duk abinda akeyi bai sani ba,da sauri ya tashi domin neman shukra,a bakin qofar quaters din baqin china ya ganta cikin kayanta irin dai wanda talakawan gari suke sawa,yadda aka jera sojojin china,ga kuma sojojin JOSHUN suma a jere suna fuskantar su kamar dai masu shirin yaqi,ta bayanta ya tsaya tare da cewa
“Shukra” juyowa tayi cikin tsoro,ganin Abdullahi ne yasa ta sauke ajiyar zuciya,hannun ta ya jawo har zuwa gidan sameer,suka shigo daki ya fara tattara kayan duk da ya san nashi ne,ganin haka shukra ta jefa masa tamabaya
“Me kenan kake yi?” Ba tare da ya kalleta ba,kuma bai daina abinda yake yi ba ya bata amsa
“Ya kamata ki bar qasar nan,saboda a halin yanzu kina cikin hatsari” Da sauri cikin daga murya tace
“Orabeuni !” (Yaya!)
Juyowa yayi a wannan lokacin ya kalleta
“Naji abinda yake faruwa shukra,Wakilin china ba zai haqura ba har sai ya sameki”
“Amma ni palace maid ce,kuma palace maid basa guduwa,hakan babban laifi ne” shukra ta fada masa
“Kina nufin ki zauna,a basu ke su tafi dake china ko? Idan suka tafi ke kashe ki zasu yi” ya fada mata qwalla tana cika a idonsa,jikinta ne yayi sanyi ganin qwallar da take idonshi,ganin bata ce komai ba ya cigaba da magana
“Kawai kiyi yadda nace,yau da daddare zamu bar garin nan,saboda haka ki shirya kawai” yana gama fada mata haka ya cigaba da hada kayansa,tana masa magana amma bai qara kallon inda take ba balle ya amsa mata tunda ya gama magana.