← Book details Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 34

Sashe 28

Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washegari da safe,a office dinsu shukra dukkansu ne a tsatstsaye kowa da abinda yakeyi,sameerah ce ta kalli shukra
“Shukra ko zaki duba wadannan litattafan sai ki jera su a tsari ki mayar inda suke?” Cikin murna shukra tace “Ehh zan iya,bari nayi” nan da nan ta fara dudduba littattafan domin hada su ta ajiye a ma’ajiyar su,daya bayan daya suka fara fita daga wajen har ya kasance daga ita sai Afrah a tsaye a wajen,shukra ce ta juya ta kalli inda afrah take
“Kingani ko? Yanzu sun fara yi min magana,har ma aiki suka fara sani in taya su” ta fada cikin farin ciki kamar wani abin arziqi aka sata tayi,afrah ce ta kalleta ta gefen ido tare da cewa
“Toh yanzu ke murnar me kike? Kawai don ance ki mayar da littattafan da ba ke kikai amfani dasu ba? ai hakan raini ne ba girmamawa ba,meyasa basu mayar da kansu ba?” Shukra ita dai hakan bai dameta ba,sai ma zancen da ta sauya
“Yauwah my lady naga kowa ya fita yana shiri,yau me akeyi a nan ne?” Afrah da take karanta wani littafi,ba tare da ta kalli shukra ba ta bata amsa
“Yau ‘yan police bureu da tribunal zasu zo domin yi mana training akan investigation (bincike) ne,shiyasa kowa yake shiri domin yau samari masu ji da kansu da kuma matsayi zasu zo” murmushi shukra tayi daidai lokacin da ta gama jera littattafan,kafin tace wani abu afrah ta ajiye littafin dake hannunta ta fice,hakan yasa itama ta bar wajen,quaters din su suka koma inda taga dukkan ‘yan matan suna gaban mudubi,suna kwalliya,masu sa powder nayi,masu sa lip gloss ma nayi domin babu jambaki mai kala a tsarinsu,ita abinma mamaki ya fara bata yadda taga kowa yana ta gyare gyaren jiki don samari zasu shigo office dinsu,nadeeyah ce da basma cikin uniform dinsu suma sun fito daga daki,suka ci karo da ‘yan matan kowa tana kwalliya,nadeeya ce tayi saurin cewa
“Kalli abinda yaran can sukeyi,bari naje…..” kafin ta qarasa basma ta katse ta
“Haba ke kuwa,ki qyale su mana,ba’a barin su suyi kwalliya lokacin aiki ,amma yanzu tunda training ne,ki qyale su mana” ta fada tana murmushi,kallonta nadeeya ta tsaya yi,kafin tayi murmushi
“Ai kyace a qyale su tunda kema ai kin shafa powder ko?” Zaro ido basma tayi tare da jin kunya,tace
“Toh ai kinsan IG din police zai zo ko? “ dariya sukasa gaba dayansu tare da barin wajen.

Gida biyu aka raba ‘yan matan,kowa da inda zasuyi training din,’yan tribunal zasu koyar da rabi yayinda ‘yan police bureu zasu koyar da rabi,a cikin ‘yan police bureu da aka taho office of investigation har da abdullahi domin zasuyi topic din binciken gawa ne,saboda haka zai taimakawa IG don ganin sun fahimci darasin sosai,yayinda ‘yan tribunal kuma jameel ne dan gidan tribunal minister wato mariqin lady jaleela,da wani abokinshi suka je,shukra ta kasance a bangaren wanda zasu dauki darasin ‘yan tribunal,yayinda afrah kuma take cikin wadanda zasu dauki darasin ‘yan police bureu,hakan yasa shukra basu hadu da sabon mai binciken gawa ba wato abdullahi,amma su afrah sun ganshi.

Bayan an gama training dinne,su sameer suka nemi ganin shukra,a bureu of music taje ta samesu,suna hangota tana tahowa sameer yace da qarfi
“Gaskiya uniform din ladies investigators yayi miki kyau sosai my lady” yana murmushi,itama murmushin ta mayar masa daidai lokacin da ta qaraso gabansu tare da gaishesu,sameer ne yayi saurin ce mata
“Shukra wani taimako nake nema a wajenki domin ke kadai ce zaki iya yi min shi” cikin damuwa shukra tace
“Wane irin taimako ne wannan yallabai?” Abin da ya dauko a dakin abdullahi ya ciro a aljihun shi ya riqe a hannunsa tare da cewa
“Akwai wani sabon mai binciken gawa a police bureu da yake haya a gidana,to naga kamar alamun rashin gaskiya a tare da shi,shine na kawo miki wannan ko zaki bincika min me hakan yake nufi” ya qarasa tare da miqo mata abin,da sauri shukra ta karba tare da zare ido tana kallon logo din da yake jikin abin,cikin razani ta dago ta kalli sameer “kace sabon mai binciken a police bureu?” daga kai sameer yayi,alamar “Ehh” kafin ya bude baki yayi mata qarin bayani shukra ta fella da gudu ta bar wajen,qwala mata kira suka fara yi,amma inaa tayi nisa.

Police bureu ta nufa kai tsaye,da yake akwai uniform a jikinta shiyasa babu wanda ya hana ta shiga,daga ganinta tana cikin tashin hankali,wani security ta tsayar tare da tambayar shi
“Dn Allah sabon mai binciken gawar da aka dauka aiki a wajen nan nake nema” kafin ya bata amsa sai da ya rusunar da kanshi alamun girmamawa sanadin kayan da ya gani a jikinta,sannan yace
“Abdullahi kike nufi,Baya nan my lady,sun fita shi da IG har yanzu basu dawo ba amma ina tsammanin sun biya wani wajen ne” da sauri ta kalle shi sosai tare da cewa
“Sunanshi abdullahi?” Jinjina kai yayi tare da cewa
“Ehh abdullahi sulaiman sunanshi,amma meyasa kike nemanshi my lady?” Ai daga inda yace sunanshi abdullahi sulaiman shukra bata qara jin komai ba,don gaba daya hankalinta baya jikinta,ganin ba zata qara kulashi ba yasa yayi gaba abinshi,yayinda ita kuma tana tsaye ta kafe idonta waje daya qwalla na zubo mata wanda da alamu bata san suna zuba ba.

Oum tasneem ✍️
❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤

ROYAL CONSORT

©️ marriam mayshanu…. ✍️

Page 25

Har dare sameer da manager suna nemanta amma basu ganta ba,hakan yasa sameer dawowa gida kuma har lokacin abdullahi bai dawo ba,yana tsaye yana ta kai-kawo a tsakar gidan yaji shigowar abdullahi,turus yayi ganin sameer a gidan,sameer ne yace masa
“Yau baka dawo da wuri ba,lapia kuwa?”
“Lafiya qalau,na biya wani waje ne” abdullahi ya bashi amsa
“Toh sai ka shiga ka kwanta”
“Toh yallabai” abdullahi ya fada tare da shiga dakinsa,yana shiga ya fara bin dakin da kallo ya san an taba masa kaya,hakan yasa ya duba abinda yake tunanin shi za’a dauka kuwa yaga baya nan,fitowa yayi ya murde hannun sameer ta baya tare da cewa
“Ina headband dina? Me kayi dashi?” Cikin jin zafin yadda abdullahi ya murde masa hannu ta baya yace
“Kayi haquri dauka nayi na bawa wata lady investigator saboda ban yadda da logo din da yake jiki ba” da sauri abdullahi yace
“Lady investigator kuma?”
“Ehh kamar qanwa take a wajena,amma ina bata ta gane LOGO din da yake jiki ta fella da gudu ta tafi nemanka kuma har yanzu ban ganta ba” jin haka da sauri ya saki hannun sameer ya juyo daidai fuskarsa tare da cewa
“Kace ta gane LOGO din da yake jiki?” Gyada kai sameer yayi
“Ehh shukra ta gane logo din” jikin abdullahi ne gaba daya yayi sanyi,da qyar yace wa sameer
“Kace sunanta shukra?”
Gyada kai sameer ya qara yi
“Ehh sunanta kenan,shukra Anas malak”
Qwalla ce kawai ta cicciko a idon abdullahi,yacewa sameer
“Taho muje ka kaini cikin palace din,ni zan nemo ta”

Suna zuwa cikin palace,bureu of music suka fara zuwa,manager ya shaida musu yanzu shukra ta bar nan kuma ta tafi gidansu ne nemanshi,hakan yasa suka qara juyowa suka dawo.
Da zuwanta ta tarar babu kowa a gidan,tana ta bude bude,ta shiga nan ta shiga can,tsayawa tayi tana tunani
*FLASHBACK*
tana yarinya qarama suna tsaye da abdullahi a tashar jirgin ruwa da je garin,irin headband din da sameer ya samo a dakin abdullahi ne a hannunsa yana nunawa shukra
“Shukriyya,kada ki manta da wannan zanen (logo) domin matuqar dai kina tare da wannan abin to komai dadewa zan dawo gareki” gyada kai tayi tare da cewa
“Ba zan manta da hakan ba,amma kwana nawa zakayi ka dawo?” Murmushin jin tausayinta abdullahi yayi tare da cewa
“Duk dadewar da zanyi,nayi miki alqawarin zan dawo gareki,ki kula da kanki”
Motsin da taji ne ya dawo da ita daga tunanin da ta tafi,juyowar da zata yi suka hada ido da abdullahi,hannunta ne ya saki kamar babu jini a jikinta ta daskare a tsaye a wajen,matsowa yake yi kusa da ita yana cewa
“Shukriyya,Ke ce? Shukriyya” hawayen farin ciki ne kawai ya lullube fuskar ta,sheshsheqar kuka ta fara,hakan yasa yayi saurin qarasowa gareta tare da rungumeta sosai a jikinsa,a hankali ta bude bakinta tare da cewa
“Orabeuni” (Babban yaya in korean)
Dagota yayi daga jikinshi yana kallon fuskarta tare da cewa
“Qara fada shukra,ni ne” hawayen bai daina zuba a idonta ba tace
“Dama kana raye? Zaka dawo gareni Yaya Abdallah?”
“Ina nan Shukriyya,dama na fada miki duk dadewar da zanyi nayi miki alqawarin zan dawo gareki”
Tuni suka manta da sameer a wajen,hakan yasa shima ya basu waje,nan gaba ya nemi qarin bayanin alaqar da ke tsakaninsu,waje suka samu suka zauna,shukra da har yanzu da hawaye a fuskarta tace
“Yaya duk lokacin da zanyi wa su Abbana addu’ah ina hadawa hadda kai domin ban taba tunanin kana nan a raye ba,na zata ni kadai ce na rage bani da sauran dangi a duniya” murmushi yayi mata shima da hawaye a fuskarshi tare da cewa
“Na dade ina nemanki shukra,amma ban sameki ba,duk cikin garin nan babu inda ban zagaya ba amma ban sameki ba”
Shiru shukra tayi ba tare da tace komai ba,abdullahi yana mata kallon tsanaki ganin yadda ta girma,tare kuma da farin cikin qara ganin qanwar tasa,jan hanci tayi da ya taru da majina
“Yaya kullun ina tunaninku,da Abba da yaya Abdulshakur,ina ma ace zan qara jin muryoyinsu suna kirana shukriyya?” Tausayinta ne ya lullube shi,dafa kafadarta yayi
“Shukriyya Abba zai yi matuqar farin ciki a duk inda yake domin kema kina cikin farin ciki,kuma nayi masa alqawarin zan kula dake,zan zame miki garkuwa” haka suka yini tare,da yake tunda zata shigo cikin gari ta cire uniform dinta ta skaa normal kaya,hakan yasa babu mai ganeta suka cigaba da zama a cikin gidan tare da hirar yaushe gamo har dare,a nan ta kwana sai da asuba ta koma office of investigation.
Chapter 28 · 0% Book details