← Book details Rayuwar Rayhana Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 14

Sashe 13

Rayuwar Rayhana Part 4 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Ita sam Jawahir ba ta lura da Ya Himu ba, balle karin ‘yar da falon ya samu. A lokacin ne Asma’u ta soma kuka tana zillo daga hannun Yaya Khalipha tana mikawa uwarta hannu, don ganin an shake mata ita.
Ibrahim ya ce,
“Kinga malama sakar min mata ta baiwa ‘yarta nono…..”
A firgice Jawahir ta juya don ta ji wata murya ne kamar ta Ya Himu, ta tabbatar shi din ne, ta kuma juya ga Yaya Khalipha wanda ya mikowa Rayhanah ‘yar, ta mika hannu ta karbeta.
Baki Jawahir ta bude tana kallon wani salon ba da nono na mutum biyu (uwa da uban). ‘Yar na shan nono amma uban ne ke rike da ita kamar shi zai yi breast feeding din, yana fadin,
“Kuma shi kenan don ta iya kamawa da kanta sai ki sakar mata? Salon ta yi katon baki irin na Jawahir? Hangangam!”
Jawahir ta bude baki (hangangam din kamar yadda yace) ta kuma kasa rufe shi. Sai ta kalli Rayhanah ta juya ta kalli Yayan nata, sannan ta maida idonta kan kyakkyawar jaririyar.
“Ki kwantar da hankalinki Jawahir na yi mata AURE!”
Ta tuna da kalaman Daddynsu a kan tambayar Rayhanah da ta yi. Shekaru uku da doriya a baya, ranar data wayi gari bata kara ganin Rayha a gidansu ba. Tun daga ranar kuma Daddy bai sake ba ta wata kofar da za ta yi masa zancen Rayhanah ba.
Wato Ya Himu ya aurawa!
Sai ta zube a kasa tana yiwa Ubangiji Sujjada, dama da mayafinta a kanta.
Jawahir ta fadi a ranta
“What a genius and examplary father they have?!”
“Bravo Daddy!”
Ta fada a hankali, idanunta na lumshewa. Kaunar mahaifinsu da mamakin kyakkyawar zuciya irin tasa ya cika mata zuciya. Irin su Daddy, V.C Baba Sa’idu (GIRMA YA FADI), Brigadier Bello Makarfi (SIRADIN RAYUWA), Alhaji Aliyu Dambatta (ALHERI), Tahir Usman Karaye (TUNA BAYA....), tsiraru ne a cikin al’umma.
‘Yan boko ne da basu fassara boko da defination din da sauran al’umma da dama suka fassara shi da shi ba, sun ba shi kyakkyawar fassara da ma’ana wadda ta yi dai-dai da addininsu wajen jin kan TALAKA da daukaka darajarsa ya tadda kafadar masu gata.
Sun kuma amince da ayar Ubangiji (SWT) ta
“inna akramakum indallahi atqaakum....”. Suna kuma aiki da ita. A cikin dukkan al’amuransu na rayuwar yau da kullum.
Jawahir tace
“How she wish za ta iya rubutu? Da ta bawa al’ummar Annabi labarinsu. Domin suyi koyi da kyawawan halayensu.
Ta mika hannu tana hawaye ta ce,
“Ku bani ita na dauke ta…..”
Rayhanah ta fizgeta daga nonon tana fadin
“Jeki wajen uwarki Asma’u…..”
Ai kuwa yarinya ta fasa kara, don bata koshi ba. A haka Rayhanah ta mannata a jikin Jawahir. Jawahir na daga cikin dai-daikun mutanen da ba za ta taba mantawa dasu ba cikin tarihin rahuwarta.
Ibraheem ya so ya yi bala’in an fizge masa ‘ya daga nono, amma ganin irin maternal rungumar da Jawahir ta yi mata tana shafa bayanta a hankali har ta yi shiru, ta ci gaba da dubanta cikin kauna, kwatankwacin kaunarta da dan’uwanta Ibraheem.
Sai ya fasa, ya dauke ido a kansu ya mayar ga amsa call din Daddy yana gaya masa sun sauka lafiya suna Abuja, sai gobe za su taho.
A ranar dai Baby Ma’u a jikin Jawahir ta kwana, kuma da yake ta fara cin abinci, ba ta farkawar dare. Da ta farka sau daya ta ba ta ruwa ba ta kara farkawa ba. A daren ta hada kayanta ta ce ita ma da ita za a Kanon, ba za ta iya barin ‘yarta ba.
Washegari basu bar Abuja da wuri ba sai da suka karya kumallo suka kintsa a tsanake, sannan suka dunguma dukkansu har Khalipha da nasa iyalin suka yo Kanon a jibgegiyar ‘BMW’ din Yaya Khalipha.
******
RAHANE A GIDAN DR. MANSUR
(Karo na Biyu)
Wannan karon, ta shiga ne da kafa mai kwari irin wadda Mimtaz ta shiga da ita. Ta samu karfin gwiwar hakan ne sakamakon hannunta da Ibrahim ya rike kam-kam cikin nasa har da matsa mata yatsun da karfi.
Asma’u na goye a bayan Jawahir ta yi barci tun a hanya. Shigar yamma suka yiwa Kanon, don basu taso da wuri ba. Ga tsaye-tsayen da Khalipha ya yi ta yi yana yiwa Mami cefane kamar yadda ya saba kullum zai je Kano. (Dankalin Turawa, Doya, Albasa, Kayan Miya, Manja da Plantain). Sanda suka shigo gidan, Daddy baya nan ma, amma sunyi waya ya ce yana kan hanyar dawowa ya samu emergency call ne.
Mami da Abida ido muzai-muzai abin tausayi, duk babu kintsi tare dasu, don Dacta Mansur ya dawo da bara bana, ya fita harkarsu da Aziza kawai yake harkokinsa, ita ta jagoranci kukunsu wajen girka abin da za a taryi bakin dasu.
Cikin Sallama a falon Mamin, wanda ke saman bene, bayan sun wuce falon kasa suka shiga falon, mazan da babbar murya suka yi sallama, matan har Jawahir mai goyo da karamar murya sukai sallamar.
Chapter 13 · 0% Book details