Sashe 23
Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Manager ne yake tahowa inda suke da wasu ma’aikata a bayanshi dauke da tebur din abinci masu yawa,haka suka zo suna ta jerawa,shukra tace
“Yallabai wannan na menene?” Kafin manager ya bata amsa sameer yace
“haba shukra,ba kya gani walima zamuyi” da sauri ya rufe bakinsa, “ina nufin my lady” juyawa tai ta kalli manager hawaye ya cika a idonta,jinjina mata kai yayi cike da farin ciki shima idonshi ya cika da ruwa,wataqila wannan shine zamansu na qarshe don zata bar wajen kenan har abada,haka suka zazzauna kowa ya fara cin abinci,kowa cikin farin ciki gwanin sha’awa.
A police bureu suma IG ne sai lieutenant da assistant suke hirar shukra,a lokacin ne ake hirar yadda aka kai mata official decree of appointment harda cikakken sunanta Shukra Anas malak,jin haka yasa IG fadawa tunani shekaru takwas da suka wuce,kamar yasan wata qaramar yarinya mai irin wannan sunan,amma ita waccan SHUKRIYYA ANAS MALAK ne sunanta,ya kwashe shekaru kusan hudu yana nemanta daga baya ya haqura,amma ya za’a yi ta kasance a cikin masarauta,kuma baiwa? maganar assistant lieutenant ce ta katse masa tunaninsa
“Yallabai,kana da baqo a waje,wani shashashan yaro yazo nemanka”
Tashi IG yayi tare da fitowa waje domin ganin me neman shi,tsayawa yayi yana kallon yadda jaleel yake shashanci da masu gadin wajen cikin uniform dinshi na ‘yan sanda,da rank din lieutenant,har bai ma kula da isowarshi wajen ba,cikin rashin daraja suka gaisa,IG ya bashi warning akan cewar idan yana da hankali da iya aiki zasu zauna lapia domin an kawo shi ne ba akan qa’ida ba,alfarmar minister of tribunal ne,kuma matsayin lieutenant aka bashi daga sama,IG ne ya kalli assistant lieutenant yace
“Ya fika matsayi a rank amma ka fishi matsayi a sanin makamar aiki,saboda haka ka kula da training dinshi” yana gama fadar haka yayi gaba ya barsu,assistant lieutenant yana yiwa jaleel magana amma ko kula shi baiyi ba ya fara tafiya yana zagaye wajen,abdullahi ne ya bullo shi da wani dan sanda da littattafai a hannunsa,abdullahi cikin girmamawa yace
“Yallabai ko zaka bani litattafan sai naje na ajiyesu a inda ake ajiyewa” kallon abdullahi yayi yace
“Zaka iya jerasu kuwa?” Dariya yayyi
“Zan iya yallabai,duk da ban iya karatu ba amma zan iya gane harufan da zan jera” miqa masa littattafan yayi tare da cewa
“Ka taimakeni kuwa abdullahi domin ina da abubuwan yi da yawa” abdullahi juyawa yayi ya nufi inda suke ajiye litattafan su,da sauri ya ajiye wanda ya shigo dasu ya fara dudduba sauran wanda suke wajen cikin sauri domin kada wani ya shigo ya tarar da shi yana bincike,magana kawai yaji a kanshi
“Sannu da aiki ko?” A razane ya dago kanshi,jaleel yace
“A ah kada ka damu,cigaba da abinda kake yi,nima ai ka taimakeni a baya ko?” hannu jaleel ya kai kan littafin da abdullahi ya bude,a fili ya karanta
“LABARIN BAYIN DA SUKAYIWA MASU KUDIN QASA KISAN GILLA” ya kalli abdullahi
“Lallai kana karanta labari mai qayatarwa”
“Karatu kuma? Ta yaya zanyi hakan? Nazo mayar da wasu litattafai ne kuma na kasa gane inda zan ajiye su” cewar abdullahi,murmushi jaleel yayi tare da cewa
“Kaine Gwani wajen iya faɗa,kuma mai ɓoyayyen tarihi,lallai kana buqatar ka ɓoye ko waye kai,ba zan cewa kowa naga kana karatu ba tunda ka nuna musu baka iya ba” Cike da razani abdullahi yake kallonshi,baice komai ba jaleel ya qara cewa yana miqa masa littafin
“Karɓi ka cigaba da karatun ka,ni na tafi,yi karatun ka kaji?” Cikin sanyin jiki abdullahi ya karbi littafin shi kuma jaleel ya fita.
A daren ranar bayan an gama walima an ci an sha an gama komai,shukra tana ta tattara komai nata domin tafiya gobe da safe,sameer ne da manager a tsaye suna kallonta,ta dago ta kalli sameer tare da miqo masa wani
“Yallabai ga wannan,shayinka ne domin yawan murar da kakeyi,ka kula sosai tunda kaga yanzu bana nan” tsayawa yayi yana kallonta,shi bai karba ba,kuma bai ce mata komai ba,hawaye ne suka cika mai ido,manager ne ya kalle shi
“Sameer menene haka?” Cikin sanyin murya sameer yace
“Sai yanzu na yadda lallai shukra tafiya zatayi ta barmu” manager ne ya harare shi
“Kamar wacce zata tafi nisan duniya? Naga dai inda zata je ma duk cikin masarautar nan ne” manager ya fada shima idonshi yana cika da qwalla,sameer ne yace
“Duk da ba barin masarautar zatayi ba,amma a nan bureu of music kamar dangi daya muke,tana tafiya kuwa ganinta ma wahala zaiyi mana” ya qaraso daidai lokacin da hawayen da yake boyewa ya sauko kan fuskarsa,shukra shiru tayi itama zuciyarta ta karye sosai,manager ne ya dauko algaitar da ta taba busawa har mai martaba yaji kidan ya miqa mata
“Ki tafi da wannan,kinga shikenan ba zan dinga yi miki fada ba don kina amfani dashi” hannu tasa ta karba a hankali,itama hawaye yana zubo mata,ba tare da ta ce musu komai ba ta fita daga wajen ta nufi waje,zama dukkansu sukayi akan kujera kowa yana kuka sosai kamar yara.
Zuwa tayi ta zauna a bakin dakin ajiyar kaya,tana shafa algaitar nan tana tunawa da yayanta,wanda a da royal musician ne kafin a kashe su shi da babanta,a hankali ta bude bakinta ta fara magana tana kallon taurari a sama
“Abbana yau zan bar bureu of music”
“Zan shiga cikin office of investigation “
“Duk da ina tsoron abinda zanje in tarar,amma zan gwada”
“Kana fada min cewar zama lowborn ba’a haihuwa ko dukiya bane”
“Idan zuciyata ta zama mai kyau,hakan yana nufin nima highborn ce”
“Ina kewarku kai da yayana”
Ta qarasa hawaye yana zubowa a idonta,haka ta raba dare a zaune a wajen kafin taje ta kwanta tayi bacci.
Washegari da safe,ladies investigators ne a jere kan layin assembly,yayinda chief sumayya take zagayawa tana duban tsafta ranta a matuqar bace,dai dai kan aliya har ta wuce,ta dawo baya,wani zare ne a gaban rigarta,chief sumayya tasa hannu ta zaro zaren tare da yarwa a qasa,tace
“Zare ya kunce a gaban rigarta,qarin night duty guda 3 ga aliya” nadeeya da take binta a baya ce ta rubuta abinda ta fada suka cigaba da zagayawa,sameerah ce tazo ta gabansu tare da cewa
“My lady,slave girl dinnan ta qaraso” bacin ran dake fuskar sumayya ne ya qaru
“Je ki taho da ita” juyawa sameerah tayi suka taho tare da shukra,shukra cike da girmamawa ta rusunar da kanta tana gaishe su,sai dai babu wanda ya amsa mata,’yan kan assembly kuwa duk suka bita da harara suna takaicin yanzu matsayinsu daya da wannan,sumayya ce ta kalli nadeeya
“Ki tafi da ita,ayi mata abinda ya kamata“
“Yes my lady” nadeeya tace tare da yin gaba,shukra ta bita a baya,sun bar assembly ground din sukayi hanyar dakin kwanan su,wasu bayin wajen suka hadu dasu da suke sanye da kaya irin na shukra,nadeeya ta tsayar dasu
“Ki bisu su baki uniform kuma su nuna miki dakin ki”
“Yes my lady” su shukra suka amsa ita da bayin guda biyu.
Shukra ta shirya tsaf cikin uniform dinta,navy blue din skirt da pink din riga,sai headband mai kyau da tambarin office of investigation a kai,a gaban madubi take tana kallon kanta tace
“Yanzu ni palace maid ce” tana ta murmushi,slave girl din da ta kawo ta ce ta shigo,tace
“My lady kin gama?”
Shukra ta kalleta,ta dan rusunar da kanta tare da cewa
“Ehh na gama” zare ido slave din tayi tare da cewa
“Ki taimaka ki daina girmamani my lady,hakan zai iya jawo min matsala” sai a lokacin shukra ta tuna ai yanzu ita za’a girmama,tace
“Toh shikenan,muje” ta fada tare da dan rusunar da kanta,slave dince a hankali tace
“Ai kin qara yi” kafin nan ta fita ta bar shukra a tsaye,a hankali ta fara magana
“Yanzu nima ya zama dole na dinga magana da bayi kai tsaye ta sigar basu umarni,kai zan iya kuwa? Wannan wani sabon yanayi ne” ta fada tana runtse ido,domin har rashin sabo da hakan ya fara damunta tun yanzu.
Tana shigowa assembly ground din kowa ya watse sai wa’yanda suke tsaye suna dan surutun su,nan aka fara nuna ta da baki suna ta binta da harara,sameerah ce ta fito daga office din sumayya tace
“Ki biyo ni muje wajen director” shukra ta dan rusunar da kanta tare da cewa
“Yes my lady” harara sameerah ta watsa mata
“Kar ki qara ce min my lady” shukra taji kunya sosai domin ita mantawa takeyi,suna tafe har office din director,suna shiga ta gaishe da kowa a wajen ta samu waje ta tsaya,director ce ta kalleta
“Yanzu ya kamata kisan cewar ke ba lowborn bace,lady investigator ce,kuma hakan yana nufin qarin girma,mutunci,da girmamawa,ki bi dukkan dokokin mu domin zama lapia”
Rusunar da kanta tayi
“Yes my lady” shukra ta fada,director ta kalli sameerah
“Ku tafi da ita” sameerah ce tayi gaba shukra ta qara binta har office din da sauran ladies din suke zaune,suna shigowa kowa ya bisu da kallo,shukra ce gaishesu duk suka qi amsawa,nan da nan suka fara ficewa daya bayan daya har ya rage daga ita sai Afrah,cikin nutsuwa ta kalleta
“Kada ki sa rai akwai wanda zai miki kirki a cikinmu,kuma kada ki zata wai don kina ‘yar talakawa ne,a ‘ah sai dai kawai dukkanmu muna jin takaicin yadda kika kama qafa da masu mulki domin zuwa inda yafi qarfin ki” tana gama fada mata haka itama ta fice ta barta,nadeeya ce ta shigo,ganin yadda kowa ya fito tasan saboda zuwan shukra ne,dafa kafadar shukra tayi
“Kada kiga laifin ‘yan matan nan,dukkansu tun suna qanana ake kawo su domin sai sun samu aqalla shekara goma suna training na shan wahala kafin su samu irin matsayin da kike kai yanzu,shiyasa suke jin haushi domin suna ganin ke kinzo a bagas ne,kuma matuqar baki gamsar da kowa cewar kin cancanta ba,babu wanda zai daukeki da muhimmanci” murmushi shukra tayi
“Nagode my lady,ke kadai kika fada min abu mai dadi,kuma nayi alqawarin zanyi qoqarin gamsar da kowa cewar na cancanta.
“Yallabai wannan na menene?” Kafin manager ya bata amsa sameer yace
“haba shukra,ba kya gani walima zamuyi” da sauri ya rufe bakinsa, “ina nufin my lady” juyawa tai ta kalli manager hawaye ya cika a idonta,jinjina mata kai yayi cike da farin ciki shima idonshi ya cika da ruwa,wataqila wannan shine zamansu na qarshe don zata bar wajen kenan har abada,haka suka zazzauna kowa ya fara cin abinci,kowa cikin farin ciki gwanin sha’awa.
A police bureu suma IG ne sai lieutenant da assistant suke hirar shukra,a lokacin ne ake hirar yadda aka kai mata official decree of appointment harda cikakken sunanta Shukra Anas malak,jin haka yasa IG fadawa tunani shekaru takwas da suka wuce,kamar yasan wata qaramar yarinya mai irin wannan sunan,amma ita waccan SHUKRIYYA ANAS MALAK ne sunanta,ya kwashe shekaru kusan hudu yana nemanta daga baya ya haqura,amma ya za’a yi ta kasance a cikin masarauta,kuma baiwa? maganar assistant lieutenant ce ta katse masa tunaninsa
“Yallabai,kana da baqo a waje,wani shashashan yaro yazo nemanka”
Tashi IG yayi tare da fitowa waje domin ganin me neman shi,tsayawa yayi yana kallon yadda jaleel yake shashanci da masu gadin wajen cikin uniform dinshi na ‘yan sanda,da rank din lieutenant,har bai ma kula da isowarshi wajen ba,cikin rashin daraja suka gaisa,IG ya bashi warning akan cewar idan yana da hankali da iya aiki zasu zauna lapia domin an kawo shi ne ba akan qa’ida ba,alfarmar minister of tribunal ne,kuma matsayin lieutenant aka bashi daga sama,IG ne ya kalli assistant lieutenant yace
“Ya fika matsayi a rank amma ka fishi matsayi a sanin makamar aiki,saboda haka ka kula da training dinshi” yana gama fadar haka yayi gaba ya barsu,assistant lieutenant yana yiwa jaleel magana amma ko kula shi baiyi ba ya fara tafiya yana zagaye wajen,abdullahi ne ya bullo shi da wani dan sanda da littattafai a hannunsa,abdullahi cikin girmamawa yace
“Yallabai ko zaka bani litattafan sai naje na ajiyesu a inda ake ajiyewa” kallon abdullahi yayi yace
“Zaka iya jerasu kuwa?” Dariya yayyi
“Zan iya yallabai,duk da ban iya karatu ba amma zan iya gane harufan da zan jera” miqa masa littattafan yayi tare da cewa
“Ka taimakeni kuwa abdullahi domin ina da abubuwan yi da yawa” abdullahi juyawa yayi ya nufi inda suke ajiye litattafan su,da sauri ya ajiye wanda ya shigo dasu ya fara dudduba sauran wanda suke wajen cikin sauri domin kada wani ya shigo ya tarar da shi yana bincike,magana kawai yaji a kanshi
“Sannu da aiki ko?” A razane ya dago kanshi,jaleel yace
“A ah kada ka damu,cigaba da abinda kake yi,nima ai ka taimakeni a baya ko?” hannu jaleel ya kai kan littafin da abdullahi ya bude,a fili ya karanta
“LABARIN BAYIN DA SUKAYIWA MASU KUDIN QASA KISAN GILLA” ya kalli abdullahi
“Lallai kana karanta labari mai qayatarwa”
“Karatu kuma? Ta yaya zanyi hakan? Nazo mayar da wasu litattafai ne kuma na kasa gane inda zan ajiye su” cewar abdullahi,murmushi jaleel yayi tare da cewa
“Kaine Gwani wajen iya faɗa,kuma mai ɓoyayyen tarihi,lallai kana buqatar ka ɓoye ko waye kai,ba zan cewa kowa naga kana karatu ba tunda ka nuna musu baka iya ba” Cike da razani abdullahi yake kallonshi,baice komai ba jaleel ya qara cewa yana miqa masa littafin
“Karɓi ka cigaba da karatun ka,ni na tafi,yi karatun ka kaji?” Cikin sanyin jiki abdullahi ya karbi littafin shi kuma jaleel ya fita.
A daren ranar bayan an gama walima an ci an sha an gama komai,shukra tana ta tattara komai nata domin tafiya gobe da safe,sameer ne da manager a tsaye suna kallonta,ta dago ta kalli sameer tare da miqo masa wani
“Yallabai ga wannan,shayinka ne domin yawan murar da kakeyi,ka kula sosai tunda kaga yanzu bana nan” tsayawa yayi yana kallonta,shi bai karba ba,kuma bai ce mata komai ba,hawaye ne suka cika mai ido,manager ne ya kalle shi
“Sameer menene haka?” Cikin sanyin murya sameer yace
“Sai yanzu na yadda lallai shukra tafiya zatayi ta barmu” manager ne ya harare shi
“Kamar wacce zata tafi nisan duniya? Naga dai inda zata je ma duk cikin masarautar nan ne” manager ya fada shima idonshi yana cika da qwalla,sameer ne yace
“Duk da ba barin masarautar zatayi ba,amma a nan bureu of music kamar dangi daya muke,tana tafiya kuwa ganinta ma wahala zaiyi mana” ya qaraso daidai lokacin da hawayen da yake boyewa ya sauko kan fuskarsa,shukra shiru tayi itama zuciyarta ta karye sosai,manager ne ya dauko algaitar da ta taba busawa har mai martaba yaji kidan ya miqa mata
“Ki tafi da wannan,kinga shikenan ba zan dinga yi miki fada ba don kina amfani dashi” hannu tasa ta karba a hankali,itama hawaye yana zubo mata,ba tare da ta ce musu komai ba ta fita daga wajen ta nufi waje,zama dukkansu sukayi akan kujera kowa yana kuka sosai kamar yara.
Zuwa tayi ta zauna a bakin dakin ajiyar kaya,tana shafa algaitar nan tana tunawa da yayanta,wanda a da royal musician ne kafin a kashe su shi da babanta,a hankali ta bude bakinta ta fara magana tana kallon taurari a sama
“Abbana yau zan bar bureu of music”
“Zan shiga cikin office of investigation “
“Duk da ina tsoron abinda zanje in tarar,amma zan gwada”
“Kana fada min cewar zama lowborn ba’a haihuwa ko dukiya bane”
“Idan zuciyata ta zama mai kyau,hakan yana nufin nima highborn ce”
“Ina kewarku kai da yayana”
Ta qarasa hawaye yana zubowa a idonta,haka ta raba dare a zaune a wajen kafin taje ta kwanta tayi bacci.
Washegari da safe,ladies investigators ne a jere kan layin assembly,yayinda chief sumayya take zagayawa tana duban tsafta ranta a matuqar bace,dai dai kan aliya har ta wuce,ta dawo baya,wani zare ne a gaban rigarta,chief sumayya tasa hannu ta zaro zaren tare da yarwa a qasa,tace
“Zare ya kunce a gaban rigarta,qarin night duty guda 3 ga aliya” nadeeya da take binta a baya ce ta rubuta abinda ta fada suka cigaba da zagayawa,sameerah ce tazo ta gabansu tare da cewa
“My lady,slave girl dinnan ta qaraso” bacin ran dake fuskar sumayya ne ya qaru
“Je ki taho da ita” juyawa sameerah tayi suka taho tare da shukra,shukra cike da girmamawa ta rusunar da kanta tana gaishe su,sai dai babu wanda ya amsa mata,’yan kan assembly kuwa duk suka bita da harara suna takaicin yanzu matsayinsu daya da wannan,sumayya ce ta kalli nadeeya
“Ki tafi da ita,ayi mata abinda ya kamata“
“Yes my lady” nadeeya tace tare da yin gaba,shukra ta bita a baya,sun bar assembly ground din sukayi hanyar dakin kwanan su,wasu bayin wajen suka hadu dasu da suke sanye da kaya irin na shukra,nadeeya ta tsayar dasu
“Ki bisu su baki uniform kuma su nuna miki dakin ki”
“Yes my lady” su shukra suka amsa ita da bayin guda biyu.
Shukra ta shirya tsaf cikin uniform dinta,navy blue din skirt da pink din riga,sai headband mai kyau da tambarin office of investigation a kai,a gaban madubi take tana kallon kanta tace
“Yanzu ni palace maid ce” tana ta murmushi,slave girl din da ta kawo ta ce ta shigo,tace
“My lady kin gama?”
Shukra ta kalleta,ta dan rusunar da kanta tare da cewa
“Ehh na gama” zare ido slave din tayi tare da cewa
“Ki taimaka ki daina girmamani my lady,hakan zai iya jawo min matsala” sai a lokacin shukra ta tuna ai yanzu ita za’a girmama,tace
“Toh shikenan,muje” ta fada tare da dan rusunar da kanta,slave dince a hankali tace
“Ai kin qara yi” kafin nan ta fita ta bar shukra a tsaye,a hankali ta fara magana
“Yanzu nima ya zama dole na dinga magana da bayi kai tsaye ta sigar basu umarni,kai zan iya kuwa? Wannan wani sabon yanayi ne” ta fada tana runtse ido,domin har rashin sabo da hakan ya fara damunta tun yanzu.
Tana shigowa assembly ground din kowa ya watse sai wa’yanda suke tsaye suna dan surutun su,nan aka fara nuna ta da baki suna ta binta da harara,sameerah ce ta fito daga office din sumayya tace
“Ki biyo ni muje wajen director” shukra ta dan rusunar da kanta tare da cewa
“Yes my lady” harara sameerah ta watsa mata
“Kar ki qara ce min my lady” shukra taji kunya sosai domin ita mantawa takeyi,suna tafe har office din director,suna shiga ta gaishe da kowa a wajen ta samu waje ta tsaya,director ce ta kalleta
“Yanzu ya kamata kisan cewar ke ba lowborn bace,lady investigator ce,kuma hakan yana nufin qarin girma,mutunci,da girmamawa,ki bi dukkan dokokin mu domin zama lapia”
Rusunar da kanta tayi
“Yes my lady” shukra ta fada,director ta kalli sameerah
“Ku tafi da ita” sameerah ce tayi gaba shukra ta qara binta har office din da sauran ladies din suke zaune,suna shigowa kowa ya bisu da kallo,shukra ce gaishesu duk suka qi amsawa,nan da nan suka fara ficewa daya bayan daya har ya rage daga ita sai Afrah,cikin nutsuwa ta kalleta
“Kada ki sa rai akwai wanda zai miki kirki a cikinmu,kuma kada ki zata wai don kina ‘yar talakawa ne,a ‘ah sai dai kawai dukkanmu muna jin takaicin yadda kika kama qafa da masu mulki domin zuwa inda yafi qarfin ki” tana gama fada mata haka itama ta fice ta barta,nadeeya ce ta shigo,ganin yadda kowa ya fito tasan saboda zuwan shukra ne,dafa kafadar shukra tayi
“Kada kiga laifin ‘yan matan nan,dukkansu tun suna qanana ake kawo su domin sai sun samu aqalla shekara goma suna training na shan wahala kafin su samu irin matsayin da kike kai yanzu,shiyasa suke jin haushi domin suna ganin ke kinzo a bagas ne,kuma matuqar baki gamsar da kowa cewar kin cancanta ba,babu wanda zai daukeki da muhimmanci” murmushi shukra tayi
“Nagode my lady,ke kadai kika fada min abu mai dadi,kuma nayi alqawarin zanyi qoqarin gamsar da kowa cewar na cancanta.