← Book details Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 34

Sashe 11

Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Chief maid din lady jalila ce tare da wasu maids din suka shigo bureu of music,wajen manager suka nufa tare da isar masa da saqon lady jalila,shukra tana bakin rijiya tana hada kayan wanki zata fara wankesu maids din suka iso tare da manager,manager ne ya kalleta sannan ya kalli chief maid din tare da cewa
“Wannan itace yarinyar da ake magana,amma dai ba wani laifin tayi ba ko my lady?” Ya tambayeta fuskarsa da dan alamun damuwa,murmushi chief maid din jalila tayi
“Ahh babu komai,ba laifi tayi ba akwai wani abu da zata yiwa her highness ne”
Boyayyiyar ajiyar zuciya ya sauke tare da maida kallonshi inda shukra take tsugunne,tare da zuba musu ido cikin rashin fahimtar inda zancensu ya dosa,yanayin ta ya karanta kafin ya bude baki yace mata
“Her highness lady jalilah ce take nemanki” zare ido tayi cikin kaduwa tace
“Lad….ladyyy jalilah kuma? Me nayi?”
Murmushi yayi mata tare da cewa
“Babu abinda kikai mata,amma dai ki tashi kije ko ma menene zaki ji” jikinta a sanyaye ta miqe tare da nufar dakin da take kwana,farar takaddar da take da zanen butterfly dinta ta dauko tare da budewa,runtse ido tayi tare da fadin
“Allah ka taimakeni yau idan na shiga cikin masarauta yau na gamu da court lady din da nake nema”
Saurin miqewa tayi tare da mayar da takaddar ta ajiye a inda ta dauko ta,fitowa tayi inda maids din lady jalilah suke suka tafi tare har quaters din ta.

Daga Shigowar shukrah ta sauke idonta akan lady jalila ta gane ta,farin ciki ne ya lullube ta cikin ranta take cewa
“Ina da tabbacin wannan itace court lady din da nake nema,idan ma ba ita bace toh kamar tayi yawa,duk da shekara bakwai kenan…..” kafin ta qarasa tunanin ta muryar chief maid din lady jalila ta katse ta
“Me kike yi a tsaye,greet her highness”
Daidai lokacin itama jalila ta dawo daga nata tunanin,wanda bata san dalilin da ya sa tunanin ya fado mata a daidai wannan lokacin ba,tunanin ta kuwa bai wuce wani mutum da ta taba haduwa dashi har ya fada mata abinda yake daga mata hankali duk lokacin da ta tuno shi,a hankali ta furta
“Kamar yadda yace duk irin daukakar da zan samu tabbas ni zan zamo inuwar ta (shadow)”
Diriricewa shukra tayi tare da rusunawa sosai tamkar zata kai qasa
“Barka da hutawa your highness”
Murmushi jalila tayi tare da cewa
“Zaki iya zama” a inda take tsaye kawai ta nade qafarta ta zauna a qasa tare da tunanin dalilin kiranta da kuma ta inda zata fara tambayar lady jalila maganar keyholder dinta,muryar lady jalila taji
“Shukrah ko? Na san zakiyi mamakin dalilin da ya sa na kira ki nan” ta dan nisa,ba tare da shukra tace komai ba ta ci gaba
“Na ji qoqarin da kikayi wajen gano gaskiya akan sharrin da aka so a qulla min,na kuma gode sosai,kuma idan ba damuwa ina son in saki wani aiki ne domin aikin yana buqatar sirri,shin zaki iya?”
Daga yadda take zaunen ta qara rusunar da kanta tare da cewa
“Ki fadi dukkan umarninki your highness,zan kasance mai biyayya a gareki”
Murmushin jin dadi jalila tayi tare da cewa
“Akwai saqo da zaki karbo min a wajen mahaifiya ta,sassaqen itatuwa ne kuma kinsan an haramta shigo da magani daga waje,saboda haka sai kinbi a hankali kuma ki tabbatar babu wanda ya ganki yayin da kike shigowa dashi”
Maganar jalila ta dan firgita shukra amma duk da yake yarinya ce,amma tana da qarfin zuciya,fuskarta babu yabo babu fallasa ta rusunar da kanta
“An gama your highness”
Ta fada tare da miqewa ta bar quaters din,sukuku ta koma bureu of music ko sameer bata sanar dashi abinda jalila ta saka ta ba,ta shirya ta cire uniform dinta na bayi tare da sa normal ta dauki hanyar fita daga masarautar.

Oum tasneem ✍️
❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏻❤️

ROYAL CONSORT
Korean inspired novel

©️ marriam mayshanu…. ✍️
Whattpad :Oum_tasneeem

Page 11

Queen dowager ce a kwance a dakinta cikin wata doguwar rigar bacci,gashinta ma a warware,kitse jelar gashin kawai akayi yayinda queen haneefah take zaune da wani baho a gabanta da kuma duster tana tsomawa tana matsewa tare da gogewa queen dowager jiki,dayan bangaren kuma royal doctor ne a tsugunne kanshi a qasa,sai royal nurses guda biyu a bayanshi suma sunyi irin zaman da yayi.
fuskar queen haneefah fal damuwa ta furta
“Sannu maama,Allah ya baki lapia”
Cikin jin jiki dowager tace
“Yauwah sannu queen,nagode da kulawarki,Allah yai miki albarka”
Murmushi queen haneefa tayi duk da damuwar bata bar fuskar ta ba tace
“Ai aiki na ne na kula dake maama,kiyi shiru Allah dai ya baki lapia”
“Ameen ta furta can qasa qasa” tare da lumshe idonta bacci ya dauketa sanadiyyar maganin da aka bata yanzu.

Shukra tana tafe har unguwar da aka kwatanta mata nanne unguwar su lady jalila,tambaya tayi aka nuna mata gidan,da sallamarta ta shiga gidan,wata maid ta tarar a tsakat gidan tana ta kai kawo,jin sallamar shujra yasa ta tsaya don ganin mai shigowar,a hankali shukra take turo kai cikin gidan da ganin maid din ta dan rusunar da kanta kadan tare da cewa
“Barka da warhaka,her highness lady jalila ce ta turo ni” da jin haka maid din murmushi kawai tayi ba tare da ta cewa shukra komai ba ta nufi qofar sitting room haj jameela,jim kadan suka fito tare,shukra da ganin ta ta rusuna tare da cewa
“Barka da war haka,sunana shukra” wani kallon wulaqanci haj jamila ta bita da shi tare da cewa
“Fuskar ki ta nuna min hakan,ba sai kin gabatar da kanki ba”
Nan take shukra ta sha jinin jikinta,haj jamila da maid dinta ne suka fita shukra tabi bayansu har wajen mai magani.
Da zuwansu gidan mai maganin haj jamila ta shiga ciki ta bar shukra da kuma maid dinta a tsakar gida,da shigarta mai maganin ya miqe daga inda yake zaune tare da rusunawa ya gaishe ta
“Barka da zuwa madam”
Ba tare da tace komai ba ta nemi waje ta zauna,shiru ne ya ratsa tsakaninsu kafin daga bisani tace
“Ina fatan maganin ya kammala ko?” Ta fada tana me dubanshi,gyaran murya yayi
“Ehh ana hadawa amma sai zuwa qarfe takwas na dare zai kammala”
Gyada kai tayi tare da cewa
“Ina tare da yarinyar da zata karba,ka tabbatar ba’a samu wata matsala ba,kuma idan har buqata ta biya kana da kyauta mai tsoka”
Washe baki yayi cike da farin ciki yace
“Ai ba za’a samu matsalar komai ba madam”
Tsam ta miqe ba tare da ta qara ce masa komai ba ta fito inda ta tarar da su shukra,sai da tazo dab da shukra sannan ta rage murya tare da cewa
“Ki jira zuwa qarfe 8 sai ki tafi da saqon,Ki tabbata ba’a samu ko wace irin matsala ba,kuma kada ki bari kowa ya ganki,ina fatan kin fahimta”
Cike da ladabi shukra tace
“Na fahimta madam”
Barin shukra tayi anan suka wuce ita da maid dinta.

Waje shukra ta samu ta zauna domin jiran saqon wani mutum ya shigo karbar magani,har ya karbi maganin shi zai wuce daidai inda take ya yarda qulli daya,shukra ce ta tsugunna tare da dauko qullin tace
“Baka ji ba”
Juyowa yayi ya kalleta tace
“Ka yar da wannan” ta fada tana miqa masa qullin maganin da ya yar a qasa,saurin karba yayi tare da cewa
“Aff ban kula bane,nagode sosai”
Murmushi shukra ta yi da ya saka ya tsaya ya qura mata ido kamar mai nazarin wani abu,a haka ya fara tafiya yana tafiya yana waigen shukra kamar dai da wani abin da ya gani a fuskar ta.

Tana nan a zaune har aka kira sallar maghreeb,tambaya tayi inda zatayi sallah aka bata,a nan ta zauna har akayi sallar ishaa ta qara tashi tayi,ta idar tana zaune wani yaron mai magani ya zo inda take tare da sanar da ita maganin ya zama ready,tashi tayi tare da bin bayansa har wajen mai maganin,a daidai lokacin da yake qunshe itatuwa,saiwa da kuma sassaqen magani a cikin wata leda daga nisani yasa zani yai masa daurin da akewa qunshin kaya,inda aka daure ya miqa mata ta karba ta tashi ta bar wajen tare da nufar hanyar komawa cikin palace.

A bangaren mai martaba yau yana police bureu wajen IG din police cikin shigar da ya saba yi idan zai shiga cikin gari,suna zaune suna hirar daren da suka kama mutanen da suke dauke da salt stone dinnan mai martaba yace
“Ai a wannan daren na hadu da wani abin mamaki,a karo na farko naji kamar nima mutum ne kamar kowa,babu durqushe durqushe,babu magana dani ana qin kallon idona”
Cike da mamakin kalamansa IG yace
“Your majesty me hakan yake nufi?”
Cikin murmushin da yake tabbatar da yana jin dadin labarin da yake bayarwa yace
“Yarinyar da ka nemo min kace a bureu of music take,kai ranar har fa gadon bayana ta taka ta hau katanga” ya qarasa tare da fitar da sautin dariya sosai cike na nishadi,haka dai suka cinye lokacin yana ta bashi labarin shukra da yadda suke haduwa bayan nan da irin yadda yake jin dadin hira da ita har qarfe takwas tayi suka tashi domin komawa palace.
Chapter 11 · 0% Book details