Sashe 12
Rayuwar Rayhana Part 4 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Dr. Asma’u ta dade tana juya kan wayarta a hannunta. Ita ba ta son irin wannan sam, a ce ta yi abu, amma ba a gaya mata dalilin yin shi ba. Tana da ayyuka masu yawa a gabanta amma dole ta ture ta mike don Abida ba ta taba yi mata haka ba.
Abida jikinta bari yake, saboda kaduwa da razana. Azizah tsalle take, tsallen murna tana fadin
“A perfect match! Miskila, sai miskili dan’uwanta. Daddy the matchmaker! What a beautiful daughter I’ve….. wayyo ni dadi kashe ni.
Come soon baby Asma’u in goya ki in miki rawa in cillaki in café ki”.
Ta isa ga hoton ta sumbaci yarinyar daidai lokacin da Mamin ta fado falon. Abida ta janyota ta isar da ita ga hoton tana fadin
“Mami dubi rainin hankalin da aka miki, har aure Ya Himu ya yi da tsintacciyar yarinyar nan har sun haihu baki sani ba saboda an raina ki…..”
Ba ta kai ga rufe bakinta ba Daddy ya fito daga dakinshi yana ba ta amsa da cewa.
“An raina ta ko ta raina kanta annamimiya? Ba tun yau na kwana da sanin mugun halinki ba, to ki sani, ita wannan da kike kira tsintacciyar mage ta zama jininki, dolenki, uwar ‘ya’yanki ko ki mutu, ko ki yi rai ba abin da zai sameta da ikon Allah, wai don kun wulakanta ta.
Babu yadda za ku yi da ita, sai dai ku ci gaba da raina kanku, domin KAINUWA ce dashen Allah, kuma murucin kan dutse baka fito ba sai da ka shirya!!!
Idan kuna da hankali wannan ya isheku ishara. An gaya muku ana yiwa Allah shisshigi ne cikin al’amarinsa?”
Ya juya ya shige dakinsa.
Abida ta yi tsumu-tsumu, ita kuwa Dr. Asma’u sai ta zube a doguwar kujerar falon tana kuka, kukan da dukkansu basu san dalilin da yasa take yinsa ba, na bakin ciki ne ko na nadama? Allah kadai ya san me ke a zuciyar bayinsa.
Cikin zuciyarta Allah ya isa take wa Dr. Halima da ta goga mata bakin fenti a idanuwan wanda ya fi kowa sonta a duniya, ya yarda da ita, ya ba ta amanar gidansa. Ya yi mata kyakkyawar shaida a zuciya da bakinsa na uwargida ta gari. Yanzu wane bayani za ta yiwa Daddy ya saurare ta?
Babban bakin cikin Mami kullacin da Dacta Mansur ya yi mata a kan ikon da ta nuna a kan Khalipha da cewa da ya yi ta nuna masa yau ba shi ya haifi Khalipha ba….. tabbas ta dade da manta wannan tunda shi din bai taba nuna wata kafa da za a bambance ko a tuno hakan tsakanin Himu da Khalipha ba.
Kenan in da halacci bai cancanci butulci da rashin biyayyar da ta saka masa dasu ba.
A lokacin da babban mutum irin Dr. Mansur yake cikin fushi, dosar shi da ba da hakuri da karbar kuskure kamar izawa wuta fetir ne. don haka Mami tasa mishi ido har tsayin kwana uku.
Sai dai fa kullum cikin dare sai ta fito falo ta kurawa hoton ido tana shafa fuskar yarinyar, wadda Allah ya kinkimo wata gundumemiyar kaunar yarinyar ya saka mata a zuci.
Ta kan dade tana kallon Rayhanah wadda babu abin da ya sauya a halittarta sai santsin fata.
Da ka ganta ka ga matashiyar Bahaushiya ‘yar kimanin shekaru ashirin da shida, amma yanayin jikinta da canzawar fatar ta sai ka yi zaton daga kwai aka barota. Ta yi sumul ta yi mulmul har da wata ‘yar kiba ta samun perfection and contentment in life.
Shi kuma angon nata da ganinshi ka ga bakin Bature, kamanninshi da mahaifinshi sun sake fitowa sarari, da ka gansu za ka fahimci cewa komai na rayuwa ya yi musu dai-dai kamar yadda kowanne dan Adam ke burin samu.
Lallai Dacta Mansur ta yarda ba karamin hatsabibin dan boko bane. Wato ta hana da Khalipha tunda ta nuna ba nashi bane, sai ya yi mata lambo ta gama shuka tsiyarta, sannan ya fito mata ta bayan gida. Ta inda bata taba zata ba.
Ta tabbata ba ta isa in Ibrahim ne ta yi masa abin da ta yiwa Khalipha ba, don shi ba shi da hakuri ko kankani. Idan yana son abu fa kawai yana son shi, haka in bai so, jan ido da lallashi basu isa su sanya ya so abin nan ba.
Yau dai ga Rayhanah da take kora don tayi nisa da zuri’arta ta zama barin rayuwar Ibraheem. Da mafi soyawa a zuciyarta, ta hada zuri’ar da ba ta so din da ita, kuma Allah ya sanya mata so da kaunar zuri’ar, kamar ko ma fiye da yadda take son Ibrahim.
Dama an ce wai abin cikin kwai ya fi kwan dadi. Gaskiyar Dr. Mansur ne da ya ce ba a yiwa Allah shisshigi cikin al’amarinsa.
Dr. Asma’u ta yi nadama matuka, nadama irin wadda Ubangiji (S.W.T) ya yi alkawarin karbarta, wato nadama da tabbacin da bawa ya yi da zuciyarsa na cewa ba zaya kuma komawa izuwa zunubin ba.
*****
[1/1, 10:27] Takori: Karfe goma dai dai na safiyar litinin jirgin KLM ya sauke Dr. Ibrahim Mansur da iyalansa a filin jirgin saman Abuja, Khalipha ne yaje ya taho dasu daga filin jirgi, duk da cewa suma dawowarsu kenan a daren jiya daga Hurghada inda yaje ya taho da Mimtaz da Jawahir, wadanda suka kwashe watanni biyu a Egypt a dalilin haihuwar da Mimtaz ta yi ya kai su can suka yi biki. Khalipha bai yi kasa a gwiwa ba wajen radawa second born dinsa suna Ibrahim Khaleel.
Yau sai ga Rayhana da Yaya Khalipha, bayan gushewar a kalla shekaru uku da doriya. Ta kasa hada ido da Yaya Khalipha wanda ke rungume da Asma’u a kirjinsa. Shima Ibrahim rungume da takwaransa, kowanne ya kasa ajiye dan ya yi tukin motar.
Dukkansu suna gaba, ita da Mimtaz suna baya. Jefi-jefi Rayhanah kan saci kallon Yaya Khalipha, ya yi kiba ‘yar kadan ta hutu, ya kara murjewa. Da ganinshi za ka fahimci cikin kwanciyar hankalinsa yake, sannan likkafa ta yi gaba ko daga irin motar da ya dauko su a ciki da Balarabiyar da ya aje mai neman kashewa mutum ido don haske da hasken idanu.
Mimtaz ba ta da bakunta ko kadan, sai jan Rayhanah take da hira ta ji Hausa zau kamar (vedan) a dalilin rayuwa da su Jawahir, in ka ji tana Larabci to ita da iyayenta da danginta ne, amma ko Khalipha da Hausa suke magana.
Ta ce, “Yaya Khalipha aniyarka ta bika, ka ce ‘yar Dr. Ibrahim da Rayhanah muni za ta yi, gata nan ta fi duk iyayen kyau da haske”.
Ya ce, “Ai albarkacin sunan Mami ne shi yasa ta dan washe”.
Ya kara duban yarinyar cike da kauna yana fadin,
“Lallai Muhd. Mansur ya yi mata, zuki!” Ya sumbaci ‘yar.
Sai a lokacin ya juya ga Rayhana yana murmushi ya ce,
“Madam kinsha aiki, mun gode fah”.
Tana murmushi ta ce,
“Aikin me Yaya Khalipha?”
Ya mikawa Mimtaz Asma’u ya tada motar ya ce,
“Aikin haifo mana UWA, ba ta barota a komai ba”.
A ranta ta ce,
“Allah yasa kada ta yo halinta”.
Don dai ita har yanzu fargabar haduwa da Mami take, don ba ta san irin tarbar da za ta yi musu ba ita da ‘yarta. Tunda ita ba ‘ya ba ce annoba ce da ake neman guje mata, Allah ya kara manna musu.
Khalipha ya so suyi sati a Abuja su huta ya dan zazzaga dasu su ga sauye-sauyen ci gaba da Nigeria ta samu a Abuja, amma Ibraheem ya ki, ya ce a gobe za su wuce ya matsu da ya ga Mami don ya dade bai jita a waya ba, shi kuma in ya kira a ce da shi a kashe take.
Jawahir ta dawo daga asibiti cikin motar Mimtaz, ta kai Muhd Mansur asibiti ne yana fama da zazzabin sauyin yanayi, domin sun dade a Hurghada sosai har watanni biyu. Tun daga kofar falonsu ta fahimci lallai suna da baki.
Don haka ta shiga bakinta da sallama rike da hannun Muhd Mansur.
Rayhanah ta dago ido don jin muryar Jawahir, suka kuwa yi ido hudu da juna. Ai Jawahir cillar da jakar hannunta ta yi ta saki Mansur ta sheka da gudu ta rungume Rayhanah, ita ma ta rungumeta hawaye na zuba daga idon su. Hawayen kauna da TUNA BAYA……
(TUNA BAYA SHINE ROKO!) Inji Sumayyah Abdulkadir Takori.
Abida jikinta bari yake, saboda kaduwa da razana. Azizah tsalle take, tsallen murna tana fadin
“A perfect match! Miskila, sai miskili dan’uwanta. Daddy the matchmaker! What a beautiful daughter I’ve….. wayyo ni dadi kashe ni.
Come soon baby Asma’u in goya ki in miki rawa in cillaki in café ki”.
Ta isa ga hoton ta sumbaci yarinyar daidai lokacin da Mamin ta fado falon. Abida ta janyota ta isar da ita ga hoton tana fadin
“Mami dubi rainin hankalin da aka miki, har aure Ya Himu ya yi da tsintacciyar yarinyar nan har sun haihu baki sani ba saboda an raina ki…..”
Ba ta kai ga rufe bakinta ba Daddy ya fito daga dakinshi yana ba ta amsa da cewa.
“An raina ta ko ta raina kanta annamimiya? Ba tun yau na kwana da sanin mugun halinki ba, to ki sani, ita wannan da kike kira tsintacciyar mage ta zama jininki, dolenki, uwar ‘ya’yanki ko ki mutu, ko ki yi rai ba abin da zai sameta da ikon Allah, wai don kun wulakanta ta.
Babu yadda za ku yi da ita, sai dai ku ci gaba da raina kanku, domin KAINUWA ce dashen Allah, kuma murucin kan dutse baka fito ba sai da ka shirya!!!
Idan kuna da hankali wannan ya isheku ishara. An gaya muku ana yiwa Allah shisshigi ne cikin al’amarinsa?”
Ya juya ya shige dakinsa.
Abida ta yi tsumu-tsumu, ita kuwa Dr. Asma’u sai ta zube a doguwar kujerar falon tana kuka, kukan da dukkansu basu san dalilin da yasa take yinsa ba, na bakin ciki ne ko na nadama? Allah kadai ya san me ke a zuciyar bayinsa.
Cikin zuciyarta Allah ya isa take wa Dr. Halima da ta goga mata bakin fenti a idanuwan wanda ya fi kowa sonta a duniya, ya yarda da ita, ya ba ta amanar gidansa. Ya yi mata kyakkyawar shaida a zuciya da bakinsa na uwargida ta gari. Yanzu wane bayani za ta yiwa Daddy ya saurare ta?
Babban bakin cikin Mami kullacin da Dacta Mansur ya yi mata a kan ikon da ta nuna a kan Khalipha da cewa da ya yi ta nuna masa yau ba shi ya haifi Khalipha ba….. tabbas ta dade da manta wannan tunda shi din bai taba nuna wata kafa da za a bambance ko a tuno hakan tsakanin Himu da Khalipha ba.
Kenan in da halacci bai cancanci butulci da rashin biyayyar da ta saka masa dasu ba.
A lokacin da babban mutum irin Dr. Mansur yake cikin fushi, dosar shi da ba da hakuri da karbar kuskure kamar izawa wuta fetir ne. don haka Mami tasa mishi ido har tsayin kwana uku.
Sai dai fa kullum cikin dare sai ta fito falo ta kurawa hoton ido tana shafa fuskar yarinyar, wadda Allah ya kinkimo wata gundumemiyar kaunar yarinyar ya saka mata a zuci.
Ta kan dade tana kallon Rayhanah wadda babu abin da ya sauya a halittarta sai santsin fata.
Da ka ganta ka ga matashiyar Bahaushiya ‘yar kimanin shekaru ashirin da shida, amma yanayin jikinta da canzawar fatar ta sai ka yi zaton daga kwai aka barota. Ta yi sumul ta yi mulmul har da wata ‘yar kiba ta samun perfection and contentment in life.
Shi kuma angon nata da ganinshi ka ga bakin Bature, kamanninshi da mahaifinshi sun sake fitowa sarari, da ka gansu za ka fahimci cewa komai na rayuwa ya yi musu dai-dai kamar yadda kowanne dan Adam ke burin samu.
Lallai Dacta Mansur ta yarda ba karamin hatsabibin dan boko bane. Wato ta hana da Khalipha tunda ta nuna ba nashi bane, sai ya yi mata lambo ta gama shuka tsiyarta, sannan ya fito mata ta bayan gida. Ta inda bata taba zata ba.
Ta tabbata ba ta isa in Ibrahim ne ta yi masa abin da ta yiwa Khalipha ba, don shi ba shi da hakuri ko kankani. Idan yana son abu fa kawai yana son shi, haka in bai so, jan ido da lallashi basu isa su sanya ya so abin nan ba.
Yau dai ga Rayhanah da take kora don tayi nisa da zuri’arta ta zama barin rayuwar Ibraheem. Da mafi soyawa a zuciyarta, ta hada zuri’ar da ba ta so din da ita, kuma Allah ya sanya mata so da kaunar zuri’ar, kamar ko ma fiye da yadda take son Ibrahim.
Dama an ce wai abin cikin kwai ya fi kwan dadi. Gaskiyar Dr. Mansur ne da ya ce ba a yiwa Allah shisshigi cikin al’amarinsa.
Dr. Asma’u ta yi nadama matuka, nadama irin wadda Ubangiji (S.W.T) ya yi alkawarin karbarta, wato nadama da tabbacin da bawa ya yi da zuciyarsa na cewa ba zaya kuma komawa izuwa zunubin ba.
*****
[1/1, 10:27] Takori: Karfe goma dai dai na safiyar litinin jirgin KLM ya sauke Dr. Ibrahim Mansur da iyalansa a filin jirgin saman Abuja, Khalipha ne yaje ya taho dasu daga filin jirgi, duk da cewa suma dawowarsu kenan a daren jiya daga Hurghada inda yaje ya taho da Mimtaz da Jawahir, wadanda suka kwashe watanni biyu a Egypt a dalilin haihuwar da Mimtaz ta yi ya kai su can suka yi biki. Khalipha bai yi kasa a gwiwa ba wajen radawa second born dinsa suna Ibrahim Khaleel.
Yau sai ga Rayhana da Yaya Khalipha, bayan gushewar a kalla shekaru uku da doriya. Ta kasa hada ido da Yaya Khalipha wanda ke rungume da Asma’u a kirjinsa. Shima Ibrahim rungume da takwaransa, kowanne ya kasa ajiye dan ya yi tukin motar.
Dukkansu suna gaba, ita da Mimtaz suna baya. Jefi-jefi Rayhanah kan saci kallon Yaya Khalipha, ya yi kiba ‘yar kadan ta hutu, ya kara murjewa. Da ganinshi za ka fahimci cikin kwanciyar hankalinsa yake, sannan likkafa ta yi gaba ko daga irin motar da ya dauko su a ciki da Balarabiyar da ya aje mai neman kashewa mutum ido don haske da hasken idanu.
Mimtaz ba ta da bakunta ko kadan, sai jan Rayhanah take da hira ta ji Hausa zau kamar (vedan) a dalilin rayuwa da su Jawahir, in ka ji tana Larabci to ita da iyayenta da danginta ne, amma ko Khalipha da Hausa suke magana.
Ta ce, “Yaya Khalipha aniyarka ta bika, ka ce ‘yar Dr. Ibrahim da Rayhanah muni za ta yi, gata nan ta fi duk iyayen kyau da haske”.
Ya ce, “Ai albarkacin sunan Mami ne shi yasa ta dan washe”.
Ya kara duban yarinyar cike da kauna yana fadin,
“Lallai Muhd. Mansur ya yi mata, zuki!” Ya sumbaci ‘yar.
Sai a lokacin ya juya ga Rayhana yana murmushi ya ce,
“Madam kinsha aiki, mun gode fah”.
Tana murmushi ta ce,
“Aikin me Yaya Khalipha?”
Ya mikawa Mimtaz Asma’u ya tada motar ya ce,
“Aikin haifo mana UWA, ba ta barota a komai ba”.
A ranta ta ce,
“Allah yasa kada ta yo halinta”.
Don dai ita har yanzu fargabar haduwa da Mami take, don ba ta san irin tarbar da za ta yi musu ba ita da ‘yarta. Tunda ita ba ‘ya ba ce annoba ce da ake neman guje mata, Allah ya kara manna musu.
Khalipha ya so suyi sati a Abuja su huta ya dan zazzaga dasu su ga sauye-sauyen ci gaba da Nigeria ta samu a Abuja, amma Ibraheem ya ki, ya ce a gobe za su wuce ya matsu da ya ga Mami don ya dade bai jita a waya ba, shi kuma in ya kira a ce da shi a kashe take.
Jawahir ta dawo daga asibiti cikin motar Mimtaz, ta kai Muhd Mansur asibiti ne yana fama da zazzabin sauyin yanayi, domin sun dade a Hurghada sosai har watanni biyu. Tun daga kofar falonsu ta fahimci lallai suna da baki.
Don haka ta shiga bakinta da sallama rike da hannun Muhd Mansur.
Rayhanah ta dago ido don jin muryar Jawahir, suka kuwa yi ido hudu da juna. Ai Jawahir cillar da jakar hannunta ta yi ta saki Mansur ta sheka da gudu ta rungume Rayhanah, ita ma ta rungumeta hawaye na zuba daga idon su. Hawayen kauna da TUNA BAYA……
(TUNA BAYA SHINE ROKO!) Inji Sumayyah Abdulkadir Takori.