← Book details Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 34

Sashe 20

Royal Consort Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Lady jalila a quaters dinta tana zaune har yanzu kana ganinta zaka san irin farin cikin da take ciki,don murmushi ne shimfide akan fuskarta,chief maid dinta da take zaune tana fuskantar ta tace
“Amma my lady,shin meyasa zaki zabi yiwa shukra irin wannan tukwuicin?” Murmushin fuskarta ne ya qaru
“Matuqar dai mai martaba ya amince,to kamar anyi an gama ne”
Rusunar da kai chief maid din tayi
“Your highness nasan shukra yarinya ce ‘yar baiwa mai kuma basira,amma yin hakan zai jawo cece kuce a masarautar nan domin abu ne wanda ba’a taba yin shi ba”
Fuskar lady jalila ta canja nan take ta kalli chief maid dinta
“Wannan ba hurumin da zaki fadi ra’ayinki bane,don haka ki iya bakin ki” rusunar da kanta tayi ba tare da ta qara cewa komai ba,lady jalila ce ta qara cewa
“Ya labarin yayana?”
“Mun samu labarin ya baro qasar china ta jirgin ruwa,zuwa gobe zai qaraso cikin garin nan” cewar chief maid
Lady jalila da murmushin fuskarta ya dawo tace
“Na matsu ya dawo na nuna masa shukra,yana da baiwar gane halayen mutane,ban san me tunaninshi zai bashi a kanta ba” ta qarasa cikin tsantsar farin ciki,domin a halin yanzu ji take kamar shukra ta zama wani bangare na jikinta.

Washegari da safe,a can cikin gari sameer ne a tsaye kamar mai jiran wani abu yana ta kai kawo a qofar wani gida,yana magana shi kadai
“Wannan mutumin ba zai zo bane? Kada fa a kawo abincin ina nan,gashi nan yau saboda shi nazo gida na kwana ban kwana a bureu of music ba” yana ta maganganun shi shi kadai,ji yayi daga bayansa ance
“Barka da safiya” da sauri ya juyo,bai damu da amsa gaisuwar ba yace
“Kaine wanda zaka kama haya?”
“Ehh nine” cewar abdullahi,sabon mai binciken gawa da ka akawo police bureu (corpse handler)
Sameer ne kawai yayi gaba tare da shigewa cikin gidan,shima abdullahi ya bishi a baya,wani daki suka nufa,sai da suka shiga sameer ya kalli abdullahi
“Kaga dakin nan,duk garin nan bazaka samu daki mai kyaun wannan ba da irin kudin da zaka biya,kuma ka kula sosai bana son qazanta kaga ni ba zama nake ba domin ni royal musician ne kamar yadda kake gani” ya qarasa yana mai nunawa abdullahi uniform din dake jikinshi,jinjina kai abdullahi yayi baice komai ba har sameer ya gama surutunsa mara kan gado ya fita daga dakin,ajiyar zuciya abdullahi ya sauke tare da cewa
“Me yasa zan fado hannun royal musician da zai dinga tuna min da Abdulshakur?” Saurin kawar da tunanin yayi tare da fara kunce kayan da ya shigo dasu yana ajiyewa domin ya huta kafin ya tafi wajen aiki.

Sameer yana fitowa qofar gida zai tafi masarauta,wani saurayi da ba zai wuce shekarunsa ba yayo kwana da gudu ya bangajeshi,yana huci saboda gudun da yasha yacewa sameer
“Ka taimakeni dn Allah,ka taimakeni” sameer ya saki baki yana kallon ikon Allah,kafin ya ankara ya ciro kudi masu yawa ya sa a hannun sameer,tare da shigewa cikin gidan neman wajen buya,shigarsa ke da wuya wasu mutane suka qaraso suka kalli sameer
“Kai kaga wani saurayi yanzunnan? Ni ina da tabbacin ma gidannan ya shiga”
Da sauri sameer yace
“Bai shiga nan ba,ni banga kowa ba”
Naushi mutumin ya kawowa sameer,sameer ya goce nan da nan tsoro ya shige shi,kamar daga sama suka ji ance
“Kai dakata” suna juyawa abdullahi ne yaji hayaniya ya fito,ya qaraso wajen yayinda sameer yayi saurin matsawa,abdullahi ne sukai fada da mutanen har suka gudu suna fadin
“Yaya za’ayi mutun yayiwa matata fyade kuma yasa ayi mana duka” haka dai suka tafi,ganin yadda abdullahi ya iya fada sosai yasa sameer ya sha jinin jikinshi.
Saurayin da ya buya ne jin anyi wa mutanen duka ya fito daga inda yake,Yayan lady jalila ne.

Kafin yaje gida har labarin abinda ya aikata yaje kunnen mahaifiyar shi da kuma mariqin Jalila,minister na tribunal,jameel da yake zaune a gaban mahaifinshi yace
“Abba idan har jaleel zaiyi amfani da matsayin ‘yaruwarsa ya dinga irin wannan abin lallai hakan zai zamar mana matsala” jinjina kai baban yayi tare da cewa
“Duk da hakan zuwan nashi yana da amfani don haka ka nema masa matsayin da zai dace da shi”
“Yehhh aboujii” (yes father) jameel ya fada tare da tashi ya bar wajen.

Jaleel yana isa gida haj jameela tayi mai ta tas akan abinda akace ya aikata,bayan ta gama yi mai fada har suka gangaro kan hirar shukra da abinda tayi wa jalila na bajinta,haj jameela ce tace,
“Kaje kana bin matan mutane,ga yarinyar nan jalila tace zata aiko ta yau”
Da sauri yace
“ita slave girl din? Zata zo gidan nan yau?” Kafin ma haj jameela ta bashi amsa suka jiyo tana sallama,fitowa sukayi dukkansu tsakar gida,kallon tsanaki jaleel yakeyi mata ba tare da yace mata komai ba ya kama hanyar sa ya fice domin tafiya ganin ‘yar uwarsa,ita kuma shukra ta bada saqon da zata bayar ta tafi.

Shigowar jaleel cikin masarautar kai tsaye quaters din lady jalila ya nufa,jin labarin isowarshi yasa ta fitowa har da dan gudun ta ta sameshi cikin matuqar farin ciki tace
“Orabeuni” (elder brother in ancient korean language) shima murmushi ne a kan fuskar shi,ya rusunar da kanshi tare da cewa
“Your highness” dariya tasa sosai har haqoranta suka fito,shima dariyar yayi tare da binta suka shiga sitroom din ta.
Zama sukayi kamar yadda yanayin zaman masarautar take,tana zaune ta nade qafarta a qasa kan abin zamanta yayinda shikuma yake zaune yana fuskantar ta da qaramin tebur din da ya raba tsakaninsu,cikin farin ciki tace
“Yanzu yaya meyasa daga dawowarka har ka fara jawo magana,maimakon ace ka nutsu sosai?”
Murmushi yayi “ke yarinya ce,ai nafi son kowa ya dinga ganin kamar ni wawa ne kuma soko,shashasha yadda ba za’a dinga sa min ido ba akan duk wani abinda zan aikata,kowa zaiyi tunanin bani da hankali ai” cewar jaleel,murmushi jalila tayi tare da cewa
“Hakane,lallai wannan shine lokacin da muke ta jira kuma gashi yazo” kallonta yayi cikin rashin fahimta,ganin haka ta cigaba
“Ka manta alqawarin da na daukarwa kaina ranar da na fara shigowa masarautar nan? Nayi alqawarin sai na kai qololuwar matsayi a cikinta,kuma yanzu lokacin zama muna kallo ya qare,saboda haka na samu wata yarinya mai tsantsar basira da hankali kuma mai iya riqe sirri,ina ganin zata yi mana amfani sosai,Ina ta Allah Allah ka dawo domin na nuna maka ita,ban san me zaka ce a kanta ba”
Da sauri yace
“Ko dai yarinyar nan ta bureu of music?”
“Har kaji labarin ta?” Cewar lady jalila
“Ehh ba labarinta ba,na ganta ma”
Da sauri jalila tace
“Yauwa fada min toh,ya kake gani?”
Shiru yayi ba tare da yace komai ba,tambayar shi ta qara yi,nan ma yai mata shiru,nan take ta sha jinin jikinta,cikin damuwa tace
“Yaya ka fada min me kayi tunani game da ita?”
Dago kanshi yayi ya kalleta
“Na tabbata yarinyar ‘yar baiwa ce,kuma da basira amma hakan ne dalilin da zaisa ki guji janyo ta jikin ki” da sauri jalila tace “saboda me?”
Sauke ajiyar zuciya yayi
“Saboda yarinyar tana abubuwa masu kama da irin naki,lowborn ce kamarki,wacce tunaninta,hankalinta,da kuma basirarta yafi qarfin matsayin rayuwarta kamar yadda kema daga haka kika fara,kuma har kika kawo zuwa wannan matsayin,shin me zaisa ita ki bata fiffiken da zai sa ta tashi sama?”
Shiru lady jalila tayi tana tunanin maganar yayanta,amma ita sam bata tunanin hakan zai iya zamar mata matsala.

Mai martaba ne zaune a grand palace yayi zurfi cikin tunani,ba komai yake tunawa ba sai maganar da sukayi da lady jalila,yana tuna lokacin da lady jalila take ce masa
“Mai martaba ina son ka bawa shukra damar da zatayi amfani da basirar da Allah ya bata kuma mutanen qasarmu ma su amfana da hakan,ina son kayi mata tukwuici daidai da abinda tayi “ da yaga tunanin ya ishe shi haka,ya tashi ya canja kaya domin fita cikin gari ko hakan zai rage masa yawan tunani,kuma ya tsayar da matsaya game da shukra.
Chapter 20 · 0% Book details