← Book details Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 34

Sashe 25

Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Slave din da shukra tayi wa tambayoyi ne a baki rijiya da gudu ta taho quaters din lady jalila,wata attendant dinta ta tarar a bakin qofa,cikin damuwa da gaggawa tace mata
“Nazo wa da lady jalila da labari ne,ya kamata ki sanar da ita yanzunnan,a office of investigation suna can sun saka lady shukra yin jarrabawa” ai da sauri labari yaje kunnen lady jalila,ta kalli baiwar nan tare da cewa
“Me kika ce? Sun sata yin jarrabawa? Ya za’ayi tayi jarrabawa yanzu,shekaran jiya fa ta shiga wajen,ya za’a yi su hada ta da wanda sukai shekara guda suna shiryawa karatun jarrabawar” cikin bacin rai sosai take magana,tare da fara tunanin abinda ya kamata tayi.

Dai dai kiran sunan Afrah tare da shukra aka kira su,suka zo suka zauna,afrah ce ta fara har ta gama,chief sumayya tace
“Afrah - pass” da yake dama duk cikinsu afrah tafisu qoqari,hankali da kuma nutsuwa.
Shukra ce ta miqa hannu ta dauko takadda tare da budewa,tsayawa tayi tana kallon takaddar domin bata iya ba,chief sumayya tace
“Karanto mana” dagowa tayi ta kalleta cikin fuskar tausayi,chief kuwa ta samu yadda take so ta qara cewa
“Ki karanta nace” ajiye takaddar shukra tayi ta fara karantawa,maimaita iya inda aka rubuta a takaddar take, ba tare da ta qara da komai ba,tana ta maimaitawa cikin rashin sanin abinda zatayi,tausayinta duk sai ya cika su nadeeyah da basma domin sun san mugunta dama aka so ayi mata,muryar chief ce take cewa shukra
“Sqi maimaita waje daya kike,ki cigaba mana” kallonta shukra tayi
“Cigaban? Cigaban?” Sumayya cikin dakewa tace
“Ehh cigaban,karanto cigaban”
Rusunar da kai shukra tayi tare da cewa
“Forgive me my lady,amma ban iya cigaban ba”
Sameerah ce ta harareta,aliya ma haka amma ita ta dan ji tausayinta,amma taji dadi tunda zata tafi ta barsu dama bata dace da wajen ba,chief sumayya ce tace
“Shukra - fail” da sauri shukra ta dago kanta ta kalli sumayya,itama ita take kallo cikin rashin tausayi,nadeeya ta sauke ajiyar zuciya domin ba haka taso ba,ta tausayawa shukra sosai haka basma ma,amma babu abinda zasu iya yi,sauran ladies investigators kuwa kowa yana ta murmushin jin shukra ta fadi.

Bayan an gama jarrabawar shukra ce take ta bin chief sumayya a baya tana cewa
“Na roqeki chief ki qara bani wata damar” tsayawa tayi ta juyo tare da kallon shukra
“Wai ba nace ki daina bina ba? Kawai ni nayi qmfani da doka ne,saboda haka ki daina bina”
Shukra ta taugunna tace
“Amma my lady kinsan ban taba karanta littafin nan ba,kuma ke kika ce min na yi jarrabawar nan daidai abinda na iya,ko dai anyi hakan ne dama domin a kore ni daga nan?” Kallonta sumayya ta tsaya yi domin tayi mamakin qarfin halinta,tace
“Ni kike fadawa haka? Bayan na riga na fada miki cewar kawai munbi yadda dokokin suke ne,mu a nan muna girmama doka,ko kina tunanin zamu baki wata alfarma ne a wajen jarrabawa? Yadda akayiwa kowa haka kema akayi miki tunda duk matsayi daya kuke”
Shukra da har yanzu take a tsugunne tace
“Ki taimaka min my lady,ki bani wata damar” cikin daga murya sumayya tace
“Ki dakata haka,idan har kin dauki kanki cikakkiyar lady investigator,to abinda ya kamata kiyi shine ki bi doka ki bar cikin wajen nan salin alin,sai ki jira fitowar sakamakon qarshe amma zamanki a nan ai ya qare” tana gama fadar haka ta yi gaba tabar shukra nan,itama shukra daga murya ta fara yi yadda zata jiyo ta
“Ki taimaka min my lady,hakan ba’a yi min adalci ba,ku qara bani wata damar” ko juyowa chief bata yi ba ta yi gaba abinta,a wajen shukra ta durqushe ta saki kuka mai ban tausayi.

A office dinsu ladies investigators suka shiga kowa da murmushi akan fuskar shi,sameerah tace
“Ni dama nasan chief ba zata taba barin yarinyar nan ta zauna ba,ashe dama abinda ta shirya kenan,yanzu ba shikenan ba mun rabu da ita ba,ko tana so ko bata so dole ta tafi”
Haka kowa yayi ta tofa albarkacin bakinshi,afrah ce tace
“Amma abinda baku sani ba shine,ba shukra bace tayi abin kunya,mu aka jawo wa abin kunya” sameerah ce ta kalle ta
“Kamar ya kenan? Kina taya ta baqin cikin zata tafi ne?” Afra tace
“Abinda nake nufi shine,duk wanda yaji wanan abin yasan an shirya hakan ne,sai a fara kallon office of investigation kamar shashahai kima marasa adalci,akwai wasu hanyoyin da za’a iya bi a koreta amma ba ta haka ba”

A office din chief sumayya su nadeeyah da basma a zaune suna bata baki akan bai kamata ayiwa shukra haka ba,kallonsu take cikin dakewa tace
“Ni dai kawai nabi doka ne,kuma ai kunsan yadda dokar take ko? Nadeeya ce tace
“Amma my lady ya kamata ce an fara mata training tukunna,a halin yanzu fa zuwanta kenan babu training din da ta fara karba”
Sumayya ce ta harareta “shin akwai wata dokar da tace lallai sai mun jira an fara mata training,alhali lokacin jarrabawa yayi?”
Basma ta sa baki
“Amma my lady ba yadda za’ai kayi tunanin yari zai iya gudu,bayan ko rarrafe bai fara ba”
Ran chief sumayya ne ya baci,ta kallesu su biyun tare da cewa
“Ni dai nabi tsarin doka ne,kuma na gama magana ta qarshe” da fadan haka ta tashi ta fita ta barsu a office din,basma ce ta kalli nadeeya
“Yanzu nadeeya yaya zamuyi,haka zamu bar yarinyar nan ta tafi? Ba’a yi mata adalci ba” nadeeya da gaba daya yanayin fuskar ta ya canja zuwa bacin rai sosai tace
“To yaya zamuyi basma?”

Lady jalila tana zaune cikin matuqar bacin rai da ba’a taba ganinta a cikinsa ba,chief maid dinta ce tace mata
“My lady ya kamata kiyi wani abu,domin idan sukayi sa’ar korar shukra toh kema suna wasa ikon ki ne,za’a rage ganin girmanki a cikin masarautar nan” cike da bacin rai jalila tace
“Ai ban taba tunanin zasu iya zubar da girmansu suyi irin wannan abin ba,amma babu abinda zanyi”
“Babu abinda zakiyi your highness?” Chief maid ta tambaya
“Ehh babu abinda zanyi wa shukra a halin yanzu,domin idan na taimaka mata ta tsallake wannan,wani abin zasu qara qirqirowa,tunda ita take zaune dasu ya kamata tayi qoqarin magance wannan matsalar da kanta,mudai mu bita da addu’a a wannan yanayin,domin nasarar ta itace tamu,faduwarta kuma faduwarmu ce”

Oum tasneem ✍️
❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤💃🏽❤

ROYAL CONSORT

©️ marriam mayshanu…. ✍️

Page 23

Shukra tana zaune tana kuka,kamar wacce ta tuna wani abu,tayi sauri ta goge hawayenta,nan da nan ta samu qarfin gwiwar tashi,da sauri take tafiya har tazo library,dube duben wasu litattafai ta fara yi har ta samu wanda take nema,budeshi ta fara yi tana neman wani shafi,murmushi tayi tare da cewa
"Yes,na samu"
Cike da qwarin gwiwa ta fito daga library din,director ta hango suna tafiya chief sumayya tana binta a baya,da gudu ta qarasa wajensu tare da cewa
"My lady,ku taimaka ku saurareni,akwai abinda nake son fada muku" director ce ta tsaya,shukra tazo gabansu ta rusunar da kanta sosai tare da cewa
"My lady,littafinnnan na rules (dokoki) nake ta karantawa tun ranar da nazo shine na ga inda yake nuna an bada jarrabawar nan ba akan qa'ida ba" littafin ta miqo tare da nuna musu layin domin su karanta,sannan ta cigaba da cewa
"A littafin dokoki an rubuta cewa za'a bada jarrabawa ne akan topic din da akayi a shekarar da ta gabata,amma littafin DOCTRINE OF THE MEAN da aka yi mana jarrabawa akai,sati biyu da suka wuce aka fara karanta shi,hakan yasa ba zai iya zama topic din jarrabawa ba" sumayya da tunda shukra ta fara magana ranta ya fara baci,huci kawai take yi tace
"Me kika ce?" Shukra ta kalleta tare da cewa
"Na tabbata kin zabi wanan littafin ne domin kinsan ban taba karanta shi ba,kuma ba'a yi min adalci ba a kan hakan,shiyasa dokar ta bada damar a sake min wata jarrbawar" saukar mari kawai taji a kan fuskarta,chief sumayya tana huci tace
"Ke kin isa ki koya min dokokin office of investigation?ganin dama ta ne na zabi duk inda nake so na bayar ayi jarrabawar akai...." shukra ce ta katse ta
"Amma my lady......"
"Rufe min baki,mutuniyar banza,shashashar yarinya" ta katse ta tare da qara miqo hannu zata qara marinta,director ce ta sa hannu ta tare ta,hakan yasa ta ja baya tare da cewa
"Yes my lady" director ta kalli shukra tare da cewa
"Kince an bada jarrabawa ba daidai ba,ke wace irin yarinya ce mai tsaurin ido? Yanzu me kike so a yi miki? Kina tunanin ko kin karanta littafin zaki ci jarrabawar ne?" Rusunar da kanta shukra tayi tare da cewa
"My lady anyi tsawon sati biyu ana koyar da littafin nan,ina ganin nima idan aka bani sati biyun......" katseta director tayi
"A baki sati biyu? A yanzu hakan ma ai mun bata kwana daya a kanki,wulaqancin da muka samu ta dalilin ki ya isa haka,don haka ki tattara salin alin ki bar cikin office dinnan don nan wajen bai dace da irin ki ba" suka wuce suka barta a wajen.

Sameer ne ya shigo office din manager ran shi a bace yana ta qwala wa manager kira
"Wai kiran na menene ne?" Manager ya tambaya yana kallon inda sameer yake shigowa
"Yallabai mummunan labari ne,ina tunanin shukra ta kusa dawo mana bureu of music" cikin razana manager yace
"Kasan me kake fada kuwa? Me zai dawo da ita?
Sameer ne ya fada masa duk abinda yake faruwa,nan da nan hankalin manager ya tashi sosai,tausayinta ya lullube shi.

Shukra a nan bakin main qofar shiga office of investigation ta zauna tana roqon su (idan kana da wata buqata ko kuma kana son a yafe maka a kan wani laifi,suna yin haka,sai ka zauna qafarka a nade kamar zaman sallah a bakin quaters din wanda kake meman alfarmar shi,ko kwana nawa zakayi,ba ci ba sha duk iska,duk damuna har sai sun fito sunji tausayinka sunyi maka abinda kake nema,hakan yana daya daga cikin al'adunsu) haka shukra ta zauna har yamma,ga hadari ya hado sosai,nan da nan aka fara ruwa mai qarfi tare da iska.
Chapter 25 · 0% Book details