← Book details Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 34

Sashe 18

Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washegari da safe,a office of investigation,chief sumayya ce sai Sameerah da Aliya a bayanta,sun taho daga bangaren da ɗakunan baccinsu yake zuwa cikin office,wata tawagar investigators ne suka taho,wacce take gaba kayanta iri daya sak da na chief sumayya,ganin yadda chief sumayya da tawagar ta suka dakata suka tsaya cak a inda suke tare da rusunar da kansu a tare hakan yasa na gane mai tahowar wata babba ce a wajen,qarasowarta wajen chief sumayya tace
“Barka da shigowa Director”
Suma wanda suke bayanta haka suka furta a tare,hakan ya tabbatar min da cewar ita wannan matar tafi sumayya matsayi a wajen,wato itace director ɗin office of investigation gaba ɗaya,fuskarta ɗauke da murmushi ta kalli sumayya tare da cewa
“Ina fatan lady jalila ta shirya domin tafiya ofishin tribunal” itama sumayyan murmushi tayi tare da rusunar da kanta tace
“Ta shirya ranki ya dade,guards din tribunal kawai muke jira wanda zasuyi mata rakiya zuwa can” jinjina kai director tayi cike da gamsuwa tace
“Office of investigation kunyi qoqari matuqa a qarqashin jagorancin ki kun kammala case mai wahalar ganewa,idan komai ya lafa zamuje tare domin ki gana da queen dowager”
Murna ne da tsantar farin ciki ya bayyana a kan fuskar sumayya,cike da zumuɗi tace
“Ranki ya dade da gaske zanje wajen queen dowager?” Murmushi director tayi mata na tabbatar wa da abinda ta fada sannan ta yi gaba ta tafi ta bar su sumayya a wajen.
Sameerah ce ta qaraso gaban sumayya tare da ce mata
“Congratulations my lady,ba qaramar karramawa bace zuwa ganin queen dowager”
Ta fada itama cikin tsantar farin ciki,sameerah ce ta qara qasa qasa da muryarta
“Dama aikinmu dole yasa queen dowager farin ciki tunda dama tana neman yadda zatayi da jalila kuma gashi ta samu,wataqila ke zaki zama next director a office dinnan”
Sumayya ce itama ta mayar mata cikin rada
“Ke ki daina gaggawa,mu fara zuwa ma mu gaisa da its kafin ki fara tunanin zama director “ ta qarasa cike da murmushi da yake nuni da tsantsar farin cikin da take ciki.

Tana shiga cikin office dinta taci karo da nadeeyah da basma wanda a qa’ida su suke biye mata a matsayi,tashi sukayi cikin girmamawa da rusunawa suka gaishe ta sannan suka koma suka zauna,cike da ladabi nadeeya tace
“Ranki ya dade akwai abin dubawa da muka ga ya dace a qara bincikawa a al’amarin nan”
a take farin cikin da ke fuskarta ya gushe,ta kallesu a tsanake tare da cewa
“Kamar ya a sake bincike? Ban gane ba”
Har basma zatayi magana,nadeeya ta katse ta da cewar
“Ranki ya dade bayan an sallami yarinyar nan shukra,ta sameni take fada min lallai fa lady jalila bata da laifi,hakan yasa na nemi taimakon basma muka tafi kasuwa inda ake dealar itatuwan,mun duba littafin da suke record kuma mun tabbatar sama da shekara uku ba’a siyar wa wannan mai maganin itacen pinellia ba,shiyasa muke tunanin idan aka sake bincike za’a iya gane inda matsalar take”
Chief sumayya tayi kasake tana jinta,sai da ta gama tsaf sannan tace
“Toh kuma sai akace don bai siya pinellia ba shikenan ba zaiyi amfani da ita ba,mu mun gama bincike kuma babu abinda zai sa mu sake wani bincike a halin yanzu,bayan ana ganin mun qara ɗaga darajar office of investigation har ana tunanin queen dowager zatayi mana tukwuici shine zaku kawo mana wani zancen banza?”
Basma cikin murya mai sanyi tace
“Ranki ya dade idan mukai haka za’a hukunta wanda ba shi yayi laifi ba,alhalin mai laifin yana nan yana yawo a cikin masarautar nan”
Wata gigitacciyar tsawa chief sumayya ta buga mata
“Ai sai kuma ku yi!!! Na fada muku ku ajiye wannan shirmen zancen da kuka samo domin bincike ya qare”
Kafin su nadeeya su farfado daga tsawar da aka daka musu,sameerah ta shigo da gudu har tana tuntube,da dukkan alamu cikin tashin hankali take
“My lady ki fito kiga me yake faruwa a waje”
Zumbur chief sumayya ta miqe da sauri tayi waje,haka nan nadeeya da basma suka bita domin ganin me yake faruwa,chief sumayya ce cike da mamaki tace
“Kamar royal guard nake gani,ina tribunal guard din kuma?”
Afrah da take tsaye ce tayi saurin qarasowa wajen chief sumayya
“My lady sun ce sunzo ne qarqashin umarnin mai martaba domin tsaron lafiyar lady jalilah”
Cike da rudani ta kalli afrah kafin tace wani abu sai ga royal chief secretary ya taho da sauran sakatarorin cikin masarautar suna dauke da tray wanda takadda ce a kai,shigowar su yasa dole director ta office din ta fito daga office,suna qarasowa dukka ladies investigators din suka rusuna don girmama su,domin da an ga chief secretary toh anga umarnin mai martaba,hannu ya miqa aka miqo masa takaddar da suka zo da ita,kai tsaye ya miqawa director din,a hankali ta bude takaddar ta fara karantawa,tashin hankali da firgici ne qarara ya bayyana akan fuskarta har takai qarshen takaddar,juyawa tayi tare da miqawa chief sumayya,tashin hankalin da sumayya ta shiga yafi wanda director ta shiga sai aka shiga kallon kallo a tsakaninsu,sauran ladies investigators da suke tsaye basu san me yake faruwa ba duk sun shiga rudanin shin me yake shirin faruwa a safiyar yau?

Oum tasneem ✍️
❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏻❤️

ROYAL CONSORT
Korean inspired novel

©️ marriam mayshanu…. ✍️
Whattpad :Oum_tasneeem

Page 18

A ɓangaren queen dowager bata san me yake faruwa a office of investigation ba,jikinta yayi qwari sosai tayi shigarta kamar yadda ta saba cikin alkyabbarta ta alfarma,tana zaune inda ta saba zama a sit room dinta,ɗan ɗaga murya tayi
“Waye a nan kusa?” Ta fada tana mai kallon qofa,chief maid dinta ce ta shigo da sauri tare da rusunar da kanta tace
“Ranki ya dade,kamar kina kirana ko?” Jinjina kai tayi
“Ehh ni na kiraki,kuyi shiri yanzu zamu fita” cewar queen dowager,qara rusunawa chief maid din tayi
“Ranki ya dade,ina zamu je a wannan lokacin?” Dago kanta tayi ta kalleta tare da bata amsa
“Ba yau da safennan za’a miqa lady jalila zuwa tribunal ba? Ya kamata naje rakiya saboda darajar qawancen da ke tsakanin mu” ta qarasa cikin shu’umin murmushi,amsawa chief maid din tayi tare da fita domin shirin fitar su.

Lady jalila tana zaune tayi nisa cikin tunani taji shigowar mutum,ɗagowar da zatayi taga chief maid dinta ce,da sauri chief maid din ta qaraso gaban lady jalila,cikin fuskar alhini tace
“Maa- maa” (your highness)
Murmushi jalila ta yi mata tare da cewa
“Me ya kawo ki nan a wannan lokacin,na zata kuma kuna karɓar hukunci saboda laifin uwar dakin ku” rusunar da kanta tayi,qwalla ta tsatstsafo a idonta,daga bisani tace
“Mun sha wahala my lady,amma wannan ba komai bane domin muna can amma zuciyar mu a cikin tunanin ki take,da fatan kina lapia”
Jinjina kai kawai jalila tayi alamar “Eh “ cike da tausayin ma’aikatan nata,
“Your highness yanzu zaki fita daga wajen nan domin an samu hujjar cewa baki da laifi” zumbur lady jalila ta miqe daga inda take zaune,idonta suka fiffito take kallon chief maid dinta cike da mamakin furucin da yake fitowa a bakinta daidai lokacin da ta riga ta yanke tsammanin fita daga wannan matsalar,cike da rikici tace
“Me kike nufi da hakan? Hujjar cewa bani da laifi? Ta yaya kenan?”
Rusunar da kanta tayi
“Yarinyar nan shukra itace ta samo hujjar,kuma mai martaba ma da kanshi ya tabbatar da hakan,saboda haka yanzu chief secretary ya shigo cikin nan wajen tare da royal order domin a wanke ki daga laifi” wani farin ciki ne mara misaltuwa ya bayyana a kan fuskar jalila,da sauri tayi hanyar fita waje chief maid dinta ma tabi bayanta,tana fitowa ta tarar da duk ma’aikatan office of investigation sunyi layi kamar ‘yan assembly suna jiran fitowar ta,director da chief sumayya da green din uniform dinsu a gaba,nadeeya da basma da ash din uniform dinsu a baya,sai sauran ladies masu pink din uniform kusan su 30 suma a baya duk sunyi layi layi kamar assembly dayan bangaren kuma maids din lady jalila da suka zo yi mata rakiya,a daya bangaren kuma royal guards ne da suka zo tsaron lafiyar jalila,sai kuma su chief secretary da sauran sakatarorin masarautar suma a gefe guda.

Tana fitowa ta tsaya kan step din office da ta fito,dukkan mutanen wajen suna qasa da ita,director ce ta fara magana
“Ki yafe mana your highness,haqiqa munyi babban kuskure,ki yafe mana” ta fada tare da rusunar da kanta har wuyanta qasa sosai alamun neman afuwa,chief sumayya ce da idon ta yai qifi qifi itama ta rusuna tare da cewa
“Haqiqa mun aikata mafi munin kuskure,ki yafe mana your highness” ta qarasa tare da qara rusunar da kanta qasa sosai,sauran ladies dinne gaba daya suka rusunar da kansu tare da fadin
“Forgive us your highness”
Cikeda nutsuwa jalila ta sauko daga inda take tsaye sai da tazo daidai inda sumayya take
“Bana jin hakan zai yiwu” ta dan ja numfashi yayin da wajen gaba daya yayi tsit suna sauraron abinda zata fada,suna da tabbacin a halin yanzu idan kashe su tace tana so ayi to fa hakan zai tabbata shiyasa duk a tsorace suke da lamarin
“Ina tunanin ai ba ni zaku bawa haquri ba,qaramar yarinyar da ta gano abinda ‘ya’yan manya,masu ilimin bincike irinku suka kasa ganowa,lallai kun kasa akan aikin ku,kun kuma nuna baku cancanta ba” ta qarasa tana kallon cikin idon sumayya
“Ya kika ji lady sumayya? Slave girl ta fiki sanin ilimin bincike,a yanzu ina ganin ina da damar da zan damu da makomarki a nan gaba ai ko?tunda kince bani da damar hakan a matsayina na mai laifi” shiru sumayya tayi sai qara sunkuyar da kai da tayii,cikin tsawa lady jalila tace
“Ko ba haka kika ce ba!!!?” Sosai lady sumayya ta firgita da yanayin jalila domin daga ganinta tana cike da tsananin bacin ran maganganun da ta dinga fada mata,qara hada baki sukai gaba dayansu tare da cewa
“We made a terrible mistake your highness,please have mercy on us” ba tare da ta qara cewa komai ba ta fara tafiya,tsakiyar su ta nufa,a take suka dare gida biyu,sukai gefe da gefe suka bude mata hanya har yanzu kansu a qasa yake har ta bar wajen tare da maids dinta da suke take mata baya sai kuma royal guards.
Chapter 18 · 0% Book details