Sashe 7
Rayuwar Rayhana Part 4 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Duk da cewa halayen basu canza ba, zuciyarshi ta yi laushin da bata da shi a baya, mijin da ko kyakkyawar surar jikinsa ta kalla kullum, ya ishi zuciyarta ta kasance cike da wadatar zuci, da godiyar Ubangiji. Ta kuma yi alfahari da zamantowarsa barin rayuwarta, kuma uban ‘ya’yanta.
Wadda ta fi kowacce mace a duniya samun alfarmarsa, har kuwa da uwar da ta haife shi sai dai a ba ta matsayinta na UWA a bar neman albarka, amma ba za ta taka wannan matsayin ba.
In haka ne bai kamata ta ji haushi, tsoro ko nuna gazawa a kan hakkinsa da Allah ya rataya a wuyanta ba. Har ta yi sake da wannan damar da Allah ya bata, wasu ‘yan iska a waje su kwace.
Masu iya magana suka ce, wai tsalle daya shi ke jefa mutum rijiya, abin nufi a nan, tun a lokaci na farko ta nuna gazawa wanda hakan zai sa ya yi baya-baya da ita don gudun bacin ranta ko bacin zuciyarta.
Ya soma tunanin hanyar da zai bi ya dinke barakar ta, wadda ba komai ba ce illa ya nemo wata, wadda za ta jurewa jarumtakarsa a auratayya.
Wannan tunanin da Rayhanah ta yi, ba wani ne ya koya mata ba, ba karantawa ta yi ba. Tsinkayen hankali ne kawai (foresight ).
An ce wai idan baka iya kuka ba, to iyayenka ne ba su mutu ba. Baki iya goyo ba saboda yana da wahala kuma zubewar aji ne, to baki haihu bane. Ko kece ‘yar Karuna in dai Bahaushiya ce ke, kuma cikakkiyar ‘yar kasar Nigeria.
Shirun da Rayhanah ta yi, da kukan da ta daina lokaci daya kamar daukewar ruwan sama, shi ya ba Doctor Takai, damar kara mamayarta (Needing for more…....).
Amma ga mamakinsa wannan karon bata nuna razana ba, shi din ne ya tuna da dinkin da ya yi mata ya hakura, amma fa ya kasa hakura da abin da ya fi so daga wadannan ‘luscious lips’ na Rayhanah, shi din ya ci gaba da yi cikin wani irin salo da Rahane ta kasa juyawa baya, lallashi da banbadanci har da hawayen neman afuwa, abinda ya gigita Rayhanah…. Ya Himu ne? (She is still doubting).
Alkawarirrikan da yake daukar mata ta san ba a hayyacinsa yake fadarsu ba, don haka ba ta kama ko daya ba.
Ba ta san lokacin da hannuwanta suka yi fitar bazata ba suka rungume Ibraheem, rungumar da bata taba yiwa wani abu a rayuwarta ba, bayan gawar mahaifinta.
Ga mamakin Ibrahim Rayhanah ta soma taya shi sumbar cikin nata salon mai bin umarnin zuciya da odar gangar jiki. Ta sakar mishi komai, ta yarda in mutuwa za ta yi ta mutun, in dai a kan farin cikin Ibrahim ne.
Shi din ne ya yi jarumtakar cewa,
“A’ah…Rayhanah ”
Yana yin baya-baya da ita kada cin zalin ya yi yawa. Ita kuma cikin kara iza shi take da tana fadin….
“Ba sai a kara dinkewa ba???”
Duk da halin da Ibraheem ke ciki bai fasa yin dariya ba saboda farin cikin da ya lullube shi. A kalla yau ya tabbatar Rayhanah na son sa, son da ba ta yiwa Khalipha.
Kalami ta yi cikin jin kan mace ga mijinta ba bisa tursasawa ba ko son fita hakkinsa, a’a, don tana sonsa. Tana son farin cikinsa fiyeda nata. Sai ya kwaikwayi ‘yar muryarta cikin dariya ya ce,
“A sake dinkewa don kin zama kwarya??????”
*****
Cikin wannan rayuwar da ta fi kowacce dadi da gardi ga kowanne dan Adam, Ibraheem da Rayhanah suka ci gaba da rayuwa a Chicago. Suna waya da Daddy da Inna Juma a kai a kai, shima Ibrahim yana gaisawa da mahaifiyarsa da Yaya Khalipha, sai dai bai taba yi mata zancen aurensa ko zancen Rayhanah ba, don Daddy ya gargade shi da kakkausan harshe da yin hakan.
An debi watanni biyar, duk abin da ya kawo shi ya kammala shi, ya auna komai da ya mallaka a Chicago bankunan gida Nigeria, wasu kuma daga ciki shipping dinsu yayi kamar motoci da furnitures da yake son kawata gidansa dasu.
Gidansa kawai ya bari bai kadar ba. A zuciyarsa ya ajiye shi ne ga first born din da duk Allah ya ba shi, mace ko namiji. Su zo su zauna ciki suyi karatu, in sunyi aure su zauna da iyalinsu.
Idan asibiti zai shiga, tare suke shiga, idan University of Chicago zai shiga yi lecturing, zama take cikin daliban ayi laccar da ita.
Ko tsura masa ido wata a cikin daliban ta yi, ta fara auna mata harara kenen. Ta hanashi motsin kirki ko doguwar hira yake yi a waya sai ta ce zance yake yi. Haka suke yawo cikin Illinois hannayensu sarke da juna.
Idan theatre za su shiga, Rayhanah na ofishinsa tana jiransa, shi Ibrahim maimakon ya ji haushi kamar yadda sauran maza ke ji in matansu na musu hakan, shi dadi yake ji. Domin ta rabashi da karnukan dake farautarsa, ko wata mu’amala ce ta hada shi da matan asibitin ko dalibansa, tana gefe sarke da hannu a kirji kafafu a sarke, tana dakon mai kawo wargi.
Ga Turawa da shegen tsoro basa son tashin hankali, ta fi ganin maita a kan Ibrahim daga mutanenmu mazauna can.
Mutum daya ta tsaya mata a rai dake yawan yi masa waya kuma su dade suna hira wai ita Sapna, bai taba ignoring kiranta ba, amma a cewarsa dalibarsa ce.
Kuma duk sanda ta binciki wayarsa babu hoto. Don haka take addu’ar Allah yasa wata rana idonta ya ga idon wannan Sapnar, sai yau Litinin a wani marece Allah ya amsa addu’arta.
******
Ibrahim na dakin ganawa da (Chief Medical Director) na Illinois TH, tare da manyan likitocin koda na duniya, tattaunawa ake yi a kan cutar (sars) tare da wakilan kungiyoyin AAPS, NAD, AMA, da Alberta. Ibrahim ya mike yana magana ta cikin ‘yar na’urar daukaka sauti dake makale jikin farar rigarsa ta likitoci, can karkashin rigar bakaken suit ne wuyanshi daure da bakin tie din da Rahane ta daura masa.
A lokacin ita Rayhanah tana can ofishinsa tana tsimayinsa, ya hadata da typing din wani record da yake son fitarwa a kan cutar ta sars, ba tare da sallama ba ko neman izinin sakatariya ko danna knocking na neman izini, wata farar yarinya kyakkyawa (ko da yake ba za a kira ta yarinya ba, domin a kalla tana da ashirin da takwas), ta murdo kofar ofishin ta shigo.
Kallon-Kallo ake tsakanin Rayhanah diyar Malam Rashidu Takai da diyar Ambasada Kabiru Abubakar Dogon-Daji. Rahanen, glasses ne prada a idanunta mai duhu wanda ya boye kwayar idonta. Tana sanye cikin traditional attire dinta atamfa ‘yar Holland koriya shar, yafe da mayafin da ya shiga da adon atamfar wato yellow, a kafafunta takalmi ne mai tsayin dunduniya sosai (heel shoe) shima yellow, babu kwalliyar komai a fuskarta sai ruwan hodar mary-kay sai lebbanta dake kyallin lip-balm mai danko.
Ita ma Sapnan ba wata kwalliya ta yi ba amma kallo daya za ka yi mata ka kirata da sunaye uku; ‘yar gata, ‘yar hutu, yar gayu.
Shadda ce getzner dinkin Senegal a jikinta dark pink wadda ba a cika zare da yawa wajen yin sirfaninta ba, wanda aka yi shi da zare light pink, haka dan shara-shara gyalen da ta zarga a wuyanta shima light pink din ne, sai babbar jaka ta mata baka mahadin takalmi flat baki da ke kafarta samfurin (gucci).
Haka suka ci gaba da kallon juna kowacce ba ta yi magana ba, amma ta soma huci, hancina sun bubbude kowanne tsiron gashi ya mike sai Allah ya jeho Ibrahim gabanin a fara baiwa hammata iska.
Wadda ta fi kowacce mace a duniya samun alfarmarsa, har kuwa da uwar da ta haife shi sai dai a ba ta matsayinta na UWA a bar neman albarka, amma ba za ta taka wannan matsayin ba.
In haka ne bai kamata ta ji haushi, tsoro ko nuna gazawa a kan hakkinsa da Allah ya rataya a wuyanta ba. Har ta yi sake da wannan damar da Allah ya bata, wasu ‘yan iska a waje su kwace.
Masu iya magana suka ce, wai tsalle daya shi ke jefa mutum rijiya, abin nufi a nan, tun a lokaci na farko ta nuna gazawa wanda hakan zai sa ya yi baya-baya da ita don gudun bacin ranta ko bacin zuciyarta.
Ya soma tunanin hanyar da zai bi ya dinke barakar ta, wadda ba komai ba ce illa ya nemo wata, wadda za ta jurewa jarumtakarsa a auratayya.
Wannan tunanin da Rayhanah ta yi, ba wani ne ya koya mata ba, ba karantawa ta yi ba. Tsinkayen hankali ne kawai (foresight ).
An ce wai idan baka iya kuka ba, to iyayenka ne ba su mutu ba. Baki iya goyo ba saboda yana da wahala kuma zubewar aji ne, to baki haihu bane. Ko kece ‘yar Karuna in dai Bahaushiya ce ke, kuma cikakkiyar ‘yar kasar Nigeria.
Shirun da Rayhanah ta yi, da kukan da ta daina lokaci daya kamar daukewar ruwan sama, shi ya ba Doctor Takai, damar kara mamayarta (Needing for more…....).
Amma ga mamakinsa wannan karon bata nuna razana ba, shi din ne ya tuna da dinkin da ya yi mata ya hakura, amma fa ya kasa hakura da abin da ya fi so daga wadannan ‘luscious lips’ na Rayhanah, shi din ya ci gaba da yi cikin wani irin salo da Rahane ta kasa juyawa baya, lallashi da banbadanci har da hawayen neman afuwa, abinda ya gigita Rayhanah…. Ya Himu ne? (She is still doubting).
Alkawarirrikan da yake daukar mata ta san ba a hayyacinsa yake fadarsu ba, don haka ba ta kama ko daya ba.
Ba ta san lokacin da hannuwanta suka yi fitar bazata ba suka rungume Ibraheem, rungumar da bata taba yiwa wani abu a rayuwarta ba, bayan gawar mahaifinta.
Ga mamakin Ibrahim Rayhanah ta soma taya shi sumbar cikin nata salon mai bin umarnin zuciya da odar gangar jiki. Ta sakar mishi komai, ta yarda in mutuwa za ta yi ta mutun, in dai a kan farin cikin Ibrahim ne.
Shi din ne ya yi jarumtakar cewa,
“A’ah…Rayhanah ”
Yana yin baya-baya da ita kada cin zalin ya yi yawa. Ita kuma cikin kara iza shi take da tana fadin….
“Ba sai a kara dinkewa ba???”
Duk da halin da Ibraheem ke ciki bai fasa yin dariya ba saboda farin cikin da ya lullube shi. A kalla yau ya tabbatar Rayhanah na son sa, son da ba ta yiwa Khalipha.
Kalami ta yi cikin jin kan mace ga mijinta ba bisa tursasawa ba ko son fita hakkinsa, a’a, don tana sonsa. Tana son farin cikinsa fiyeda nata. Sai ya kwaikwayi ‘yar muryarta cikin dariya ya ce,
“A sake dinkewa don kin zama kwarya??????”
*****
Cikin wannan rayuwar da ta fi kowacce dadi da gardi ga kowanne dan Adam, Ibraheem da Rayhanah suka ci gaba da rayuwa a Chicago. Suna waya da Daddy da Inna Juma a kai a kai, shima Ibrahim yana gaisawa da mahaifiyarsa da Yaya Khalipha, sai dai bai taba yi mata zancen aurensa ko zancen Rayhanah ba, don Daddy ya gargade shi da kakkausan harshe da yin hakan.
An debi watanni biyar, duk abin da ya kawo shi ya kammala shi, ya auna komai da ya mallaka a Chicago bankunan gida Nigeria, wasu kuma daga ciki shipping dinsu yayi kamar motoci da furnitures da yake son kawata gidansa dasu.
Gidansa kawai ya bari bai kadar ba. A zuciyarsa ya ajiye shi ne ga first born din da duk Allah ya ba shi, mace ko namiji. Su zo su zauna ciki suyi karatu, in sunyi aure su zauna da iyalinsu.
Idan asibiti zai shiga, tare suke shiga, idan University of Chicago zai shiga yi lecturing, zama take cikin daliban ayi laccar da ita.
Ko tsura masa ido wata a cikin daliban ta yi, ta fara auna mata harara kenen. Ta hanashi motsin kirki ko doguwar hira yake yi a waya sai ta ce zance yake yi. Haka suke yawo cikin Illinois hannayensu sarke da juna.
Idan theatre za su shiga, Rayhanah na ofishinsa tana jiransa, shi Ibrahim maimakon ya ji haushi kamar yadda sauran maza ke ji in matansu na musu hakan, shi dadi yake ji. Domin ta rabashi da karnukan dake farautarsa, ko wata mu’amala ce ta hada shi da matan asibitin ko dalibansa, tana gefe sarke da hannu a kirji kafafu a sarke, tana dakon mai kawo wargi.
Ga Turawa da shegen tsoro basa son tashin hankali, ta fi ganin maita a kan Ibrahim daga mutanenmu mazauna can.
Mutum daya ta tsaya mata a rai dake yawan yi masa waya kuma su dade suna hira wai ita Sapna, bai taba ignoring kiranta ba, amma a cewarsa dalibarsa ce.
Kuma duk sanda ta binciki wayarsa babu hoto. Don haka take addu’ar Allah yasa wata rana idonta ya ga idon wannan Sapnar, sai yau Litinin a wani marece Allah ya amsa addu’arta.
******
Ibrahim na dakin ganawa da (Chief Medical Director) na Illinois TH, tare da manyan likitocin koda na duniya, tattaunawa ake yi a kan cutar (sars) tare da wakilan kungiyoyin AAPS, NAD, AMA, da Alberta. Ibrahim ya mike yana magana ta cikin ‘yar na’urar daukaka sauti dake makale jikin farar rigarsa ta likitoci, can karkashin rigar bakaken suit ne wuyanshi daure da bakin tie din da Rahane ta daura masa.
A lokacin ita Rayhanah tana can ofishinsa tana tsimayinsa, ya hadata da typing din wani record da yake son fitarwa a kan cutar ta sars, ba tare da sallama ba ko neman izinin sakatariya ko danna knocking na neman izini, wata farar yarinya kyakkyawa (ko da yake ba za a kira ta yarinya ba, domin a kalla tana da ashirin da takwas), ta murdo kofar ofishin ta shigo.
Kallon-Kallo ake tsakanin Rayhanah diyar Malam Rashidu Takai da diyar Ambasada Kabiru Abubakar Dogon-Daji. Rahanen, glasses ne prada a idanunta mai duhu wanda ya boye kwayar idonta. Tana sanye cikin traditional attire dinta atamfa ‘yar Holland koriya shar, yafe da mayafin da ya shiga da adon atamfar wato yellow, a kafafunta takalmi ne mai tsayin dunduniya sosai (heel shoe) shima yellow, babu kwalliyar komai a fuskarta sai ruwan hodar mary-kay sai lebbanta dake kyallin lip-balm mai danko.
Ita ma Sapnan ba wata kwalliya ta yi ba amma kallo daya za ka yi mata ka kirata da sunaye uku; ‘yar gata, ‘yar hutu, yar gayu.
Shadda ce getzner dinkin Senegal a jikinta dark pink wadda ba a cika zare da yawa wajen yin sirfaninta ba, wanda aka yi shi da zare light pink, haka dan shara-shara gyalen da ta zarga a wuyanta shima light pink din ne, sai babbar jaka ta mata baka mahadin takalmi flat baki da ke kafarta samfurin (gucci).
Haka suka ci gaba da kallon juna kowacce ba ta yi magana ba, amma ta soma huci, hancina sun bubbude kowanne tsiron gashi ya mike sai Allah ya jeho Ibrahim gabanin a fara baiwa hammata iska.