Sashe 14
Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A office of investigation chief madam ce take cewa shukra
“Da alama bakya son rayuwar ki,ki fadi abinda ake buqata ki bar wajen nan kema ki huta amma kinqi ko?”
Shukra ta bude baki cikin yunwa da qishirwa tace
“Magana ta daya ce,banyi hakan akan unarnin kowa ba kuma babu pinellia a cikin abinda na shigo dashi” ta qarasa da qyar.
“Nice nan na saka ta shigo min da maganin”
Dukkansu suka kalli daga inda maganar ta fito,da mamakinsu lady jalila ce,chief madam da sauri ta qarasa inda take ta tsaya,dan rusunar da kanta tayi kamar an mata dole tare da cewa
“Your highness kinsan me kike fada kuwa?”
Gyada kai jalila tayi tare da buga mata harara
“Tabbas na san me nake fada,ko ba abinda kike son kiji yarinyar nan ta fada bane? Shine na fada miki da bakina,sai ku sake ta ta tafi domin bata da laifi”
Chief madam ta kafeta da ido babu ladabi tace
“Hakan yana nufin office dinmu zai bincike ki fah kenan your highness”
“A shirye nake da hakan shiyasa kika ganni a nan”
Umarni chief madam ta bayar a saki shukra a kuma raka lady jalila inda za’a yi mata tambayoyi,shukra cikin galabaita ta daga kanta ta kalli jalila
“Me yasa kikai haka your highness? Ni da ke mun san bamu shigo da pinellia ba,meyasa zaki dauki laifin da ba ke kika aikata ba?”
Murmushin takaici tayi ta kalli shukra tace
“Nayi hakan saboda ba zan iya jurewa kina cikin wannan halin saboda ni ba,ko ba komai ni zan samu sassauci ko don kasancewa ta CONSORT a cikin masarautar nan,kuma in har kin yadda bani da laifi komai daren dadewa gaskiya zata fito,ki yafe min akan wahalar da kika sha saboda ni”
Tana gama fadar haka ta shige ciki ta bar shukra a nan,kunce shukra akayi,cikin warfin hali take takawa cikin rakiyar special lady investigator mai ash uniform guda daya (Basma) da kuma lady investigator mai pink uniform guda daya(Aliya) sameer da manager da suke tsaye a bakin wajen suka jiyo motsin tafiya,buya sukayi da sauri yayinda su shukra suka qaraso bakin qofar,cikin girmamawa shukra ta daure tayi da rusunar da kanta
“Nagode” ba tare da sunce mata komai ba suka juya zasu koma ciki maganarta ta tsayar dasu
“Amma ne zai faru da lady jalila?” Ta fada cikin nuna tsantsar damuwar ta
Aliya ce ta kalleta kamar zata kai mata duka tace
“Ina ruwanki da abinda zai faru da ita,ke dai tunda kin tsira maza bace daga nan” ta qarasa cikin fada,shiru shukra tayi su kuma suka koma suka barta a tsaye a wajen,duk abinda akeyi a kunnen su sameer da manager da suke labe,suna ganin investigators din sun bar wajen suka fito kowannen su da saurin shi ya qaraso inda shukra take tsaye,cikin farin cikin ganinsu gaba daya ta jefo musu
“Me kukeyi a nan? Saboda ni kuka zo?”
Manager ne ya bata amsa da
“Ko bacci bamu iya yi ba jiya saboda fargabar halin da kike ciki,basu ji miki ciwo ba ko?”
Jikinta yake bi da kallo wai yana neman ko sunji mata ciwo,sameer da yake tsaye bai ce komai ba ne ya miqo mata gorar ruwa,da sauri ta karba ta fara sha kamar bata taba sha ba,tausayinta ne ya rufe su gaba daya suka zuba mata ido,sai da ta sha yadda ya ishe ta sannan ta sauke gorar daga bakinta tare da kallon sameer tace
“Nagode yallabai,nagode da nuna damuwarku a gareni”
Manager ne ya cafe
“Kema sai ki daina janyo mana magana da rashin jin ki da karambani” shiru tayi tare da sunkuyar da kai
“Ni tunani na ma wane irin hali lady jalila zata shiga”
Sameer yai saurin cewa
“Ai da sun gama yi mata tambaya zasu barta ta tafi tunda matar sarki ce ai ba zasu riqe ta ba kuma gashi ma tana da juna biyu”
Jinjina kai manager da shukra sukayi,suka fara tafiya domin komawa bureu of music.
Suna qarasawa abinci ta samu mai rai da lafiya sun tanadar mata,ta zauna taci mai isarta,iya gata taga gata a ranar domin shaquwar su ta qara habaka sosai.
Lady jalila a kan teburin tambayoyi,chief madam inspector ce (lady sumayya) tana zaune akan kujerar da take fuskantar jalila,cikin girmamawar da bata kai har zuciyar ta ba tace
“Your highness ina fatan zaki bamu hadin kai domim amsa dukkan tambayoyin da zamuyi miki”
Cikin qasaita jalila tace
“Tsawon wani lokaci tambayoyin naku zasu kai?”
Lady sumayya tace
“A bisa tsari suna kaiwa tsawon awa daya”
Jinjina kai jalila tayi alamun gamsuwa,miqewa lady sumayya tayi tare da kallon special investigator da take kusa da ita mai ash uniform(Nadeeya) da kuma lady investigator mai pink din uniform (Afrah) sannan tayi hanyar fita,nadeeya da afra ne tabi bayanta,kafin su qarasa bakin qofar office din sumayya ta tsaya ta kalli nadeeya tare da cewa
“Ke nadeeya kije ki samu basma ku tafi quaters din lady jalila ku bincika komai a wajen,kada kubar komai baku duba ba,mu kuma zamu tsawaita lokacin tambayoyin har ku gama abinda kukeyi zamu riqeta a nan” ta fada a cikin sigar bada umarni,cikin girmamawa nadeeyah ta rusunar da kanta tare da cewa
“Yes my lady”
Chief madam ta juya ta kalli Afrah “ke kuma muje duk abinda ta fada ki dinga rubutawa,kuma ki tabbatar bakiyi rubutu da sauri ba”
Rusunar da kanta afrah tayi tare da cewa
“Yes my lady”
Chief madam sumayya da afrah suka koma ciki yayinda nadeeya kuma ta fita neman basma.
Jameel ne cikin tashin hankali yake shigowa dakin mahaifin sa,a zaune ya tarar da mahaifinsa nasa a inda ya saba zama yayi zurfi cikin tunani,zama shima yayi a qasa tare da cewa
“Abba kaji abinda yake faruwa kuwa? Jalila fa ta kai kanta office of investigation “
Jinjina kai ba tare da yace komai ba kuma bai juyo ya kalli jameel ba,ba komai yake tunawa ba sai lokacin da jalila take fada masa zata miqa kanta saboda wata baiwa,jameel ne ya qara cewa
“Abba kamar baka jin abinda nake cewa”
“Ina ji mana,yanzu me kake so muyi jameel? Jalila ta san cewa dukkan yankin mu sun dogara ne da qarfin ikonta a cikin masarauta kuma ta aikata hakan,yanzu idan muka ce zamu shiga muma zata iya jan mu ta goga mana laifin,saboda haka abinda yafi kawai shine mu qyale ta taji da abinda ta daukowa kanta”
Cike da mamaki jameel yake kallon mahaifin nasa,yace
“Haba Abba,ko ba komai jalila fa ‘yar dan uwanka ce,ni dai a ganina mu nemi yadda zamuyi mu dorawa wani laifin amma jalila ta kubuta,ko da wannan baiwar ce shukra tunda mayar da laifin kanta zai fi sauqi tunda itace ta shigo da maganin”
Shiru tribunal minister yayi yana nazarin maganar da jameel yake fada,cikin qara gamsar dashi jameel ya qara cewa
“Ina jin a jikina akwai wani abu da son qullawa jalila a cikin masarautar nan,domin kuwa mai bada maganin nan shi kadai ne shaidar cewa bata karbi pinellia a wajenshi ba kuma kaga an kashe shi saboda wata manufar”
Gyaran murya minister yayi tare da cewa
“Zancen ka gaskiya ne jameel,idan muka bar jalila ta fadi to muma mun fadi,zamu san yadda za’ai a mayar da laifin kan yarinyar yadda ko jalila ba zata iya kareta ba”
Cikin gamsuwa jameel yace
“Nagode da ka fahimceni Abbana”
Murmushi yayi masa tare da shafa fuskar sa yace
“Idan ban fahmce ka ba,wa zan fahimta babban mutumi?” Murmushi jameel ya mayar masa tare da tashi ya bar dakin.
Oum tasneem ✍️
❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏻❤️
ROYAL CONSORT
Korean inspired novel
©️ marriam mayshanu…. ✍️
Whattpad :Oum_tasneeem
Page 14
Duk tsawon lokacin da suka dauka a qarshe dai aka gama yiwa lady jalila tambayoyi,afrah ce ta kalli lady jalila cikin girmamawa tare da cewa
"Your highness zan aika a kirawo maids dinki su raka ki quaters dinki" lady jalila ta miqe tsaye ba tare da ta kalli afrah ba tace
"A ah ki barshi,na san guda biyu suna jirana a waje,zamu tafi tare da su" tana magana tana takawa zuwa hanyar waje.
A daidai wannan lokacin an birkita ko ina a cikin quaters din lady jalila ba tare da saninta ba,ladies investigators ne masu pink din kaya ko ina a cikin quaters din suna ta bincike bincike,wata murya ce mai tashi tace
"Ga shi nan na samo" dukkansu suka dakata da abinda sukeyi tare da mayar da hankalinsu inda maganar take fitowa,wata yarinya ce lady investigator Sameerah,Basma ce ta qaraso inda take da sauri,sameerah ta rusunar da kanta tare da miqawa basma abinda ta samo,hakan yasa suka bar binciken tunda sun samu abinda suke nema. Maids din lady jalila suna ta kuka saboda qarshen wulaqancin da akai wa iwar dakinsu na binciken rashin mutunci,kuma gashi ance an samo abinda suke da yaqinin babu shi a cikin quaters din,tabbas wani makircin ne ake qoqarin qulla mata.
“Da alama bakya son rayuwar ki,ki fadi abinda ake buqata ki bar wajen nan kema ki huta amma kinqi ko?”
Shukra ta bude baki cikin yunwa da qishirwa tace
“Magana ta daya ce,banyi hakan akan unarnin kowa ba kuma babu pinellia a cikin abinda na shigo dashi” ta qarasa da qyar.
“Nice nan na saka ta shigo min da maganin”
Dukkansu suka kalli daga inda maganar ta fito,da mamakinsu lady jalila ce,chief madam da sauri ta qarasa inda take ta tsaya,dan rusunar da kanta tayi kamar an mata dole tare da cewa
“Your highness kinsan me kike fada kuwa?”
Gyada kai jalila tayi tare da buga mata harara
“Tabbas na san me nake fada,ko ba abinda kike son kiji yarinyar nan ta fada bane? Shine na fada miki da bakina,sai ku sake ta ta tafi domin bata da laifi”
Chief madam ta kafeta da ido babu ladabi tace
“Hakan yana nufin office dinmu zai bincike ki fah kenan your highness”
“A shirye nake da hakan shiyasa kika ganni a nan”
Umarni chief madam ta bayar a saki shukra a kuma raka lady jalila inda za’a yi mata tambayoyi,shukra cikin galabaita ta daga kanta ta kalli jalila
“Me yasa kikai haka your highness? Ni da ke mun san bamu shigo da pinellia ba,meyasa zaki dauki laifin da ba ke kika aikata ba?”
Murmushin takaici tayi ta kalli shukra tace
“Nayi hakan saboda ba zan iya jurewa kina cikin wannan halin saboda ni ba,ko ba komai ni zan samu sassauci ko don kasancewa ta CONSORT a cikin masarautar nan,kuma in har kin yadda bani da laifi komai daren dadewa gaskiya zata fito,ki yafe min akan wahalar da kika sha saboda ni”
Tana gama fadar haka ta shige ciki ta bar shukra a nan,kunce shukra akayi,cikin warfin hali take takawa cikin rakiyar special lady investigator mai ash uniform guda daya (Basma) da kuma lady investigator mai pink uniform guda daya(Aliya) sameer da manager da suke tsaye a bakin wajen suka jiyo motsin tafiya,buya sukayi da sauri yayinda su shukra suka qaraso bakin qofar,cikin girmamawa shukra ta daure tayi da rusunar da kanta
“Nagode” ba tare da sunce mata komai ba suka juya zasu koma ciki maganarta ta tsayar dasu
“Amma ne zai faru da lady jalila?” Ta fada cikin nuna tsantsar damuwar ta
Aliya ce ta kalleta kamar zata kai mata duka tace
“Ina ruwanki da abinda zai faru da ita,ke dai tunda kin tsira maza bace daga nan” ta qarasa cikin fada,shiru shukra tayi su kuma suka koma suka barta a tsaye a wajen,duk abinda akeyi a kunnen su sameer da manager da suke labe,suna ganin investigators din sun bar wajen suka fito kowannen su da saurin shi ya qaraso inda shukra take tsaye,cikin farin cikin ganinsu gaba daya ta jefo musu
“Me kukeyi a nan? Saboda ni kuka zo?”
Manager ne ya bata amsa da
“Ko bacci bamu iya yi ba jiya saboda fargabar halin da kike ciki,basu ji miki ciwo ba ko?”
Jikinta yake bi da kallo wai yana neman ko sunji mata ciwo,sameer da yake tsaye bai ce komai ba ne ya miqo mata gorar ruwa,da sauri ta karba ta fara sha kamar bata taba sha ba,tausayinta ne ya rufe su gaba daya suka zuba mata ido,sai da ta sha yadda ya ishe ta sannan ta sauke gorar daga bakinta tare da kallon sameer tace
“Nagode yallabai,nagode da nuna damuwarku a gareni”
Manager ne ya cafe
“Kema sai ki daina janyo mana magana da rashin jin ki da karambani” shiru tayi tare da sunkuyar da kai
“Ni tunani na ma wane irin hali lady jalila zata shiga”
Sameer yai saurin cewa
“Ai da sun gama yi mata tambaya zasu barta ta tafi tunda matar sarki ce ai ba zasu riqe ta ba kuma gashi ma tana da juna biyu”
Jinjina kai manager da shukra sukayi,suka fara tafiya domin komawa bureu of music.
Suna qarasawa abinci ta samu mai rai da lafiya sun tanadar mata,ta zauna taci mai isarta,iya gata taga gata a ranar domin shaquwar su ta qara habaka sosai.
Lady jalila a kan teburin tambayoyi,chief madam inspector ce (lady sumayya) tana zaune akan kujerar da take fuskantar jalila,cikin girmamawar da bata kai har zuciyar ta ba tace
“Your highness ina fatan zaki bamu hadin kai domim amsa dukkan tambayoyin da zamuyi miki”
Cikin qasaita jalila tace
“Tsawon wani lokaci tambayoyin naku zasu kai?”
Lady sumayya tace
“A bisa tsari suna kaiwa tsawon awa daya”
Jinjina kai jalila tayi alamun gamsuwa,miqewa lady sumayya tayi tare da kallon special investigator da take kusa da ita mai ash uniform(Nadeeya) da kuma lady investigator mai pink din uniform (Afrah) sannan tayi hanyar fita,nadeeya da afra ne tabi bayanta,kafin su qarasa bakin qofar office din sumayya ta tsaya ta kalli nadeeya tare da cewa
“Ke nadeeya kije ki samu basma ku tafi quaters din lady jalila ku bincika komai a wajen,kada kubar komai baku duba ba,mu kuma zamu tsawaita lokacin tambayoyin har ku gama abinda kukeyi zamu riqeta a nan” ta fada a cikin sigar bada umarni,cikin girmamawa nadeeyah ta rusunar da kanta tare da cewa
“Yes my lady”
Chief madam ta juya ta kalli Afrah “ke kuma muje duk abinda ta fada ki dinga rubutawa,kuma ki tabbatar bakiyi rubutu da sauri ba”
Rusunar da kanta afrah tayi tare da cewa
“Yes my lady”
Chief madam sumayya da afrah suka koma ciki yayinda nadeeya kuma ta fita neman basma.
Jameel ne cikin tashin hankali yake shigowa dakin mahaifin sa,a zaune ya tarar da mahaifinsa nasa a inda ya saba zama yayi zurfi cikin tunani,zama shima yayi a qasa tare da cewa
“Abba kaji abinda yake faruwa kuwa? Jalila fa ta kai kanta office of investigation “
Jinjina kai ba tare da yace komai ba kuma bai juyo ya kalli jameel ba,ba komai yake tunawa ba sai lokacin da jalila take fada masa zata miqa kanta saboda wata baiwa,jameel ne ya qara cewa
“Abba kamar baka jin abinda nake cewa”
“Ina ji mana,yanzu me kake so muyi jameel? Jalila ta san cewa dukkan yankin mu sun dogara ne da qarfin ikonta a cikin masarauta kuma ta aikata hakan,yanzu idan muka ce zamu shiga muma zata iya jan mu ta goga mana laifin,saboda haka abinda yafi kawai shine mu qyale ta taji da abinda ta daukowa kanta”
Cike da mamaki jameel yake kallon mahaifin nasa,yace
“Haba Abba,ko ba komai jalila fa ‘yar dan uwanka ce,ni dai a ganina mu nemi yadda zamuyi mu dorawa wani laifin amma jalila ta kubuta,ko da wannan baiwar ce shukra tunda mayar da laifin kanta zai fi sauqi tunda itace ta shigo da maganin”
Shiru tribunal minister yayi yana nazarin maganar da jameel yake fada,cikin qara gamsar dashi jameel ya qara cewa
“Ina jin a jikina akwai wani abu da son qullawa jalila a cikin masarautar nan,domin kuwa mai bada maganin nan shi kadai ne shaidar cewa bata karbi pinellia a wajenshi ba kuma kaga an kashe shi saboda wata manufar”
Gyaran murya minister yayi tare da cewa
“Zancen ka gaskiya ne jameel,idan muka bar jalila ta fadi to muma mun fadi,zamu san yadda za’ai a mayar da laifin kan yarinyar yadda ko jalila ba zata iya kareta ba”
Cikin gamsuwa jameel yace
“Nagode da ka fahimceni Abbana”
Murmushi yayi masa tare da shafa fuskar sa yace
“Idan ban fahmce ka ba,wa zan fahimta babban mutumi?” Murmushi jameel ya mayar masa tare da tashi ya bar dakin.
Oum tasneem ✍️
❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏻❤️
ROYAL CONSORT
Korean inspired novel
©️ marriam mayshanu…. ✍️
Whattpad :Oum_tasneeem
Page 14
Duk tsawon lokacin da suka dauka a qarshe dai aka gama yiwa lady jalila tambayoyi,afrah ce ta kalli lady jalila cikin girmamawa tare da cewa
"Your highness zan aika a kirawo maids dinki su raka ki quaters dinki" lady jalila ta miqe tsaye ba tare da ta kalli afrah ba tace
"A ah ki barshi,na san guda biyu suna jirana a waje,zamu tafi tare da su" tana magana tana takawa zuwa hanyar waje.
A daidai wannan lokacin an birkita ko ina a cikin quaters din lady jalila ba tare da saninta ba,ladies investigators ne masu pink din kaya ko ina a cikin quaters din suna ta bincike bincike,wata murya ce mai tashi tace
"Ga shi nan na samo" dukkansu suka dakata da abinda sukeyi tare da mayar da hankalinsu inda maganar take fitowa,wata yarinya ce lady investigator Sameerah,Basma ce ta qaraso inda take da sauri,sameerah ta rusunar da kanta tare da miqawa basma abinda ta samo,hakan yasa suka bar binciken tunda sun samu abinda suke nema. Maids din lady jalila suna ta kuka saboda qarshen wulaqancin da akai wa iwar dakinsu na binciken rashin mutunci,kuma gashi ance an samo abinda suke da yaqinin babu shi a cikin quaters din,tabbas wani makircin ne ake qoqarin qulla mata.